Sashe 152
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari Engr Khalid ya samu da batun don baisan ta yanda zai soma tink’aran Aunty Daula da wannan labari ba, Engr yaita basa baki had’ida k’arfafa masa gwiwa ya kuma sanar dashi shi zai sami Ammah da batun... Koda labarin accident d’in ya isa masu Abbah sai cewa Abbah yai maza su shirya su tafi, Aunty Bara’atu, Aunty Daula da yaranta ,Khalid da kuma Nabila suka d’auki hanyar Abuja bayan Abbah da Mamy sun kumayima Nabilah nasiha mai shiga zuciya, gashi tinda ya dawo makaranta taji wannan batu hankalinta ya tashi sosai, tausayin Khalid d’in ya cika mata zuciya ashe shisa bai sami zarafin d’aga wayarta ba, lallai yana cikin matuk’ar tashin hankali... Taga yanda a kwanakin ya shak’u sosai da mahaifinsa... Dole ma hankulansu ya tashi dan basuga yanayin halinda jikin Daddyn ke ciki ba, fatanta Allah ya tashi kafad’un Daddy ya basa lafiya...Dikda tana cikin yanayi na rabuwa da gida amma halinda mijinta Ke ciki sai yafi d’aga mata hankali, ga Aunty Daula ma wacce batasan soyayyan kowa ba tsawon shekarun nan bayan d’an uwanta Ma’aruf saiko na mijinta, itama dik ta koma abin tausai...
Wannan shine ana wata ga wata dan acan gidan Abban ma yanzu kam hankalinsu ya soma tashi na rashin sanin tak’aimemmen yanda Mamani ta tafi ga girma a tattare da ita, dole hankulansu ya tashi, in Kaga Abbah duk a birkice yake shima... Can gidan gidan Baba Alhaji ma abin babu sauk’i tin sanda Magajiya ta iso gidan a matsayin kishiyar Hajiya Haule abubuwa suka dad’a kwab’ewa... Ga Hafiz ya tada hauka wa mahaifin nasa cewa sai ya saki Magajiya dan bazai dinga shigowa gidan mahaifinsa yana karo da ‘yan daudu ba... Toh a can gidan Engr ma bayan zab’e da ya k’arato sosai maganan b’acewar Akram ya soma d’aga mai hankali a halin yanzu, dan harta Umman Akram d’inma yau sawunta na biyu kenan a gidan tana kuka tana fad’in ya taimaka ya nemo mata d’anta baida kowa sai Engr d’in kuma maraya ne... Kar ya dubi girman laifin da Akram d’in yai masa ya taimaka ya bincika yanda za’a sami Akram...
Engr ya sanarda ita ta kwantar da hankalinta idan ta kama za’ai tracking har layin da Akram yai amfani ya kirasa dashi last... Da wannan batu mahaifiyar Akram ta d’an sami sauk’i... Dole Engr ya had’a binciken da jami’an tsaro....
A b’angaren Sameer kaw yaso ya tafi ya duba jikin Daddy saidai Mummynsa da Daddynsa yau suke dawowa daga k’asar Saudiya yanda aka sallamo Daddyn nasa daga can Saudi German bayan kwashe sama da watanni hud’u yana jinya a can..... Dama tuni sun sanar dashi ta Kano zasu sauk’a...
Tarba na girma suka samu daga iyayen Sameer dikda halin tashin hankalin da suke ciki hakan bai hanasu karrama iyayen rik’on Ma’aruf ba mutanenda bayansu Sameer baida wanda suka fisu, Alhamdulillah jikin Daddy yayi kyau sosai dan Sameer d’in yaji dad’in yanda yaga jikin Daddyn nasa yayi kyaun gani... Allah sarki Sameer da Mummy tamkar su had’iyi juna dan Farin ciki... Mamy da Abbah har rasa kalaman da zasuyi amfani wajen mik’a godiyarsu ga wad’Annan bayin Allah da suka rik’e masu d’a tamkar nasu sukai.... Sai Hawaye kurum da Mamy keyi...
Mummy Fatahiyya ta rungumeta tana fad’in “Hajiya Mariya ai d’ah na kowa ne... Dik wanda kikaga ya rik’i d’an da ba nasa ba a wulak’ance dan kawai bashi ya haifesa ba Toh ki tabbata wannan mutumin baida zuciya a k’irjinsa idan kuma yanadashi Toh fah itada babu dik d’aya ne... Shi d’ah basai ka haifa ba ya zamto naka... So tari zaka haifi d’an baka mora ba wani daban ya moreshi.... Shi wanda baka haifan ba sai kafi moranshi sama da naka.... Haka Allah yake gudanar da Al’amaranshi.... Kin gama min komai da kika haifo min d’ah kaman Sameer cikin Duniyar nan....” Ta k’arashe tana kuma kamo hannayen Mamy da itama hawayen take....
Kirkin mutanen har ya zarta misali, haka kalaman Hajiya Fatahiyya sukaita yawo a kwanyar Abbah, tabbas dik abubuwan data fad’i gaskiya ne... Ko menene Mamani tai a baya ya rik’eshi da duka soyayyarta kuma bata masa rik’on sakainan kashi ba... Idan har ya cika d’a mai biyayya dole ya nemota yanda ta shiga ta fita ya kuma saurara daga b’angarenta....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*97*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Babu b’ata lokaci Sameer ya soma shirye shiryen bin iyayen nasa zuwa Kaduna a Washe gari, dan hakan ne ya kamata sannan daga can zai biya ya duba jikin Daddy... Nan Abbah ya umarcesa da ya d’auki matarsa ya tafi da ita, babu musu ya amsawa nahaifin nasa, sai sannan su Daddy suke samun labarin k’arin auren da Sameer yai, sukaita mamaki Mummy har tana dungurinshi tana fad’in wato ya tsere ma Babansa, su dai su Mamy sai mamakin yanda Sameer ke matuk’ar wasa da Mummynsa suke, da gani ba k’aramin Sabo da shak’uwa bace tsakaninsu... Sai sannan ake breaking wannan labari wa Raihanah kasancewar zatabi mijinta su tafi... Ita harga Allah abin mamaki yaita bata, Wai itace matar Ya Ma’aruf... Ita Raihanatu itace akai mata aure da Ya Ma’aruf ba Addarta Sahariyya ba... Take taji wane irin rauni kuma can k’asar zuciyarta...Ta sani Ya Ma’aruf mutumin kirki ne da ko wacce mace zatai alfaharin samu a matsayin miji... Amma harga Allah ji take auren yai mata diran sauri, ko da wasa bata tab’a kawowa aurenta na nan kusa ba... Abbah da Mamy sukaita bata baki suna nuna mata in sha Allah Ma’aruf zai zamto alkhairi a gareta kuma bazata kuka da zab’insu ba da izinin Allah... Ita dai kanta kife kurum yake sai Hawaye dake gangaro mata cikin sabon mayafin da Mamy ta rufa mata da kanta, tana jin sallamansa bugun zuciyarta ya k’aru... Zama yai daga gefe kad’an kusan k’afan Abbah...
Abbah ya kuma masu nasiha mai shiga jiki sosai musamman Sameer da yanzu mata biyu Ke gareshi...
Mummy kaw tuni itama ta shiga nan nan da Raihanah, abin sosai yai mata dad’i, ita d’in shaidace yanda D’an nata ya sha wahala da aure, sam zamansu da Siyama rabi a gidansu Siyama tayisa, tabbas taji dad’in wannan aure na Sameer tana kuma fatan nutsuwar da bai samu a baya ba ya samu yanzu...
A d’aki Mamy taci gaba da lallashin Raihanah tana sanar da ita, nan Kano zata zauna... Yanzu rakiya kawai zasuyima iyayen goyonsa amma da zaran al’amara sun daidaita yace nan Kano zai ajeta kusa da gida... Da wannan batu na Mamy Raihanah ta d’an sami sauk’i a zuciyarta...
Da dare suna zaune d’aki itada Marliya tana tayata shiryawa lokaci guda tana ci gaba da zolayarta “A’a ashe dai ashe dai patient ce matar... No wonder dik abinda ya shafi patient Yaya Ke baiwa abin kulawa na musamman ashe dai....”
Raihanah ta galla mata harara tana ci gaba da share hawayenta....
Marliya ta d’an marairaice fuska tace “Allah sarki ki hak’uri mutuniyar gobe war haka ina nan ina kewarki...”
Raihanah dai batace komai ba sai goge hawayenta data ci gaba dayi.... Marliya ta ije rigar da take linkewa kana tace “Toh Wai ma wasu kaya zaki tafi dasu bayan inaji d’azu Ya Ma’aruf na fad’iwa Mamy da zaran kun tafi Kaduna zai maki sayayya... Inye yarinya kin mori miji d’an gayu mai taste...”
Jifa mata rigar dake hannunta tai kana tace “Idan bazaki tayan ba Ki tashi Ki fita.. Na mori miji ta ina bayan wannan matar tasa tsoro take bani harga Allah. kuma yanzu Addah Sahariyya mai zata kirani tinda kinsan yanda ta d’aukaki auren nan... Nidai Allah dan bazan iya musu masu Abbah bane da.....” Kasa ci gaba da magana tai sakamakon sallamansa da suka jiyo daga k’ofa... Marliya tai zumbur ta mik’e tana mai k’ok’arin gaidashi lokaci guda ta fice ta basu waje...
Zuciyarta taci gaba da tsinkewa... Banda sautin dum dum! K’irjinta bai komai, gaba d’aya ma sai ta daburce ta mance mai take, da k’yar ta iya lalumo kalmomi saman harshenta ta soma gaidashi...
Saida wasu dak’ik’ai suka d’an gauta kana ya amsa mata yana mai karantar yanayinta, ita dai dik tsarge take, ko bata d’ago ta dubesa ba jikinta na bata tsareta yai da idanunsa... Har ta ciren ran bazai kuma cewa komai ba ta sinkayo muryarsa na fad’in “Gobe idan Allah ya kaimu before mu wuce akwai yanda zamuje... So ki shirya da wuri ko...”
Jinjina masa kai kurum tai ba tareda ta iya amsawa ba, gaba d’aya sai yaji jikinsa ya masa sanyi... A ‘yan shekaruntan nan ta tari labarin aurenta haka dole abin ya dameta, sosai tausayinta ya cika zuciyarsa... Koda bata d’ago idanunta ba zai iya ta tabbatarwa hawaye take... Gaba d’aya sai yaji babu dad’i, alk’awari ya d’aukarwa kansa koda ace bai sonta zai koya ma kansa yanda ake sonta... Koda ace bai tab’a son wata d’iya mace sama da Siyama ba bazai tab’a bari Raihanah ta fahimci hakan ba sabida ta cancanci fiyeda hakan.... Tana jin ficewarsa yana amsa kira ya sanyata saurin mik’ewa ta nufi bathroom tana mai kuma tintsirewa da sabon kuka... Sameer yana iya sauraro yanda take shesshek’ar kuka daga toilet, ya lumshe idanunsa a hankali yana mai ije ‘yar jakan kayan da ya shigo mata dashi saman gado... Cikin sauri yasa kai ya fice daga d’akin dan kukan nata sosai yake breaking d’insa....
***
A can Abuja kaw tinda suka isa sukaga condition d’in Daddy hankulansu suka kuma tashi, tabbas Daddy yana matuk’ar jin jiki dan ko d’akin da yake ba’a bari a shiga, da k’yar suka k’yale Auhty Daula da Khalid suka shiga bayan sun saka kayan sukuf irinta ma’aikatan lafiya... Haka hawaye ya dinga d’iga masu ganin Daddy kwance unconscious... Addu’o’i sukai masa kana suka fito dan babu halin Kwana ma’aikatan lafiyan basuda buk’atan kowa ya kwana wajensa musamman dashike har yanzu baisan yanda yake ba, na’urar bature ne kawai da buwayar Ubangiji ke aiki akansa....
Haka suka d’unguma suka nufi gida jiki dik a mace, Nabilah da Aunty Bara’atu suke k’ok’arin d’ebewasu Ijlaal kewa musamman Humaira data fara wayo ta fahimci abindake faruwa....
Haka nan sukai dinner babu dad’i gaba d’aya abincin ba wani ci sukai ba, baranma Khalid da sam ko fitowa parlorn baiba tinda suka dawo daga asibiti...
Wannan shine ana wata ga wata dan acan gidan Abban ma yanzu kam hankalinsu ya soma tashi na rashin sanin tak’aimemmen yanda Mamani ta tafi ga girma a tattare da ita, dole hankulansu ya tashi, in Kaga Abbah duk a birkice yake shima... Can gidan gidan Baba Alhaji ma abin babu sauk’i tin sanda Magajiya ta iso gidan a matsayin kishiyar Hajiya Haule abubuwa suka dad’a kwab’ewa... Ga Hafiz ya tada hauka wa mahaifin nasa cewa sai ya saki Magajiya dan bazai dinga shigowa gidan mahaifinsa yana karo da ‘yan daudu ba... Toh a can gidan Engr ma bayan zab’e da ya k’arato sosai maganan b’acewar Akram ya soma d’aga mai hankali a halin yanzu, dan harta Umman Akram d’inma yau sawunta na biyu kenan a gidan tana kuka tana fad’in ya taimaka ya nemo mata d’anta baida kowa sai Engr d’in kuma maraya ne... Kar ya dubi girman laifin da Akram d’in yai masa ya taimaka ya bincika yanda za’a sami Akram...
Engr ya sanarda ita ta kwantar da hankalinta idan ta kama za’ai tracking har layin da Akram yai amfani ya kirasa dashi last... Da wannan batu mahaifiyar Akram ta d’an sami sauk’i... Dole Engr ya had’a binciken da jami’an tsaro....
A b’angaren Sameer kaw yaso ya tafi ya duba jikin Daddy saidai Mummynsa da Daddynsa yau suke dawowa daga k’asar Saudiya yanda aka sallamo Daddyn nasa daga can Saudi German bayan kwashe sama da watanni hud’u yana jinya a can..... Dama tuni sun sanar dashi ta Kano zasu sauk’a...
Tarba na girma suka samu daga iyayen Sameer dikda halin tashin hankalin da suke ciki hakan bai hanasu karrama iyayen rik’on Ma’aruf ba mutanenda bayansu Sameer baida wanda suka fisu, Alhamdulillah jikin Daddy yayi kyau sosai dan Sameer d’in yaji dad’in yanda yaga jikin Daddyn nasa yayi kyaun gani... Allah sarki Sameer da Mummy tamkar su had’iyi juna dan Farin ciki... Mamy da Abbah har rasa kalaman da zasuyi amfani wajen mik’a godiyarsu ga wad’Annan bayin Allah da suka rik’e masu d’a tamkar nasu sukai.... Sai Hawaye kurum da Mamy keyi...
Mummy Fatahiyya ta rungumeta tana fad’in “Hajiya Mariya ai d’ah na kowa ne... Dik wanda kikaga ya rik’i d’an da ba nasa ba a wulak’ance dan kawai bashi ya haifesa ba Toh ki tabbata wannan mutumin baida zuciya a k’irjinsa idan kuma yanadashi Toh fah itada babu dik d’aya ne... Shi d’ah basai ka haifa ba ya zamto naka... So tari zaka haifi d’an baka mora ba wani daban ya moreshi.... Shi wanda baka haifan ba sai kafi moranshi sama da naka.... Haka Allah yake gudanar da Al’amaranshi.... Kin gama min komai da kika haifo min d’ah kaman Sameer cikin Duniyar nan....” Ta k’arashe tana kuma kamo hannayen Mamy da itama hawayen take....
Kirkin mutanen har ya zarta misali, haka kalaman Hajiya Fatahiyya sukaita yawo a kwanyar Abbah, tabbas dik abubuwan data fad’i gaskiya ne... Ko menene Mamani tai a baya ya rik’eshi da duka soyayyarta kuma bata masa rik’on sakainan kashi ba... Idan har ya cika d’a mai biyayya dole ya nemota yanda ta shiga ta fita ya kuma saurara daga b’angarenta....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*97*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Babu b’ata lokaci Sameer ya soma shirye shiryen bin iyayen nasa zuwa Kaduna a Washe gari, dan hakan ne ya kamata sannan daga can zai biya ya duba jikin Daddy... Nan Abbah ya umarcesa da ya d’auki matarsa ya tafi da ita, babu musu ya amsawa nahaifin nasa, sai sannan su Daddy suke samun labarin k’arin auren da Sameer yai, sukaita mamaki Mummy har tana dungurinshi tana fad’in wato ya tsere ma Babansa, su dai su Mamy sai mamakin yanda Sameer ke matuk’ar wasa da Mummynsa suke, da gani ba k’aramin Sabo da shak’uwa bace tsakaninsu... Sai sannan ake breaking wannan labari wa Raihanah kasancewar zatabi mijinta su tafi... Ita harga Allah abin mamaki yaita bata, Wai itace matar Ya Ma’aruf... Ita Raihanatu itace akai mata aure da Ya Ma’aruf ba Addarta Sahariyya ba... Take taji wane irin rauni kuma can k’asar zuciyarta...Ta sani Ya Ma’aruf mutumin kirki ne da ko wacce mace zatai alfaharin samu a matsayin miji... Amma harga Allah ji take auren yai mata diran sauri, ko da wasa bata tab’a kawowa aurenta na nan kusa ba... Abbah da Mamy sukaita bata baki suna nuna mata in sha Allah Ma’aruf zai zamto alkhairi a gareta kuma bazata kuka da zab’insu ba da izinin Allah... Ita dai kanta kife kurum yake sai Hawaye dake gangaro mata cikin sabon mayafin da Mamy ta rufa mata da kanta, tana jin sallamansa bugun zuciyarta ya k’aru... Zama yai daga gefe kad’an kusan k’afan Abbah...
Abbah ya kuma masu nasiha mai shiga jiki sosai musamman Sameer da yanzu mata biyu Ke gareshi...
Mummy kaw tuni itama ta shiga nan nan da Raihanah, abin sosai yai mata dad’i, ita d’in shaidace yanda D’an nata ya sha wahala da aure, sam zamansu da Siyama rabi a gidansu Siyama tayisa, tabbas taji dad’in wannan aure na Sameer tana kuma fatan nutsuwar da bai samu a baya ba ya samu yanzu...
A d’aki Mamy taci gaba da lallashin Raihanah tana sanar da ita, nan Kano zata zauna... Yanzu rakiya kawai zasuyima iyayen goyonsa amma da zaran al’amara sun daidaita yace nan Kano zai ajeta kusa da gida... Da wannan batu na Mamy Raihanah ta d’an sami sauk’i a zuciyarta...
Da dare suna zaune d’aki itada Marliya tana tayata shiryawa lokaci guda tana ci gaba da zolayarta “A’a ashe dai ashe dai patient ce matar... No wonder dik abinda ya shafi patient Yaya Ke baiwa abin kulawa na musamman ashe dai....”
Raihanah ta galla mata harara tana ci gaba da share hawayenta....
Marliya ta d’an marairaice fuska tace “Allah sarki ki hak’uri mutuniyar gobe war haka ina nan ina kewarki...”
Raihanah dai batace komai ba sai goge hawayenta data ci gaba dayi.... Marliya ta ije rigar da take linkewa kana tace “Toh Wai ma wasu kaya zaki tafi dasu bayan inaji d’azu Ya Ma’aruf na fad’iwa Mamy da zaran kun tafi Kaduna zai maki sayayya... Inye yarinya kin mori miji d’an gayu mai taste...”
Jifa mata rigar dake hannunta tai kana tace “Idan bazaki tayan ba Ki tashi Ki fita.. Na mori miji ta ina bayan wannan matar tasa tsoro take bani harga Allah. kuma yanzu Addah Sahariyya mai zata kirani tinda kinsan yanda ta d’aukaki auren nan... Nidai Allah dan bazan iya musu masu Abbah bane da.....” Kasa ci gaba da magana tai sakamakon sallamansa da suka jiyo daga k’ofa... Marliya tai zumbur ta mik’e tana mai k’ok’arin gaidashi lokaci guda ta fice ta basu waje...
Zuciyarta taci gaba da tsinkewa... Banda sautin dum dum! K’irjinta bai komai, gaba d’aya ma sai ta daburce ta mance mai take, da k’yar ta iya lalumo kalmomi saman harshenta ta soma gaidashi...
Saida wasu dak’ik’ai suka d’an gauta kana ya amsa mata yana mai karantar yanayinta, ita dai dik tsarge take, ko bata d’ago ta dubesa ba jikinta na bata tsareta yai da idanunsa... Har ta ciren ran bazai kuma cewa komai ba ta sinkayo muryarsa na fad’in “Gobe idan Allah ya kaimu before mu wuce akwai yanda zamuje... So ki shirya da wuri ko...”
Jinjina masa kai kurum tai ba tareda ta iya amsawa ba, gaba d’aya sai yaji jikinsa ya masa sanyi... A ‘yan shekaruntan nan ta tari labarin aurenta haka dole abin ya dameta, sosai tausayinta ya cika zuciyarsa... Koda bata d’ago idanunta ba zai iya ta tabbatarwa hawaye take... Gaba d’aya sai yaji babu dad’i, alk’awari ya d’aukarwa kansa koda ace bai sonta zai koya ma kansa yanda ake sonta... Koda ace bai tab’a son wata d’iya mace sama da Siyama ba bazai tab’a bari Raihanah ta fahimci hakan ba sabida ta cancanci fiyeda hakan.... Tana jin ficewarsa yana amsa kira ya sanyata saurin mik’ewa ta nufi bathroom tana mai kuma tintsirewa da sabon kuka... Sameer yana iya sauraro yanda take shesshek’ar kuka daga toilet, ya lumshe idanunsa a hankali yana mai ije ‘yar jakan kayan da ya shigo mata dashi saman gado... Cikin sauri yasa kai ya fice daga d’akin dan kukan nata sosai yake breaking d’insa....
***
A can Abuja kaw tinda suka isa sukaga condition d’in Daddy hankulansu suka kuma tashi, tabbas Daddy yana matuk’ar jin jiki dan ko d’akin da yake ba’a bari a shiga, da k’yar suka k’yale Auhty Daula da Khalid suka shiga bayan sun saka kayan sukuf irinta ma’aikatan lafiya... Haka hawaye ya dinga d’iga masu ganin Daddy kwance unconscious... Addu’o’i sukai masa kana suka fito dan babu halin Kwana ma’aikatan lafiyan basuda buk’atan kowa ya kwana wajensa musamman dashike har yanzu baisan yanda yake ba, na’urar bature ne kawai da buwayar Ubangiji ke aiki akansa....
Haka suka d’unguma suka nufi gida jiki dik a mace, Nabilah da Aunty Bara’atu suke k’ok’arin d’ebewasu Ijlaal kewa musamman Humaira data fara wayo ta fahimci abindake faruwa....
Haka nan sukai dinner babu dad’i gaba d’aya abincin ba wani ci sukai ba, baranma Khalid da sam ko fitowa parlorn baiba tinda suka dawo daga asibiti...