Sashe 32
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba d’aya sunyi zaune a mahad’a suna jiran k’arasowar aminiyar sirri, Hajiya tace “Lami anya Aminiya zatazo...?”
Lami tace “Dole ma tazo domin kuwa idan asiri ya tonu ba mu kad’aine a rana ba saima ta fimu shiga...”
Hajiya ta jinjina kai tana buga hannayenta a hankali tana waige waigen ta yanda zata hango Aminiyar sirri...
Daga can suka hango mai tasi ya ajiyeta tana k’arasowa yanda suke sai waige waige take tamkar mai tsoron kada wani ya hangota...
A tare Lami da Haule suka kalli juna kafin suka mik’e gaba d’aya sanda ta k’araso....
“Aminiyar sirri ganin ki yayi wahala...” Hajiya tace sanda take dubanta
Murmushi matar ta saki wacce batakaisu a shekare ba kana tace “Haule, Lami shekaru talatin baya babu abinda ya canza a rayuwarku......”
Lami ta nuna mata kujera kana tace “Sirrin dake b’oye shekaru talatin baya yana neman ya bayyana kanshi...”
Murmushi Aminiyar Sirri ta saki kana tace “Mai kuke tunanin zai bayyanashi idan ba d’aya daga cikinku bane ta bud’i baki ta fad’i...”
Haule tai saurin katseta “Tabbas mukeda babban dalili domin kaw Ma’aruf muke gani yana neman dawowa cikin rayuwarmu...”
Ta kuma murmusawa kana tace “Bazaku tab’a canzawa ba.... Amma..” Ta k’arashe tana bud’e zip d’in jakanta...
Kayan k’aramin yaro ta ciro d’aukeda bushesshen jini ta shiga warware masu...
Lami da Haule suka dubi juna tabbas wannan shine kayan dake jikin Ma’aruf sanda suka sabautar dashi...
Aminiyar sirri ta murmusa tace “Meyasa kuke tunanin zanbar Ma’aruf a raye bayan duk duniya babu aninda na tsana irin farin cikin mahaifiyarsa kuma nasan dani daku akan haka mukayi tarayya...”
Haule da Lami suka kuma duban juna kana sukace “Aminiya idan kikaga abinda muka gani kema zaki yarda cewa tabbas Ma’aruf na raye....”
K’uri ta masu kana tace “Laifukanku suke bibiyarku suka hanaku sukuni amma ina mai tabbatar maku ba Ma’aruf kuka gani ba, Ma’aruf ya jima da zama tarihi don haka idan bakune kuke son tonowa kanku ba kada ku bud’e sirrinku da kanku, randa duk aka fahimci akwai aminci na sirri tsakaninmu sanin kanku ne zargi zai mana yawa don haka shawarina a nan shine muci gaba da nisanta kanmu da juna domin tsira da mutuncinmu...”
Haule da Lami suka dubi juna bawai don sun gamsu da ita ba...
Har suka bar wajen hankulansu ba’a nitse yake ba, yauma kaman kullum Lami aka soma sauk’ewa kafin aka wuce da Hajiya..
Nabila da dawowarta kenan daga makaranta taga Aunty Lami ta sauk’a adaidaita guda da Hajiyar Yaya Hafiz, maganar da sukai da safe itada Marliya ya kuma dawo mata Sabo, wannan matar tabbas akwai abinda take b’oyewa ba abin kayi sharing da Mamy ba ba yarda zatai ba saidaima tace rashin kunyarka ne, amma what so ever she’s hiding saita tono shi da yardar Allah.. As they say no secret remains hidden forever...
Cikin sauri ta k’araso murmushi saman fuskarta ganin Aunty Lami d’in zata shige cikin gida..
“Aunty sannu da dawowa...” Tayi maganar fuska fal fari’a abinda bata saba yi mata ba...
Aunty Lami ta dubeta da mamaki don koda wasa Nabila bata tab’a mata hakan ba... Murmushin yak’e Aunty Lami tai kana tace “Yauwa Nabila ‘yan makaranta an dawo...”
Nabilah ta jinjina kai had’ida amsar jakan hannun Aunty Lami ta rik’e mata suka jera tare suka nufi cikin gida Nabilah na fad’in “Lecture d’aya nayi shiyasa ban fita da wuri ba na kuma dawo da wuri..”
Aunty Lami ta jinjina kai tana mamakin yanda Nabilah ta sake tana mata fira, har sashenta Nabilah tai mata rakiya rik’eda jakan Aunty Lami d’in, tai mata tayin abinci tace ta k’oshi, tai mata sallama fuska fal fari’a kana ta fice..
Aunty Lami sai mamakin canzawan Nabilah take lokaci guda....
***
Hankalin Sameer ya gaza kwanciya, sosai yake son tafiya gida sabida d’inbin tambayoyi da yakeson yima iyayenshi, washe gari ya shirya tafiya Kaduna ba tareda ya sanar da kowa ba don koh Siyama bai sanar da ita ba....
Kai tsaye gidansa ya shige don hutawa kafin ya nufi can gidan iyayenshi..
Kai tsaye ya nufi bedroom d’insu ya shiga rage kayan jikinsa donyin wanka, ya k’arasa bedside ya aje agogonsa da ya cire nan yaji k’afarsa ya taka wani abu kaman gidan magani..
Kai dubansa k’asa aiko gidan maganin ya taka...
Ya shiga duk’awa a hankali k’irjinsa na tsananin bugu abinka da likita yana fata cikin zuciyarsa Allah yasa ba maganin da yake tunani bane... Wani irin bugu k’irjin Sameer yayi sanda ya d’auki maganin ya shiga juyawa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*28*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Jiri ne yaji na niman d’ibanshi daga yanda yake durk’ushe, take idanunsa suka kad’a sukai jazir... Cikin wani irin yanayi yake furta “How could you... How could you do this to me Siyama...” Kasa ci gaba da magana yayi sai k’ok’arin mik’ewa da yake cikin sanyin jiki...
Ya d’aga idanu yana duban picture d’insu dake ajiye gefen bedside d’in cikin k’aramar frame su duka biyun suna cikin tsananin farin ciki, take yasa hannu ya d’auko hoton had’ida k’ura mata idanun da suka koma jajazir, inama ace abinda yake gani ba gaskiya bane, Siyama itace mace guda da ya tab’a so tsawon rayuwarsa, shin da gaske ita bata sonshi to the point that bata k’aunar had’a jini dashi... Shin mai ya mata da tsanani shin menene laifinsa, shin tsananin soyayyar da yake mata ne laifinsa.... Siririyar hawaye mai tsananin zafi ya gangaro mashi...
A hankali ya maida hoton ya ajiye, wankan da bai iya yayi ba kenan yasa kai ya fito daga d’akin, tamkar wanda ruwa ya shanye haka Sameer ke d’aga k’afafunsa,da k’yar ya iya sauk’owa daga staircase yaji jiri na neman kifa shi, zama yayi cikin kujera had’ida k’urama waje guda idanu, fatar jikinsa ta koma jazir haka nan idanunsa, abubuwa da dama ke ziyartar zuciyarsa....
***
Yesmin ba’a sama ba’a k’asa yau dai so ake a birge oga Khalid da alama, gaba d’aya abincin gidan ta d’auki ragama ta hana ma’aikatan saka hannu, Kubura ta cika tayi fam duk wani juyi da Yesmin zatai a kitchen harara kurum take aika mata had’ida tab’e baki musamman idan ta tuna wai duk don a janyo hankalin Khalid d’inta ake wannan abun.. Sai ‘yan wak’e wak’enta take na habaici tana giftawa...
Yesmin kaw ko a jikinta sai rawar kai ake ana kiran Mummy tana kuma turo wasu recipes d’in, dama tun safe driver ya kaita tayo shopping d’inta da kanta abubuwan da tasan bazata samu a store ba...
Ammi ce ta shigo kitchen d’in ta tadda Yesmin kace kace sai aiki take...
Ammi na murmushi take fad’in “A’a lallai yau munada cin delicious babbar chef ce a kitchen d’in namu...”
Yesmin ta murmusa cikeda kunya kana tace “I love cooking Ammi...”
Ammi ta murmusa kana tace “Toh what’s the occasion, what are we celebrating...?”
Nan ma cikeda kunya ta kuma murmusawa kana tace “Ammi I hope Khalid will like it....”
Ammi ta d’an matso kusanta had’ida dafata kad’an kana tace “I’m sure he’s going to love it sweetheart... Mamanki ta fad’a min your passion about cooking tun kina k’arama unlike your own cousin Siyama wacce saidai a dafa a bata, I’m sure d’ana yayi dace..”
Yesmin ta kuma murmusawa cikeda jin dad’i kana tace “Thank you Ammi..” Suka rungume juna cikeda jin dad’i kafin Ammi ta fice ta bar Yesmin a kitchen tana ci gaba da hidimanta had’ida dad’a zak’ewa...
Bayan komai ya kammala Yesmin ta umarci su Kubura su jera komai bisa dining ita kuma ta wuce sama ta tsala wanka had’ida cancad’a kwalliya...
Siyama data dawo a gajjiye nan taga ma’aikatan sai kai komo suke suna jeren had’add’un dishes da warmers...
K’arasawa tayi ta shige bud’ewa ko wanne tana tab’awa tana lumshe idanu had’ida kad’a kunne don santi..
Yesmin ta fito ta taddata a haka, k’arasowa tai ta d’an tab’a Siyama kana tace “How do I look...?” Tai maganar tana juyi gaban Siyama..
Siyama ta jinjina kai tana had’iye abinda ke bakinta kana tace “Um gorgeous, you look just good... So, is my brother here...?”
Yesmin ta d’an murmusa kana tace “Not yet, but I’m sure he’s on his way...”
Siyama ta jinjina kai tace “You cook all this...?”
Yesmin ta jinjina kai tana juya idanu
Siyama ta d’an tab’e baki tana jinjina kai tace “Lallai Khalid is lucky, niko kinga babu abinda na iya when it comes to kitchen, Sameer shikeyin komai... Kinga let me go take shower sai nazo muyima abincin nan cin gaske cos I’m really really starving...”
Jinjina kai Yesmin tai kafin taci gaba da kallon kanta cikin k’aton madubi da aka k’awata dining area d’in dashi...
Kubura na lab’e tana dubanta ta cika tayi fam, jira kawai take Yesmin ta kauce ta cika aikinta...
Suna zazzaune bisa dining d’in saidai basu fara cin abincin ba fira suke kanyi Khalid yayi sallama ya shigo, kallo guda zaka masa ka fahimci a stananin gajjiye yake, kusan komai yanzu sakar masa Daddy yake a company d’in a cewarsa he wants him to grow up, ballanta yanzu da Daddy yake on a business trip komai sakarwa Khalid d’in yake...
Ammi ta sakar masa murmushi kana tace “You arrived just on time son.... k’araso”
Murmushi ya sakar mata kana ya gaidata bata saki hannunsa ba saida ta zaunar dashi saman kujera tana fad’in “Lets eat son,...”
Ammi ta shiga serving d’insa da kanta, Yesmin kaw sai faman sinne kai take musamman da taji Khalid na cewa yunwa dama yakeji amma yaso ya fara yin wanka, Ammi tace a’a shi kawai suke jira sai sunci abinci tukuna...
Lami tace “Dole ma tazo domin kuwa idan asiri ya tonu ba mu kad’aine a rana ba saima ta fimu shiga...”
Hajiya ta jinjina kai tana buga hannayenta a hankali tana waige waigen ta yanda zata hango Aminiyar sirri...
Daga can suka hango mai tasi ya ajiyeta tana k’arasowa yanda suke sai waige waige take tamkar mai tsoron kada wani ya hangota...
A tare Lami da Haule suka kalli juna kafin suka mik’e gaba d’aya sanda ta k’araso....
“Aminiyar sirri ganin ki yayi wahala...” Hajiya tace sanda take dubanta
Murmushi matar ta saki wacce batakaisu a shekare ba kana tace “Haule, Lami shekaru talatin baya babu abinda ya canza a rayuwarku......”
Lami ta nuna mata kujera kana tace “Sirrin dake b’oye shekaru talatin baya yana neman ya bayyana kanshi...”
Murmushi Aminiyar Sirri ta saki kana tace “Mai kuke tunanin zai bayyanashi idan ba d’aya daga cikinku bane ta bud’i baki ta fad’i...”
Haule tai saurin katseta “Tabbas mukeda babban dalili domin kaw Ma’aruf muke gani yana neman dawowa cikin rayuwarmu...”
Ta kuma murmusawa kana tace “Bazaku tab’a canzawa ba.... Amma..” Ta k’arashe tana bud’e zip d’in jakanta...
Kayan k’aramin yaro ta ciro d’aukeda bushesshen jini ta shiga warware masu...
Lami da Haule suka dubi juna tabbas wannan shine kayan dake jikin Ma’aruf sanda suka sabautar dashi...
Aminiyar sirri ta murmusa tace “Meyasa kuke tunanin zanbar Ma’aruf a raye bayan duk duniya babu aninda na tsana irin farin cikin mahaifiyarsa kuma nasan dani daku akan haka mukayi tarayya...”
Haule da Lami suka kuma duban juna kana sukace “Aminiya idan kikaga abinda muka gani kema zaki yarda cewa tabbas Ma’aruf na raye....”
K’uri ta masu kana tace “Laifukanku suke bibiyarku suka hanaku sukuni amma ina mai tabbatar maku ba Ma’aruf kuka gani ba, Ma’aruf ya jima da zama tarihi don haka idan bakune kuke son tonowa kanku ba kada ku bud’e sirrinku da kanku, randa duk aka fahimci akwai aminci na sirri tsakaninmu sanin kanku ne zargi zai mana yawa don haka shawarina a nan shine muci gaba da nisanta kanmu da juna domin tsira da mutuncinmu...”
Haule da Lami suka dubi juna bawai don sun gamsu da ita ba...
Har suka bar wajen hankulansu ba’a nitse yake ba, yauma kaman kullum Lami aka soma sauk’ewa kafin aka wuce da Hajiya..
Nabila da dawowarta kenan daga makaranta taga Aunty Lami ta sauk’a adaidaita guda da Hajiyar Yaya Hafiz, maganar da sukai da safe itada Marliya ya kuma dawo mata Sabo, wannan matar tabbas akwai abinda take b’oyewa ba abin kayi sharing da Mamy ba ba yarda zatai ba saidaima tace rashin kunyarka ne, amma what so ever she’s hiding saita tono shi da yardar Allah.. As they say no secret remains hidden forever...
Cikin sauri ta k’araso murmushi saman fuskarta ganin Aunty Lami d’in zata shige cikin gida..
“Aunty sannu da dawowa...” Tayi maganar fuska fal fari’a abinda bata saba yi mata ba...
Aunty Lami ta dubeta da mamaki don koda wasa Nabila bata tab’a mata hakan ba... Murmushin yak’e Aunty Lami tai kana tace “Yauwa Nabila ‘yan makaranta an dawo...”
Nabilah ta jinjina kai had’ida amsar jakan hannun Aunty Lami ta rik’e mata suka jera tare suka nufi cikin gida Nabilah na fad’in “Lecture d’aya nayi shiyasa ban fita da wuri ba na kuma dawo da wuri..”
Aunty Lami ta jinjina kai tana mamakin yanda Nabilah ta sake tana mata fira, har sashenta Nabilah tai mata rakiya rik’eda jakan Aunty Lami d’in, tai mata tayin abinci tace ta k’oshi, tai mata sallama fuska fal fari’a kana ta fice..
Aunty Lami sai mamakin canzawan Nabilah take lokaci guda....
***
Hankalin Sameer ya gaza kwanciya, sosai yake son tafiya gida sabida d’inbin tambayoyi da yakeson yima iyayenshi, washe gari ya shirya tafiya Kaduna ba tareda ya sanar da kowa ba don koh Siyama bai sanar da ita ba....
Kai tsaye gidansa ya shige don hutawa kafin ya nufi can gidan iyayenshi..
Kai tsaye ya nufi bedroom d’insu ya shiga rage kayan jikinsa donyin wanka, ya k’arasa bedside ya aje agogonsa da ya cire nan yaji k’afarsa ya taka wani abu kaman gidan magani..
Kai dubansa k’asa aiko gidan maganin ya taka...
Ya shiga duk’awa a hankali k’irjinsa na tsananin bugu abinka da likita yana fata cikin zuciyarsa Allah yasa ba maganin da yake tunani bane... Wani irin bugu k’irjin Sameer yayi sanda ya d’auki maganin ya shiga juyawa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*28*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Jiri ne yaji na niman d’ibanshi daga yanda yake durk’ushe, take idanunsa suka kad’a sukai jazir... Cikin wani irin yanayi yake furta “How could you... How could you do this to me Siyama...” Kasa ci gaba da magana yayi sai k’ok’arin mik’ewa da yake cikin sanyin jiki...
Ya d’aga idanu yana duban picture d’insu dake ajiye gefen bedside d’in cikin k’aramar frame su duka biyun suna cikin tsananin farin ciki, take yasa hannu ya d’auko hoton had’ida k’ura mata idanun da suka koma jajazir, inama ace abinda yake gani ba gaskiya bane, Siyama itace mace guda da ya tab’a so tsawon rayuwarsa, shin da gaske ita bata sonshi to the point that bata k’aunar had’a jini dashi... Shin mai ya mata da tsanani shin menene laifinsa, shin tsananin soyayyar da yake mata ne laifinsa.... Siririyar hawaye mai tsananin zafi ya gangaro mashi...
A hankali ya maida hoton ya ajiye, wankan da bai iya yayi ba kenan yasa kai ya fito daga d’akin, tamkar wanda ruwa ya shanye haka Sameer ke d’aga k’afafunsa,da k’yar ya iya sauk’owa daga staircase yaji jiri na neman kifa shi, zama yayi cikin kujera had’ida k’urama waje guda idanu, fatar jikinsa ta koma jazir haka nan idanunsa, abubuwa da dama ke ziyartar zuciyarsa....
***
Yesmin ba’a sama ba’a k’asa yau dai so ake a birge oga Khalid da alama, gaba d’aya abincin gidan ta d’auki ragama ta hana ma’aikatan saka hannu, Kubura ta cika tayi fam duk wani juyi da Yesmin zatai a kitchen harara kurum take aika mata had’ida tab’e baki musamman idan ta tuna wai duk don a janyo hankalin Khalid d’inta ake wannan abun.. Sai ‘yan wak’e wak’enta take na habaici tana giftawa...
Yesmin kaw ko a jikinta sai rawar kai ake ana kiran Mummy tana kuma turo wasu recipes d’in, dama tun safe driver ya kaita tayo shopping d’inta da kanta abubuwan da tasan bazata samu a store ba...
Ammi ce ta shigo kitchen d’in ta tadda Yesmin kace kace sai aiki take...
Ammi na murmushi take fad’in “A’a lallai yau munada cin delicious babbar chef ce a kitchen d’in namu...”
Yesmin ta murmusa cikeda kunya kana tace “I love cooking Ammi...”
Ammi ta murmusa kana tace “Toh what’s the occasion, what are we celebrating...?”
Nan ma cikeda kunya ta kuma murmusawa kana tace “Ammi I hope Khalid will like it....”
Ammi ta d’an matso kusanta had’ida dafata kad’an kana tace “I’m sure he’s going to love it sweetheart... Mamanki ta fad’a min your passion about cooking tun kina k’arama unlike your own cousin Siyama wacce saidai a dafa a bata, I’m sure d’ana yayi dace..”
Yesmin ta kuma murmusawa cikeda jin dad’i kana tace “Thank you Ammi..” Suka rungume juna cikeda jin dad’i kafin Ammi ta fice ta bar Yesmin a kitchen tana ci gaba da hidimanta had’ida dad’a zak’ewa...
Bayan komai ya kammala Yesmin ta umarci su Kubura su jera komai bisa dining ita kuma ta wuce sama ta tsala wanka had’ida cancad’a kwalliya...
Siyama data dawo a gajjiye nan taga ma’aikatan sai kai komo suke suna jeren had’add’un dishes da warmers...
K’arasawa tayi ta shige bud’ewa ko wanne tana tab’awa tana lumshe idanu had’ida kad’a kunne don santi..
Yesmin ta fito ta taddata a haka, k’arasowa tai ta d’an tab’a Siyama kana tace “How do I look...?” Tai maganar tana juyi gaban Siyama..
Siyama ta jinjina kai tana had’iye abinda ke bakinta kana tace “Um gorgeous, you look just good... So, is my brother here...?”
Yesmin ta d’an murmusa kana tace “Not yet, but I’m sure he’s on his way...”
Siyama ta jinjina kai tace “You cook all this...?”
Yesmin ta jinjina kai tana juya idanu
Siyama ta d’an tab’e baki tana jinjina kai tace “Lallai Khalid is lucky, niko kinga babu abinda na iya when it comes to kitchen, Sameer shikeyin komai... Kinga let me go take shower sai nazo muyima abincin nan cin gaske cos I’m really really starving...”
Jinjina kai Yesmin tai kafin taci gaba da kallon kanta cikin k’aton madubi da aka k’awata dining area d’in dashi...
Kubura na lab’e tana dubanta ta cika tayi fam, jira kawai take Yesmin ta kauce ta cika aikinta...
Suna zazzaune bisa dining d’in saidai basu fara cin abincin ba fira suke kanyi Khalid yayi sallama ya shigo, kallo guda zaka masa ka fahimci a stananin gajjiye yake, kusan komai yanzu sakar masa Daddy yake a company d’in a cewarsa he wants him to grow up, ballanta yanzu da Daddy yake on a business trip komai sakarwa Khalid d’in yake...
Ammi ta sakar masa murmushi kana tace “You arrived just on time son.... k’araso”
Murmushi ya sakar mata kana ya gaidata bata saki hannunsa ba saida ta zaunar dashi saman kujera tana fad’in “Lets eat son,...”
Ammi ta shiga serving d’insa da kanta, Yesmin kaw sai faman sinne kai take musamman da taji Khalid na cewa yunwa dama yakeji amma yaso ya fara yin wanka, Ammi tace a’a shi kawai suke jira sai sunci abinci tukuna...