← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 121 OF 198

Sashe 121

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Raihanah na zaune k’asa kusan k’afafun Mamani tana warwarewa Mamanin k’unshi a k’afafunta lokaci guda suna kallon maimaicin shirin draman Dad’in kowa da ake nunawa a tashar Arewa24 Sameer yai sallama...
Mamani ta shiga Washe baki tana fad’in “Shigo abinki angon gobe..”
Raihanah kaw gaba d’aya sai ta tsinci kanta da daburcewa musamman dashike kanta a bud’e ne ko d’ankwali babu, jan top ne a jikinta saiko zanin tampa, ida tsifanta kenan Mamani tace ta cire mata k’unshi, gashi hannayenta gaba d’aya b’ace suke da k’unshi, gaba d’aya sai jinta take a tsarge... Tana jin suna gaisawa da Mamani ta kasa koda d’ago idanu ne balle ta gaidashi.....
Shiko Sameer tinda ya shigo duba d’aya yaima bayanta ya d’auke idanunsa gabansa na wani irin yankewa, sam bai kawo Raihanah bace zaune wajen dan shi zai iya rantsuwa baisan yaya suffar jikinta yake ba dikda cewa shi yai treating ciwonta, dashike ba abinda yake dubawa ba kenan, aikinsa kenan yai treating ciwo nothing more....
Mamani sai jansa da firan biki take bai iya amsawa saidai murmushi da jinjina kai kurum da yake mata, ita kaw Rainah banda addu’an samun mafitar yanda zata mik’e ta bar wajen bata komai.. Kaman wacce addu’arta ya amsu taji ya mik’e yana amsa waya... Harda ‘yar ajiyan zuciya ta sauk’e wanda ta tabbata badon tv dake kunne ba da Mamani ta jiyo sautin ajiyan zuciyarta...
Muryar Mamanin ne ya katseta da fad’in “Yauwa sannu ‘yar albarka, maza tashi ki wanke hannun naki ki dama masa furan nan da d’azu Babanku ya aiko....
Ta mik’e tana mai gyara d’aurin zaninta “Toh Mamani...”
D’aki ta nufa daidai sanda ya ida wayar yana k’ok’arin komowa parlorn, ai a d’ari ta fad’a d’akin tana mai kuma sauk’e ajiyan zuciya, bathroom ta fad’a ta wanke hannunta kana ta bud’e wardrobe ta ciro hijabin da ya kusan kaiwa gwiwarta ta zira, kana iya tudun sumarta yanda ta tupke shi tsakiya dashike sumar nata mai yalwan cika ne kuma bata saka mar relaxer...
Idonsa k’yam a k’ofar d’akin da yaga ta shige tamkar mai jiran fitowar nata, dik bayanan da Mamani ke masa ba wani fahimtar ta yake ba, yafi maida hankaliga duban k’ofar... Aiko tana fitowa sukai ido hud’u, tai saurin maida nata idanun k’asa tana gaidashi...
Ya amsa yana mai duban k’afarta mai ciwo da yanayin tafiyar nata....
Ita dai Raihanah kitchen ta shige abinta dan kawo masa damin fura kaman yanda Mamani ta buk’ata....
Tana cikin had’a kindirmon ta cirota kenan daga cikin fridge Marliya ta shigo ta isketa....
“Patient d’in Yaya mi kike a kitchen... Salon Ya Ma’aruf yace an sakaki aiki tinda islamiya ma hanaki zuwa yai...”tace sanda take k’arasowa cikin kitchen d’in...
Gajeriyar murmushi Raihanah tai kana tace “Tinda mashi zanyi aikin bazai hana ba... Kinga shigo ma ki tayani...” Ta k’arashe tana mik’a mata bowl.. Marliya ta kame baki tace “A’a kedai cika ladarki hajiya patient..”
Raihanah ta d’an langab’e kai tace “Kai Marliya yanzu bazaki tayani ba....”
“Cikata ladanki kawai patient d’in Yaya dama Mamy ke nemanki bara naje nace kina zuwa...” Bata jira cewan Raihanar ba tai ficewarta da d’an gudu gudu....

A can parlor kaw Sameer mik’ewa yai da niyyar tafiya Mamani ta tsaidashi da fad’in “Aff ai kuwa Raiha na kitchen tana dama maka fura bazaka tsaya kasha ba....”
D’an sosa k’eyarsa yai da makullin mota “A’a Mamani a barshi har na dawo, ana nemana ne a can asibiti....”
Mamani ta jinjina kai tace “Oh ni yaron nan sam baka hutu saikace agogo... Toh Allah shi tsare amma ka lek’a kitchen d’in ka amsa ko a mota sai ka sha....”
Da toh ya amsa mata dan baiso ya kuma jan zancen yasan tinda ta soma fad’in sai ya amsa toh bazata k’yalesa ba har sai ya amsa d’in.... Yana jiyo muryarsa tanai masa addu’an Allah ya tsare...

Lokaci guda tabi bayansa da kallo tausayinsa na d’awainiya da ita... Anya batai katsalandan ma rayuwarsa ba, ta rasa da wa zata had’asa aure sai d’iyar Haule...? Toh amma ai ‘yar uwarsa ce ta daifi masa wancan ballagazar matar tasa ko babu komai Sahariyya bazata rabasu dashi ba kaman wancan mai zubin awakan, idan ya tuna yanada iyalina gida dole ya waiwayesu....kuma yanzu Haule tayi hankali ta tuba ta gyara halayyanta... Dik d’an adam kuma ajizi ne tinda itama a baya ba haka take ba saida ta nemi yafiyan ahalinta, da wannan tinani ta d’an samu zuciyarta yai sanyi...

Tsaye yai a k’ofar kitchen d’in yana duban yanda take kokawa da ice block saikace wata mai fasa gini duk ta wani daddage k’arfinta....
Abin yaso basa dariya, gyaran muryar da ya d’anyi ne ya sanyata saurin juyowa... Ta daidaita zaman hijabinta tana mai maida idanunta k’asa, sihirtaccen murmushi saman fuskarta “Laa Yaya ka gaji da jira koh... Dama yanzu zan kawo maka...”
Sameer ya ida shigowa cikin kitchen d’in yana duban yanda take gudanar da al’amranta wanda zai tabbatar maka ita d’in ma’abociya hidima da kitchen ne “Is okay, kiyi min packaging kawai zan tafi dashi ne...”
Jinjina masa kai tai kana tace “Ok bara na d’uko jug cikin drawer...”
Gaba d’aya a daburce take gashi ya tsaya ya tsareta da idanunsa... Drawers dake k’asa ta soma dubawa bata sami jug ciki ba, dole tasan suna drawers d’in sama kenan... Sanin cewa tsawonta bazai kai ba dole ta shiga neman abinda zata taka ta ciro jug d’in...
Shiko Sameer harda kame hannaye yana kallon ikon Allah... Toh mai take nema haka...? Bai ida tinanin ba yaga ta d’auko k’aramar kujera irin ta zaman kitchen ta d’ale tana k’ok’arin mik’a tsawonta alamun dai har yanzu tsawon nata bai k’arasa ba... Girgiza kai kurum yai yana mai d’an murmusawa kad’an, sai ganinsa kurum Raihanah tai gefenta ya bud’e drawer d’in... “Wanne zan ciro miki...?” Ya tambaya yana duban jugs d’in dake jere cikin drwer d’in, kusan guda uku...
Murmushi saman fuskarta tace “Ko wanne ma Yaya...”
Dubanta yai yaga wanda idanunta Ke bisa kana yasa hannu ya ciro shi... Daidai saitin kunnenta ya rage sautin muryarsa yana fad’in “Be careful kinsan har yanzu ked’in patient ce...” Bai jira cewarta ba ya ije mata jug d’in saman sink
Wane irin kunyarsa ya rufeta, ta k’araso kai a sanne ta isa ta d’auraye jug d’in kana ta juye damin furan ciki...
idanunsa naga wayarsa sanda ta k’araso ta mik’a masa jug d’in cikeda risinawa... Ya amsa yana fad’in “Da fatan dai baki zuba sugar ba..?”
Girgiza masa kai tai alamun a’a kana tace “Ban saka ba Yaya....”
“Good..” Ya furta yana amsar jug d’in lokaci guda ya shiga magana a wayarsa... Ta bisa da kallo tana mamakin wannan bawan Allah kullum cikin amsa waya yake... Daga nan ta shige amsa kiran Mamy....

SameenaAleeyou 📚

*INDA RAI*
_................DA RABO_

*84*

*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Chapter 121 · 0% Book details