Sashe 13
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsawa ya daka mata daga yanda take tsaye amma ko gizau batayi ba saima dubansa da takeyi da idanunta da suka kad’a sukayi jazir har lokacin tana nan tsaye, da k’arfin gaske ya fuzge wayarsa a dai dai lokacinda hawaye mai d’umi ya sauk’a saman k’uncinta....
Bai daina huci ba ya shiga duba kiranda ta amsa, d’ago murtuk’ekk’en fuskar da babu alamun annuri cikinta yayi kana yace “Ubanwa yace ki amsa min waya....?!”
Bata amsa shi ba haka nan bata d’ago idanu ta dubeshi ba.,,,
Ya kuma daka mata tsawa “Nace da izinin ubanwa kika d’aga min waya...? Yaushema kika soma tab’a min wayata a gidan nan...?”
Shiru bata bashi amsa ba...
“Ba magana nake miki ba..!!” Ya kuma daka mata tsawa...
Saida tasa tafukan hannayenta ta share hawaye suka sauk’o fuskarta kana tayi k’ok’arin saita kanta tace “Kayi hak’uri....” A tak’aice....
Huci kawai yake yana dubanta kana yayi k’wafa yaci gaba da fad’in “Sai kinyi abu kicewa mutum yayi hak’uri bayan ni hak’urin zama dake nake, an lik’amin ke ana tausana ana bani hak’urin ci gaba da zama dake matar da babu wani alkhairi a tattaredake face sharri.. Wllhi kinji na rantse zan maki kashedi na k’arshe duk ranar da aka kuma kirata kika d’aga sai na karyaki kafin na maidake gidan iyayenki su baki tarbiya da kyau, duk kuma abinda kikaji daga wayata ke kika jiyowa kanki don babu ubanda ya aikeki d’agawa... Jaka mai farar k’afa....”
Yana gama yab’a mata munan kalamai yayi shirinsa abinsa ya fice yana neman layin Sawwama da tak’i d’aga kiransa....
Can k’uryar d’aki Zulfah ta rakub’e idnunta na mata wani irin barkono don kukan ma nemansa tayi ta rasa, wannan shine mijin da mahaifinta ya zab’ar mata zama dashi har yake ikirarin idan tayi abunda aka sakota babu ita babu shi sannan kada ta dawo masa gida ta nemi wani uban ba shi ba, ita kuma kalan tata k’addarar kenan, haka Allah yaso ya jarabceta, inama ace Hafiz ya tsaya a zagi da wulak’anci kawai, inama ace aure ya k’ara ba bin matan titi ba, shin wannan shine wanda iyayenta suka zab’ar mata tayi rayuwar sunnah dashi..? Wannan shine uban ‘ya’yanta da zasu tashi suyi alfahari dashi su nunashi suce ga mahaifinsu...? Shin idan iyayenta sun zab’ar mata wannan mutumin ita tayi adalci wa ‘ya’yan da zata haifa kenan....? Take wasu hawaye masu tsananin rad’ad’i taji suna gangaro mata... Ta jima tak’ure a wajen tanayin mai isarta kafin ta mik’e ta nufi band’aki ta d’auro alwala ta shiga mik’a kukanta ga Ubangiji wanda batada gatan da yafi Shi.....
***
Tun bayan shigowarta office d’in tayi amai ak’alla sau uku kenan, harta coffee d’in da sakatariyarta ta kawo mata hamamin kawai saida ya sata k’waza amai, gaba d’aya ta zama pale and weak, batajin kuzari sam a tattareda ita ga tashin zuciya da ya addabeta, a halin yanzu bata buk’atan komai face hutu saidai zamanta a office d’in ya fiye mata don bataso Ammy ta fahimci halin da take ciki idan har abinda take zargi ya tabbata....
Wani aman ne yazo mata ta mik’e a guje ta kuma fad’awa bathroom tana kumayi... Tamkar zata amayar harda ‘yan hanjinta haka take nishi....
Da k’yar da dafe bango ta fito daga bathroom d’in yanda ta tadda aminiyarta k’wara d’aya tak a duniya zaune saman kujera mai kallon nata damuwa kwance saman fuskarta alamun taji yanda take k’waza aman....
Kallo guda Siyama tayiwa Laila ta d’auke kai kafin ta isa k’aramar fridge d’in dake a cikin office d’in ta d’auko chocolate tana afawa a bakinta ko zata sami sauk’in tashin zuciyar da ya addabeta....
Zama tayi saman kujerarta ta d’an kishingid’a had’ida lumshe idanu tana mai maida numfashi a hankali....
Kaman daga sama ta tsinkayo muryar Laila tana fad’in “Siyama wai bazakije asibiti ba kina zaune da ciwo, ki duba ki gani yau d’aya yanda kika lalace....
Gyara zamanta ta d’anyi kana tace “Laila bazaki gane ba, ni na rigada nasan abinda ke damuna amma saidai idan shid’in ne I’m not ready yet, Wllhi ban shirya zama uwa ba, ban shirya d’aukan responsibilities ba Laila not now....”
K’uri Laila ta mata kana tace “Tirk’ashi, toh amma kema kinyi kuskure da kika bari kika d’auki ciki baki shirya ba...”
Siyama ta jinjina kai tace “I know Laila, wllhi na sani shiyasa ma na kiraki don bansan yaya zanyi ba sauk’ina d’aya Sameer baya nan balle ya fahimci wani abu...”
Laila ta tab’e baki kad’an kana tace “Toh yanzu da kika riga kika d’auki cikin me kike so ayi, nidai a nawa ganin kawai ki hak’uri ki haife abinki tinda dai dama bamu isa muce komai sai mun shirya ma zuwansa ba, just take the risks ki haifa kawai....”
Banda harara Siyama bata aika mata komai, gajeren tsaki tayi kana tace “You’re not helping... Idan na haihu yanzu komai na rayuwata canzawa zatayi, harta d’anda na haifah can come between us nida Partner, maybe ma yafi son d’an sama dani sannan zan iya rasa attention d’in mijina gaba d’aya... Bama wannan ba kawai I’m not ready to become a mother......”
Laila ta jinjina kai kana tace “Tun farko you shouldn’t be so careless, da ace kina taking precautions da ba’azo nan ba... Amma yanzu shawari d’aya ce idan har bakison haife cikin nan muje ayi flushing d’insa and start taking precautions kin fahimta...”
Siyama ta jinjina kai a hankali kana tace “Then it has to be today, like right now don banso na koma gida a halinda nake ciki....”
Laila ta jinina kai kafin Siyama ta mik’e ta rufe office d’in sukayi ficewarsu...
Suna tafe a mota take ganin sak’on shi na shigowa, a hankali ta saki murmushi kana ta furta “I’m sorry Partner.... I love you too...”
Da gefen ido Laila ke dubanta had’da tab’e baki, a haka suka karyi kwanan asibitin.....
Siyama na hawaye ga k’irjinta dake bugawa haka ta shiga d’akin operation d’in nan fuskar Sameer na mata gizo cikin zuciyarta da k’wayan idanunta...
***
Nabilah da Aunty B sukayi jigum jigum suna duban Zulfah da tun zuwansu a haka take ta kuma kasa sanar dasu meke damunta...
Nabila ta yab’e baki tace “Aunty wllhi karma ki tambaya wannan mijin nata da danginsa sun k’unsa mata wani abin ne....”
Zulfah ta aikawa Nabila harara kana ta dubi Aunty B dake dubanta a yagalgale kana tace “Aunty karki biye na wannan yarinyar ni wllhi babu komai kewar Kausar ne kawai ya addabeni...”
Aunty B ta jinjina kai tace “Ehhh naga alama ai, kewar d’iyarki shiyasa fuskarki duk ta kumbura, idan kewar d’iyarkice karki damu don yau zata dawo gareki... Nabilah tashi muje...” Aunty B ta k’arashe tana sab’a mayafi...
Nabila kaman akan k’aya take tuni ta mik’e tanaji tamkar sallah...
Zulfah tayi saurin shan gabansu tana fad’in “Aunty don Allah ku barta kawai ai idan ta gama hutun za’a dawo da ita...”
Idan gyalen Aunty B ya amsa itama zata amsa ko kula Zulfa’u batayi ba ta fizgo hannun Nabila suka fice Nabilar na kuma ingizata....
Dafe kai kurum Zulfah tayi tana ambaton Allah don tasan yau sai yanda ta kaya tsakanin su Nabilah da Hajiya da yaranta...
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*13*
Cikin sauri Zulfah ta koma d’aki ta zura hijab ta fice bakin layi sauri sauri tana neman adaidaita.....
***
Raihana suka tadda tsakar gidan goyeda Kausar tana dakar d’anyar kub’iyar miyan dare ga k’amshi daddawa dake faman tashi alamun ta d’aura sanwa tuni....
Baki har kunne ta k’araso ta rungume Nabilah tana masu sannu da zuwa don ba barinta ake taje gidajen Baffahnin nata ba balle taga ‘yan uwan nata....
Nabilah sai faman binta da kallo take yanda duk ta zagwanye ta wani lalace ba kaman yanda ta ganta kwanan baya ba kafin a masu hutun makaranta don makaranta d’aya Raihana da Marliya autar Mamy suke hasalima ajinsu guda ga islamiya ma anyi hutu duk kad’aici ya isheta, Kausar ce mai d’ibe mata kewa don d’an zaman da yarinyar tayi a gidan har sun saba....
“Addah Nabilah Ina Marliya wato tinda akayi hutu ko lek’owa ta dainayi....”
Nabilah dai dubanta kawai take cikeda mamakin wai dama Raihana ke abincin gidan Baba Alhaji lallai Hajiya ta cika azzaluma...
“Raiha kece mai abincin...?”
Nabilah ta tambaya tana dafe da Raihanar...
Murmushin yak’e Raihana tayi kana ta jinjina kai lokaci guda tana mai jijjiga Kausar dake bayanta...
“Toh ina sauran gardayen gidan kike girki ke kad’ai...?”
Raihanah ta d’an juya a tsorace ta hangi k’ofar parlorn Hajiya kana tace “Aunty Sahariyya tana d’aki tana bacci Najah kuma sun fita ina tsammanin ta raka Hajiya unguwa ne.... Amma ai na saba Addah Nabilah kullum ni nakeyi...” Tayi maganar tana mai murmushi mai cikeda ban tausayi...
Dafata Aunty B tayi kana tace “Karki damu yarinya idan sunyi tunanin cutarki suke k’wararki suke sunyi kuskure domin kuwa kece dai kikaci ribar zama dasu duk yanda kikaje a rayuwa babu yanda bazaki iya zama ba don haka kece kikaci ribar zamada Hajiya kinji koh...”
A hankali Raihanah ke jinjina kai tana shafa hannayenta da tuni sunyi kanta sabida tsananin tuk’a tuwo mai tarin yawa da ake aikawa kasuwa da sauran aikace aikace da suka girmi shekarunta....
Nabilah ta dubi Aunty suna jinjina mugunta irinta Hajiyar Hafiz kana tace “Aunty sauk’i abin Raiha na nan kuma na tabbata tana kulada Kausar amma da wa yasan yanda zasu ballagazantar da yarinyar nan don bawai imani ne dasu ba...”
Aunty tace “Sauk’ota mu ganta...”
Babu musu Raihana ta soma kiciniyar sauk’e Kausar take ta soma rusa kuka alamun baccin tsoro tayi....
Sahariyya da ta sinkayo kukan nata tamkar a mafarki uban tsuka ta buga kana ta yaye labulen window tana fad’in “Ke Raiha kukan uban mai kuma yarinyar nan keyi....?”
Cak ta tsaya da kalaman nata tana kuma k’anne idanunta masu cikeda bacci tana hango fuskokin Nabila da Aunty B dake faman danna mata mummunar kallo....
“Ke Raiha su waye wad’annan tsaye sunama mutane kallon raini...?”
Kafin Raihana ta bata amsa ta sinkayo muryar Aunty B mai cikeda charisma tana fad’in “Uwarki ne... Tambad’edd’iya marar kunya...”
Kambala’in chan.... Sahariyya ta ambata cikin zuciyarta, lallai zata shayar da matar nan mamaki don ta lura kan matar hayak’i....
Bai daina huci ba ya shiga duba kiranda ta amsa, d’ago murtuk’ekk’en fuskar da babu alamun annuri cikinta yayi kana yace “Ubanwa yace ki amsa min waya....?!”
Bata amsa shi ba haka nan bata d’ago idanu ta dubeshi ba.,,,
Ya kuma daka mata tsawa “Nace da izinin ubanwa kika d’aga min waya...? Yaushema kika soma tab’a min wayata a gidan nan...?”
Shiru bata bashi amsa ba...
“Ba magana nake miki ba..!!” Ya kuma daka mata tsawa...
Saida tasa tafukan hannayenta ta share hawaye suka sauk’o fuskarta kana tayi k’ok’arin saita kanta tace “Kayi hak’uri....” A tak’aice....
Huci kawai yake yana dubanta kana yayi k’wafa yaci gaba da fad’in “Sai kinyi abu kicewa mutum yayi hak’uri bayan ni hak’urin zama dake nake, an lik’amin ke ana tausana ana bani hak’urin ci gaba da zama dake matar da babu wani alkhairi a tattaredake face sharri.. Wllhi kinji na rantse zan maki kashedi na k’arshe duk ranar da aka kuma kirata kika d’aga sai na karyaki kafin na maidake gidan iyayenki su baki tarbiya da kyau, duk kuma abinda kikaji daga wayata ke kika jiyowa kanki don babu ubanda ya aikeki d’agawa... Jaka mai farar k’afa....”
Yana gama yab’a mata munan kalamai yayi shirinsa abinsa ya fice yana neman layin Sawwama da tak’i d’aga kiransa....
Can k’uryar d’aki Zulfah ta rakub’e idnunta na mata wani irin barkono don kukan ma nemansa tayi ta rasa, wannan shine mijin da mahaifinta ya zab’ar mata zama dashi har yake ikirarin idan tayi abunda aka sakota babu ita babu shi sannan kada ta dawo masa gida ta nemi wani uban ba shi ba, ita kuma kalan tata k’addarar kenan, haka Allah yaso ya jarabceta, inama ace Hafiz ya tsaya a zagi da wulak’anci kawai, inama ace aure ya k’ara ba bin matan titi ba, shin wannan shine wanda iyayenta suka zab’ar mata tayi rayuwar sunnah dashi..? Wannan shine uban ‘ya’yanta da zasu tashi suyi alfahari dashi su nunashi suce ga mahaifinsu...? Shin idan iyayenta sun zab’ar mata wannan mutumin ita tayi adalci wa ‘ya’yan da zata haifa kenan....? Take wasu hawaye masu tsananin rad’ad’i taji suna gangaro mata... Ta jima tak’ure a wajen tanayin mai isarta kafin ta mik’e ta nufi band’aki ta d’auro alwala ta shiga mik’a kukanta ga Ubangiji wanda batada gatan da yafi Shi.....
***
Tun bayan shigowarta office d’in tayi amai ak’alla sau uku kenan, harta coffee d’in da sakatariyarta ta kawo mata hamamin kawai saida ya sata k’waza amai, gaba d’aya ta zama pale and weak, batajin kuzari sam a tattareda ita ga tashin zuciya da ya addabeta, a halin yanzu bata buk’atan komai face hutu saidai zamanta a office d’in ya fiye mata don bataso Ammy ta fahimci halin da take ciki idan har abinda take zargi ya tabbata....
Wani aman ne yazo mata ta mik’e a guje ta kuma fad’awa bathroom tana kumayi... Tamkar zata amayar harda ‘yan hanjinta haka take nishi....
Da k’yar da dafe bango ta fito daga bathroom d’in yanda ta tadda aminiyarta k’wara d’aya tak a duniya zaune saman kujera mai kallon nata damuwa kwance saman fuskarta alamun taji yanda take k’waza aman....
Kallo guda Siyama tayiwa Laila ta d’auke kai kafin ta isa k’aramar fridge d’in dake a cikin office d’in ta d’auko chocolate tana afawa a bakinta ko zata sami sauk’in tashin zuciyar da ya addabeta....
Zama tayi saman kujerarta ta d’an kishingid’a had’ida lumshe idanu tana mai maida numfashi a hankali....
Kaman daga sama ta tsinkayo muryar Laila tana fad’in “Siyama wai bazakije asibiti ba kina zaune da ciwo, ki duba ki gani yau d’aya yanda kika lalace....
Gyara zamanta ta d’anyi kana tace “Laila bazaki gane ba, ni na rigada nasan abinda ke damuna amma saidai idan shid’in ne I’m not ready yet, Wllhi ban shirya zama uwa ba, ban shirya d’aukan responsibilities ba Laila not now....”
K’uri Laila ta mata kana tace “Tirk’ashi, toh amma kema kinyi kuskure da kika bari kika d’auki ciki baki shirya ba...”
Siyama ta jinjina kai tace “I know Laila, wllhi na sani shiyasa ma na kiraki don bansan yaya zanyi ba sauk’ina d’aya Sameer baya nan balle ya fahimci wani abu...”
Laila ta tab’e baki kad’an kana tace “Toh yanzu da kika riga kika d’auki cikin me kike so ayi, nidai a nawa ganin kawai ki hak’uri ki haife abinki tinda dai dama bamu isa muce komai sai mun shirya ma zuwansa ba, just take the risks ki haifa kawai....”
Banda harara Siyama bata aika mata komai, gajeren tsaki tayi kana tace “You’re not helping... Idan na haihu yanzu komai na rayuwata canzawa zatayi, harta d’anda na haifah can come between us nida Partner, maybe ma yafi son d’an sama dani sannan zan iya rasa attention d’in mijina gaba d’aya... Bama wannan ba kawai I’m not ready to become a mother......”
Laila ta jinjina kai kana tace “Tun farko you shouldn’t be so careless, da ace kina taking precautions da ba’azo nan ba... Amma yanzu shawari d’aya ce idan har bakison haife cikin nan muje ayi flushing d’insa and start taking precautions kin fahimta...”
Siyama ta jinjina kai a hankali kana tace “Then it has to be today, like right now don banso na koma gida a halinda nake ciki....”
Laila ta jinina kai kafin Siyama ta mik’e ta rufe office d’in sukayi ficewarsu...
Suna tafe a mota take ganin sak’on shi na shigowa, a hankali ta saki murmushi kana ta furta “I’m sorry Partner.... I love you too...”
Da gefen ido Laila ke dubanta had’da tab’e baki, a haka suka karyi kwanan asibitin.....
Siyama na hawaye ga k’irjinta dake bugawa haka ta shiga d’akin operation d’in nan fuskar Sameer na mata gizo cikin zuciyarta da k’wayan idanunta...
***
Nabilah da Aunty B sukayi jigum jigum suna duban Zulfah da tun zuwansu a haka take ta kuma kasa sanar dasu meke damunta...
Nabila ta yab’e baki tace “Aunty wllhi karma ki tambaya wannan mijin nata da danginsa sun k’unsa mata wani abin ne....”
Zulfah ta aikawa Nabila harara kana ta dubi Aunty B dake dubanta a yagalgale kana tace “Aunty karki biye na wannan yarinyar ni wllhi babu komai kewar Kausar ne kawai ya addabeni...”
Aunty B ta jinjina kai tace “Ehhh naga alama ai, kewar d’iyarki shiyasa fuskarki duk ta kumbura, idan kewar d’iyarkice karki damu don yau zata dawo gareki... Nabilah tashi muje...” Aunty B ta k’arashe tana sab’a mayafi...
Nabila kaman akan k’aya take tuni ta mik’e tanaji tamkar sallah...
Zulfah tayi saurin shan gabansu tana fad’in “Aunty don Allah ku barta kawai ai idan ta gama hutun za’a dawo da ita...”
Idan gyalen Aunty B ya amsa itama zata amsa ko kula Zulfa’u batayi ba ta fizgo hannun Nabila suka fice Nabilar na kuma ingizata....
Dafe kai kurum Zulfah tayi tana ambaton Allah don tasan yau sai yanda ta kaya tsakanin su Nabilah da Hajiya da yaranta...
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*13*
Cikin sauri Zulfah ta koma d’aki ta zura hijab ta fice bakin layi sauri sauri tana neman adaidaita.....
***
Raihana suka tadda tsakar gidan goyeda Kausar tana dakar d’anyar kub’iyar miyan dare ga k’amshi daddawa dake faman tashi alamun ta d’aura sanwa tuni....
Baki har kunne ta k’araso ta rungume Nabilah tana masu sannu da zuwa don ba barinta ake taje gidajen Baffahnin nata ba balle taga ‘yan uwan nata....
Nabilah sai faman binta da kallo take yanda duk ta zagwanye ta wani lalace ba kaman yanda ta ganta kwanan baya ba kafin a masu hutun makaranta don makaranta d’aya Raihana da Marliya autar Mamy suke hasalima ajinsu guda ga islamiya ma anyi hutu duk kad’aici ya isheta, Kausar ce mai d’ibe mata kewa don d’an zaman da yarinyar tayi a gidan har sun saba....
“Addah Nabilah Ina Marliya wato tinda akayi hutu ko lek’owa ta dainayi....”
Nabilah dai dubanta kawai take cikeda mamakin wai dama Raihana ke abincin gidan Baba Alhaji lallai Hajiya ta cika azzaluma...
“Raiha kece mai abincin...?”
Nabilah ta tambaya tana dafe da Raihanar...
Murmushin yak’e Raihana tayi kana ta jinjina kai lokaci guda tana mai jijjiga Kausar dake bayanta...
“Toh ina sauran gardayen gidan kike girki ke kad’ai...?”
Raihanah ta d’an juya a tsorace ta hangi k’ofar parlorn Hajiya kana tace “Aunty Sahariyya tana d’aki tana bacci Najah kuma sun fita ina tsammanin ta raka Hajiya unguwa ne.... Amma ai na saba Addah Nabilah kullum ni nakeyi...” Tayi maganar tana mai murmushi mai cikeda ban tausayi...
Dafata Aunty B tayi kana tace “Karki damu yarinya idan sunyi tunanin cutarki suke k’wararki suke sunyi kuskure domin kuwa kece dai kikaci ribar zama dasu duk yanda kikaje a rayuwa babu yanda bazaki iya zama ba don haka kece kikaci ribar zamada Hajiya kinji koh...”
A hankali Raihanah ke jinjina kai tana shafa hannayenta da tuni sunyi kanta sabida tsananin tuk’a tuwo mai tarin yawa da ake aikawa kasuwa da sauran aikace aikace da suka girmi shekarunta....
Nabilah ta dubi Aunty suna jinjina mugunta irinta Hajiyar Hafiz kana tace “Aunty sauk’i abin Raiha na nan kuma na tabbata tana kulada Kausar amma da wa yasan yanda zasu ballagazantar da yarinyar nan don bawai imani ne dasu ba...”
Aunty tace “Sauk’ota mu ganta...”
Babu musu Raihana ta soma kiciniyar sauk’e Kausar take ta soma rusa kuka alamun baccin tsoro tayi....
Sahariyya da ta sinkayo kukan nata tamkar a mafarki uban tsuka ta buga kana ta yaye labulen window tana fad’in “Ke Raiha kukan uban mai kuma yarinyar nan keyi....?”
Cak ta tsaya da kalaman nata tana kuma k’anne idanunta masu cikeda bacci tana hango fuskokin Nabila da Aunty B dake faman danna mata mummunar kallo....
“Ke Raiha su waye wad’annan tsaye sunama mutane kallon raini...?”
Kafin Raihana ta bata amsa ta sinkayo muryar Aunty B mai cikeda charisma tana fad’in “Uwarki ne... Tambad’edd’iya marar kunya...”
Kambala’in chan.... Sahariyya ta ambata cikin zuciyarta, lallai zata shayar da matar nan mamaki don ta lura kan matar hayak’i....