Sashe 91
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Gyara tsayuwarsa yai jikin mota k’afarsa a hard’e yana ci gaba da wasa da d’an makullin motar kana yace “Idan bazaki introducing d’ina wa Mamy ba, zan shiga nayi da kaina don dama kinsan wajen Mamani kam banida matsala.....”
Nabilah dai sai waige waige take duk a tsarge take jinta don bata saba tsayuwa da maza a waje ba kana tace “Kaga ni zan shige yanzu za’a fito masallaci sallan azahar, and banso mutane suyita kallona a nan suna wucewa....”
Ya d’an gimtse kana yace “teddy bear I’m serous, inaso family d’inki susan dani sabida bada wasa nazo ba.....” Yayi maganar babu alamun wasa a tattaredashi wanda saida ya haifarwa Nabilah da bugun zuciya.... Batasan mai zatace masa ba sai duban k’asa da tai..... Daidai lokacin Sameer ya fito daga gidan da niyyan tafiya masallaci....
Khalid yana hango Sameer ya saki murmushi don bai manta ba dama sun tab’a had’uwa a gidan saidai a wancan lokacin Sameer ya sanar masa cewa alak’asar da mutanen gidan sabo ne kawai sabida zaman unguwa guda, a halin yanzu baisan asalin alak’ar Sameer d’in da ahalin gidan ba....
K’arasowa Sameer d’in ma yai yana mamakin hango Khalid da k’anwarsa Nabilah a tare.....
“Aaa Dr ashe zan sameka a nan....” Khalid ya fad’i sanda ya shige Nabilah ya k’arasa ya baiwa Sameer hannu sukai masbaha....
Gaban Nabilah ya fad’i jin muryar Yayanta Ma’aruf suna gaisawa da Khalid.... Cikin sauri ta k’araso zata shige cikin gida, kai a k’asa taceda Sameer “Ina yini Yaya...”
Ya amsa mata a tak’aice bata kuma cewa komai ba ta shige cikin gida.....
Daga Sameer d’in har Khalid d’in kallo suka bita dashi har ta shige cikin sauri....
Sameer ya dubi Khalid yace “So you two know each other....?”
D’an shafa sumarsa yai kana tin kafin na had’uda kai a gidan nan nasan miss grumpy.....” Yai maganar yana murmushi....
Shiru Sameer ya d’anyi kana yace “Amma kasan alak’ar dake tsakanina da ita.....?”
Sai sannan Khalid ya d’ago yana dubansa with a serious face kana ya furta “Ban fahimceka ba....”
Dafasa Sameer yai yana murmushi kana yace mu k’arasa masallaci za’a shiga sallah.... Idan mun fito you’ve a lot to explain to me kasan bazan bari a yaudari k’anwata ba....” Ya k’arashe yana mai ci gaba da warware hannun rigarsa da yai folding wajen alwala
Khalid ya bisa da kallo yana mai nanata kalman k’anwata da Sameer yace har suka shige haraban masallacin
***
Yasmeen tai d’add’aya a parlorn tana ci gaba da aikin kuka wanda tin isowarta garin takeyi..... Mahaifiyarta kaw sai faman cika take tana huci, ita kad’ai takai mari takai bango tana mai jinjina rashin mutuncin da Khalid ya masu....
Cikin kuka Yesmeen taci gaba da fad’in “Momy Wllhi nayi imani Kano ya tafi wajen tsinanniyar can ya tafi tinda gashi Ammi tayi waya tana tambayar mun sauk’a lafiya... Momy nidai Wllhi bazan tab’a bari Khalid ya auri wata bani ba... Kigafah kalan wulak’ancin da yamin ya barni a train station yayi tafiyarsa.....” Ta k’arashe tana mai kuma jejjefa k’afafu tana kururuwa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*71*
Mamakine ya cika Khalid jin cewa Iyayen Nabilah sune Iayayen Sameer na asali, wannan shine ikon Allah, who would’ve thought mutanen da Siyama ta tsana zasu juya su zama dangin mijinta....? Yai k’asaitaccen murmushi a hankali yana mai jinjina kai Don ko babu komai sosai abin ya masa zak’i.... Yana ganin kiran Ammi na shigo masa yayi biris yak’i d’agawa don yasan k’arshen zancen, k’arshe ma saka wayar yai a flight mode sanin cewa bazasu daina kiran nasa ba... Yana can sashen Mamani suna firan Yaushe rabo yayinda Sameer ke zaune parlorn Mamy suna tattaunawa kan batun Khalid d’in da Nabilah.....
Mamy ta sauk’e ajiyan zuciya kana tace “Amma Ma’aruf kana ganin wannan al’amari mai d’orewa ne..? Banso azo ana samun sab’ani musamman da ya kasance d’anuwan matarka ne....”
Turowa kad’an yai daga cikin kujera kana yace “Mamy munyi magana sosai da Khalid kuma ya tabbatar min cewa da aure yake son Nabilah, sannan na yarda da halayya da d’abi’un Khalid Mamy... Yana dai da hali irin nasa na rashinji wasu lokutan but I assure you he’s a good person... Bawai don ya kasance dan uwa ga Siyama ba no, na sanshi tun yaranta yaron kirki ne Mamy... Amma saidai wani hanzari ba gudu ba...”
Mamy ta d’ago tana dubansa kana tace “Umhum ina saurarenka....”
Sameer ya d’an fuzar da iska kana yace “Mamy iyayen Khalid suna yunk’urin had’a aurensa da wata ‘yar uwarsa ce wanda sam shi bai k’aunarta... Kinji a yanda matsalar take, ni kuma sam bazan zauna a cutar da ‘yar uwata ko a k’untata mata ba, bazanso tai auren da zatazo tana shan wahala ba koma azo anacewa da an sani da ba’ayi ba....”
Jinjina kai Mamy tai kana tace “Wannan gaskiya ne Sameer, abinda yafi dacewa tun kafin maganan nan ya isa gaban Abbanku ka sami shi Khalid d’in kuyi magana, yaje yabi umarnin iyayensa yayi masu biyayya daga shi har Nabilar suyi hak’uri da juna, ni zan sami Nabilah nai mata magana, ka fahimta....”
Shiru ya d’anyi kaman mai nazari kana yace “A’a Mamy baza ai haka ba, idandai suna son junansu inaga bamuda hurumin datse masu farin cikinsu, komai d’an gwaji ne a rayuwa, inaga mu baiwa Khalid dama ya gwada nasa k’ok’arin wajen shawo kan iyayensa da nuna masu kuskuren dake cikin k’ok’arin da suke wajen auren da sam babu soyayya cikinta tinda kinga a nan gidan Auren Zulfa’u da Hafiz aya ce, ta zama izna ga masu yunk’urin irin wannan had’in da akeyi ba tareda baiwa yara daman zab’an abokan zamansu na rayuwa ba.. Aure is a lifetime commitment Mamy, one has to be very careful wajen deciding....”
Mamy ta jinjina kai cikeda gamsuwa da bayanan d’an nata kana tace “Haka ne Ma’aruf, kayi gaskiya Ubangiji ya maka Albarka....”
Sameer ya amsada Ameen Mamy kafin ya mik’e yana fad’in “Barin shiga na duba Mamani....”
Mamy tace “Toh a fito lafiya....”
Nabilah dake mak’ale jikin k’ofar d’akin Mamy taji komai, tsanin mamakine ya cikata, Wato wannan Siyamar itace matar Ya Ma’aruf... Kam bala’in can.... Matar datazo har cikin gidan nan ta gama rashin daraja ashe gidan sirakanta ne....? Aiko wllhi bataci bulus ba bashi taci Dan Wllhi wannan rashin darajan da tayi cikin gidan nan tsaf saita kwashesu ta maida cikin aljihunta saidai ba sunanta Nabilah ba... Ta saki murmushi a hankali tana hasasho ramuwar gayyar da zataiwa Siyama matar Ya Ma’aruf... Ita a halin yanzu ma bata ta tata da Khalid kawai burinta ta k’untatawasu Siyama ta huce takaicinta... Da wannan tunanin ta koma cikin d’aki ta haye kan gado ta lumshe idanunta tamkar mai bacci jin Mamy ta nufo cikin d’akin....
Nabilah dai sai waige waige take duk a tsarge take jinta don bata saba tsayuwa da maza a waje ba kana tace “Kaga ni zan shige yanzu za’a fito masallaci sallan azahar, and banso mutane suyita kallona a nan suna wucewa....”
Ya d’an gimtse kana yace “teddy bear I’m serous, inaso family d’inki susan dani sabida bada wasa nazo ba.....” Yayi maganar babu alamun wasa a tattaredashi wanda saida ya haifarwa Nabilah da bugun zuciya.... Batasan mai zatace masa ba sai duban k’asa da tai..... Daidai lokacin Sameer ya fito daga gidan da niyyan tafiya masallaci....
Khalid yana hango Sameer ya saki murmushi don bai manta ba dama sun tab’a had’uwa a gidan saidai a wancan lokacin Sameer ya sanar masa cewa alak’asar da mutanen gidan sabo ne kawai sabida zaman unguwa guda, a halin yanzu baisan asalin alak’ar Sameer d’in da ahalin gidan ba....
K’arasowa Sameer d’in ma yai yana mamakin hango Khalid da k’anwarsa Nabilah a tare.....
“Aaa Dr ashe zan sameka a nan....” Khalid ya fad’i sanda ya shige Nabilah ya k’arasa ya baiwa Sameer hannu sukai masbaha....
Gaban Nabilah ya fad’i jin muryar Yayanta Ma’aruf suna gaisawa da Khalid.... Cikin sauri ta k’araso zata shige cikin gida, kai a k’asa taceda Sameer “Ina yini Yaya...”
Ya amsa mata a tak’aice bata kuma cewa komai ba ta shige cikin gida.....
Daga Sameer d’in har Khalid d’in kallo suka bita dashi har ta shige cikin sauri....
Sameer ya dubi Khalid yace “So you two know each other....?”
D’an shafa sumarsa yai kana tin kafin na had’uda kai a gidan nan nasan miss grumpy.....” Yai maganar yana murmushi....
Shiru Sameer ya d’anyi kana yace “Amma kasan alak’ar dake tsakanina da ita.....?”
Sai sannan Khalid ya d’ago yana dubansa with a serious face kana ya furta “Ban fahimceka ba....”
Dafasa Sameer yai yana murmushi kana yace mu k’arasa masallaci za’a shiga sallah.... Idan mun fito you’ve a lot to explain to me kasan bazan bari a yaudari k’anwata ba....” Ya k’arashe yana mai ci gaba da warware hannun rigarsa da yai folding wajen alwala
Khalid ya bisa da kallo yana mai nanata kalman k’anwata da Sameer yace har suka shige haraban masallacin
***
Yasmeen tai d’add’aya a parlorn tana ci gaba da aikin kuka wanda tin isowarta garin takeyi..... Mahaifiyarta kaw sai faman cika take tana huci, ita kad’ai takai mari takai bango tana mai jinjina rashin mutuncin da Khalid ya masu....
Cikin kuka Yesmeen taci gaba da fad’in “Momy Wllhi nayi imani Kano ya tafi wajen tsinanniyar can ya tafi tinda gashi Ammi tayi waya tana tambayar mun sauk’a lafiya... Momy nidai Wllhi bazan tab’a bari Khalid ya auri wata bani ba... Kigafah kalan wulak’ancin da yamin ya barni a train station yayi tafiyarsa.....” Ta k’arashe tana mai kuma jejjefa k’afafu tana kururuwa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*71*
Mamakine ya cika Khalid jin cewa Iyayen Nabilah sune Iayayen Sameer na asali, wannan shine ikon Allah, who would’ve thought mutanen da Siyama ta tsana zasu juya su zama dangin mijinta....? Yai k’asaitaccen murmushi a hankali yana mai jinjina kai Don ko babu komai sosai abin ya masa zak’i.... Yana ganin kiran Ammi na shigo masa yayi biris yak’i d’agawa don yasan k’arshen zancen, k’arshe ma saka wayar yai a flight mode sanin cewa bazasu daina kiran nasa ba... Yana can sashen Mamani suna firan Yaushe rabo yayinda Sameer ke zaune parlorn Mamy suna tattaunawa kan batun Khalid d’in da Nabilah.....
Mamy ta sauk’e ajiyan zuciya kana tace “Amma Ma’aruf kana ganin wannan al’amari mai d’orewa ne..? Banso azo ana samun sab’ani musamman da ya kasance d’anuwan matarka ne....”
Turowa kad’an yai daga cikin kujera kana yace “Mamy munyi magana sosai da Khalid kuma ya tabbatar min cewa da aure yake son Nabilah, sannan na yarda da halayya da d’abi’un Khalid Mamy... Yana dai da hali irin nasa na rashinji wasu lokutan but I assure you he’s a good person... Bawai don ya kasance dan uwa ga Siyama ba no, na sanshi tun yaranta yaron kirki ne Mamy... Amma saidai wani hanzari ba gudu ba...”
Mamy ta d’ago tana dubansa kana tace “Umhum ina saurarenka....”
Sameer ya d’an fuzar da iska kana yace “Mamy iyayen Khalid suna yunk’urin had’a aurensa da wata ‘yar uwarsa ce wanda sam shi bai k’aunarta... Kinji a yanda matsalar take, ni kuma sam bazan zauna a cutar da ‘yar uwata ko a k’untata mata ba, bazanso tai auren da zatazo tana shan wahala ba koma azo anacewa da an sani da ba’ayi ba....”
Jinjina kai Mamy tai kana tace “Wannan gaskiya ne Sameer, abinda yafi dacewa tun kafin maganan nan ya isa gaban Abbanku ka sami shi Khalid d’in kuyi magana, yaje yabi umarnin iyayensa yayi masu biyayya daga shi har Nabilar suyi hak’uri da juna, ni zan sami Nabilah nai mata magana, ka fahimta....”
Shiru ya d’anyi kaman mai nazari kana yace “A’a Mamy baza ai haka ba, idandai suna son junansu inaga bamuda hurumin datse masu farin cikinsu, komai d’an gwaji ne a rayuwa, inaga mu baiwa Khalid dama ya gwada nasa k’ok’arin wajen shawo kan iyayensa da nuna masu kuskuren dake cikin k’ok’arin da suke wajen auren da sam babu soyayya cikinta tinda kinga a nan gidan Auren Zulfa’u da Hafiz aya ce, ta zama izna ga masu yunk’urin irin wannan had’in da akeyi ba tareda baiwa yara daman zab’an abokan zamansu na rayuwa ba.. Aure is a lifetime commitment Mamy, one has to be very careful wajen deciding....”
Mamy ta jinjina kai cikeda gamsuwa da bayanan d’an nata kana tace “Haka ne Ma’aruf, kayi gaskiya Ubangiji ya maka Albarka....”
Sameer ya amsada Ameen Mamy kafin ya mik’e yana fad’in “Barin shiga na duba Mamani....”
Mamy tace “Toh a fito lafiya....”
Nabilah dake mak’ale jikin k’ofar d’akin Mamy taji komai, tsanin mamakine ya cikata, Wato wannan Siyamar itace matar Ya Ma’aruf... Kam bala’in can.... Matar datazo har cikin gidan nan ta gama rashin daraja ashe gidan sirakanta ne....? Aiko wllhi bataci bulus ba bashi taci Dan Wllhi wannan rashin darajan da tayi cikin gidan nan tsaf saita kwashesu ta maida cikin aljihunta saidai ba sunanta Nabilah ba... Ta saki murmushi a hankali tana hasasho ramuwar gayyar da zataiwa Siyama matar Ya Ma’aruf... Ita a halin yanzu ma bata ta tata da Khalid kawai burinta ta k’untatawasu Siyama ta huce takaicinta... Da wannan tunanin ta koma cikin d’aki ta haye kan gado ta lumshe idanunta tamkar mai bacci jin Mamy ta nufo cikin d’akin....