Sashe 24
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai Sameer yayi yana dubanta kana yace “But Siyama k’afarki bata gama warkewa ba kin rufeta cikin takalmi, sannan duka duka fah jiya nazo kuma bazan wuce kwana biyu ba, yau zaki fice office ki barni... C’mon Siyama....”
D’an juya idanunta tai kana ta zauna jikinsa ta kamo hannayensa ta langab’e kai gefe tace “But Partner you know I’m a successful career woman, tun kafin ka aureni kasan da wannan, Sameer so kake na neglecting aikina, please mana... Ko ka mance kai kake supporting d’ina before....”
D’ago face d’inta ya d’anyi kana yace “Siyama ba cewa nake ki ajiye aikinki ba but at least tinda jiya na dawo ai na cancanci a bani kulawa na d’an kwana biyun nan da zanyi... Honey musamman fah sabidake na baro ayyukana na taso nazo, wannan shine tarban da za’a bani....?” Ya k’arashe yana mai kasheta da kallo...
Hannayensa ya kuma rik’owa cikin nata still tana zaune saman cinyarsa kana tace “Partner kasan idan banyi presentation d’in nan yau ba Daddy bazaiji dad’i ba dama yace yanzu Khalid ya fini k’wazo a aiki a company d’in please mana Partner... I don’t want to let Daddy down...” Ta k’arashe kaman zatai kuka...
Jinjina kai yayi kana yace “Fine, it’s alright... Kije, zanje na duba Mummy nima anjima... Take care of yourself ok....” Ya k’arashe yana sakar mata murmushi had’ida gyara mata mayafinta da ya zame ya rufe mata jikinta gaba d’aya...
Dubansa take tsananin k’aunarsa na d’awainiya da ita, lokaci guda ta rungumesa tana furta “I love you Partner...”
“I love you too...” Ya fad’i fuskarsa babu yabo babu fallasa....
Ko takan breakfast batabi ba ta fice cikin sauri tana amsa waya tana fad’in gata nan k’arasowa....
Kallo yabi bayanta dashi har ta fice kafin ya sauk’e ajiyan zuciya ya mik’e ya nufi dining table d’in shi kad’ai kad’aici na d’awainiya dashi, har sai yaji yayi missing Shamsu da Mama dashike idan bazai fice office da wuri ba tare suke karya kumallo gaba d’aya saman dining table.. A hankali ya saki murmushi abincin da bai iya ci ba ya mik’e ya haura upstairs ya shirya tsaf ya nufi nasu gidan....
A kitchen ya tadda Mummy tana directing ma’aikatanta abinda zasu dafa lunch don dama ita d’abi’arta kenan sam bata sakewa ma’aikata girkinta dole sai tana supervising nasu wasu abubuwan ma da kanta take don a wajenta Sameer ya soma koyon girki rabin yinin Mummy a kitchen ne shiyasa shima yasan abubuwa da dama gameda kitchen....
Innani ce ta soma hangosa zatai magana ya mata alamu da ido kan tayi shiru, Mummy naci gaba da fad’in “Ina Zilai tazo ta yanka veggies d’in nan banso a barsu haka nan....” Batakai aya ba saiji tai an rungumeta ta baya....
Ta saki murmushi don tasan mutum guda da zai mata haka, ba tareda ta juyo ba ta d’ago hannu ta d’an dunguri kanshi tana fad’in “Yaushe zaka girma ne wai Sameer, ko sai ka haifo min jikokin nawa ne sannan ka girma ka bar masu jikin nawa su ci gaba da tsalle akai....”
Murmushi kwance saman fuskarsa yace “A wajen Mummy na bazan tab’a girma ba ko yara nawa zan haifa, suje jikin nasu Mummy d’in suyi nima su barmin nawa....”
Murmushi tai cikeda jin dad’i kafin suka soma gaisawa, nan Sameer d’in suka gaisa da ma’aikatan kowa na fad’in yayi kewarsa musamman Innani data jima sosai a gidan tun Sameer d’in na yaro...
Nan kuma aka soma haba haba dashi ana tambayarshi mai za’a kawo masa..
Mummy tace “Innani kina mancewa ne wannan ai saidai ya shiga ya dafa da kansa koda yake k’ila yanzu ya daina tinda yayi aure yanada mai mishi...”
Murmushi kawai ya d’anyi baisan dalili ba amma sai yaji maganar Mummy ya masa wani iri, ko don Siyama bata mishi ne.... Duban Innani yayi kana yace a kawo mishi breakfast...
Mummy ta kalleshi da mamaki kana tace “Ba tun jiya kacemin kazo gari ba, ko yanzu ne sauk’ar naka...?”
Girgiza mata kai yayi kana yace “Tun jiya ne, daga gida nake Mummy....”
Bata kuma cewa komai ba sai d’an sanyi da jikinta yayi, anya wannan aure na Sameer na jin dad’inta kuwa, ace miji yazo gari takannas a kasa dafa masa karin kumallo sai yazo gida...? Ita kad’ai take tambayar kanta cikin zuciyarta, tasan hak’uri irin na Sameer shiyasa kwanaki da suka sami sab’ani da Siyama tabi bayan d’iyar k’awarta Siyama daga baya saida taji bata kyauta wa d’anta ba tinda ita ta tayar dashi ta kuma san sarai Sameer mutum ne mai tsananin hak’uri da kai zuciya nesa toh amma katsalanda a rayuwar ma’aurata ma duk baida wani amfani....
Da kanta ta shiga kitchen ta had’o masa delicious ta dawo parlor ta tayasa zama yana ci suna hira, yana mata hiran abokinsa Shamsu da shima ya tab’a zama gidansu, ya k’arada suna gaishesu gaba d’aya...
Yini zubur yayi a gidan har saida Daddy ya dawo suka gaisa suka b’ige da fira suma... Ba shi ya bar gidan sai bayan isha bayan Mummy ta gama cika mishi ciki da abinci...
A b’angaren Siyama kuwa tuntuni ta dawo donma saida ta biya gida ta d’auko pills d’inta da ta mance sannan ta biya eatery ta sai masu abinci Incase Sameer baiyi ba...
Koda ya dawo ta masa tayin abinci ce mata yayi yaci gidan Mummy, bata damu ba taci nata takai sauran kitchen...
Yau dai kafin ya nemeta tayi k’ok’ari takai kanta dashike tasha maganinta na hana d’aukan ciki...
***
Kwanan Sameer biyu ya tattara ya koma Kano ya bar Partner d’insa da kewarsa...
A b’angaren Khalid kuwa baida buri da ya wuce Daddy ya kuma aikensa Kano, shi ko Daddy bai aikesa ba ma shi zaijeshi da zaran aiki ya ragu mishi, Yesmin tana nan zatai kwana biyu a Kaduna kafin ta koma Abuja don tuni Mummynta ta koma ta barta da hud’uban kar ta kuskura ta dawo Abuja ba tareda ta saye zuciyar Khalid ba...
***
Aunty Lami da Hajiyar Hafiz zaune gaban Malam mai bugun k’asa ana masu duba idan Ma’aruf na raye...
Malam ya buga k’asa yayi wasu zane da yatsun hannunsa guda biyu kana ya d’ago ya dubesu..
Har suna had’e baki wajen cewa “Malam yaya shin yana raye ko ya mutu.....??”
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*23*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Malam ya d’ago ya dubesu ba tareda ya furta komai ba, Hajiya tai saurin furta “Malam yaya... Shin kaga Ma’aruf na numfashi a doron k’asa....?”
Kallonta Malam yayi ba tareda ya kuma furta koda kalma ba kana ya iza babbar rigarsa mai tsananin daud’a ya kuma zana layi guda da yatsarsa...
Aunty Lami sai faman yakushin Hajiya take tana k’yafta mata idanu tana fad’in “Ke Haule mu dakata muji ta bakin Malam....”
Gyaran murya Malam yayi kana yace “Abu ne a duhu....”
Suka kalli juna cikeda k’osawa...
Lami ta gyara zama sosai kana tace “Allah gafarta Malam bamu gane ba, kaman yaya abune a duhu...?”
Malam ya kuma sab’a babban garensa kana yace “Kasa bai nuna min komai ba, ban hago tak’aimemen abinda ke wakana ba, zan baku hak’uri ku dawo wani lokaci....”
Cikeda jin haushi Hajiya tace “Yo mai kake nufi kenan Malam, so kake kace muna biyanka a iska, kaga idan bazaka iya duba mana bane sai ka fad’i mana mu tafi wani wajen bawai kace mana bakaga komai ba....”
Duk yanda Aunty Lami ke muskutin Hajiya ta kasa rufe baki sai faman b’araka take...
Malam ya jinjina kai kana yace “Kuna iya zuwa wani wajen a duba maku amma ina mai tabbatar maku K’asa bazata min k’arya ba, duk yanda kukaje iyakacin abinda za’a gaya maku kenan, K’asa da Taurari bazasu min k’arya ba.. Amma tinda kun zab’i zuwa wani wajen sai anjimanku Allah bamu alkhairi...” Ya k’arashe yana k’ok’arin nad’e buzunsa...
Aunty Lami tai saurin katseshi da fad’in “A’a baza’ai haka ba Allah gafarta, yarda da aikinka yasa mukazo nan, tinda kace haka ai sai mu tafi mu dawo wani lokacin....”
Malam ya jinjina kai kana yace “Zan baku rana ku dawo rana itiyau kafin nan na k’irga taurari naga abinda zan iya gani....”
Suka jinjina kai a tare kafin suka mik’e suka masa sallama suka d’au hanyar gida...
Tinda suka fito Hajiya ke sababin cewa wannan bokan neman raina masu hankali yake dama sun nemi wani ne su k’yale tashan wannan gidahumin Malamin...
Aunty Lami tace “Um um Laure mubi a sannu, tinda yace mu dawo ran sati ai sai mu dawo ba wani abu bane....”
Hajiya ta jinjina kai kana tace “Yanzu abinda za’ai kisan yanda zakiyi kisha mana cikin mijinki muji alak’arsa da wannan saurayi da ya firgitaki kin fahimta idan yaso sai musan yanda zamu b’ullowa lamarin....”
Shiru Aunty Lami tai tamkar mai nazari kana tace “Kinfa sanshi kinsan mijina wane irin rikitaccen mutum ne, haka nan yake a tank’ware yawa arnen da, fuskarsa ma kurum bazai bari na iya tambayarsa ba...”
Hajiyar Hafiz ta buga tsaki kana tace “Ai kinji matsalarki shegen tsoron miji, ance ki kai sunansa gaban Malam kin kasa da yanzu kina zuba mulkinki son ranki, ni yanzu kinga duk taurin Alhaji saidai ya ganni ya barni don billahillazi sai nace ayi ayi idan kaw bance ba babu uban da ya isa yi...”
Aunty Lami ta murmusa kana tace “Haule kenan ni fah baso nayi mulki nake ba babban buri na shine na zama tauraruwa a cikin gidana ya kasance kowa ni yake kallo kowa ni yake so wanda da zallan makirci zan iyayin hakan babu taimakon boka balle Malam bawai na mallake mijina na maidashi mijin tace ba, a nan ra’ayinmu yasha banban gaskiya....”
Hajiya ta watsa mata kallo had’ida tab’e baki tace “Ai kinji, wake yayin auren haula bayan kanada masu share maka kuka,ke kikaga zaki iya... Nidai kinsan yanda zakiyi ki binciko mana wannan saurayi musan matakin d’auka akansa.... Ita kuma Aminiyar sirri ba zuba mata idanu zamuyi ba, zuwan takannas zamu mata ta sanar damu abinda tayida Ma’aruf kar mu zama wawaye...”
Da wannan tattaunawa suka rabu, adaidaita guda daman suka d’ale, Hajiya Haule aka soma sauk’ewa kafin aka wuce da Lami....
***
D’an juya idanunta tai kana ta zauna jikinsa ta kamo hannayensa ta langab’e kai gefe tace “But Partner you know I’m a successful career woman, tun kafin ka aureni kasan da wannan, Sameer so kake na neglecting aikina, please mana... Ko ka mance kai kake supporting d’ina before....”
D’ago face d’inta ya d’anyi kana yace “Siyama ba cewa nake ki ajiye aikinki ba but at least tinda jiya na dawo ai na cancanci a bani kulawa na d’an kwana biyun nan da zanyi... Honey musamman fah sabidake na baro ayyukana na taso nazo, wannan shine tarban da za’a bani....?” Ya k’arashe yana mai kasheta da kallo...
Hannayensa ya kuma rik’owa cikin nata still tana zaune saman cinyarsa kana tace “Partner kasan idan banyi presentation d’in nan yau ba Daddy bazaiji dad’i ba dama yace yanzu Khalid ya fini k’wazo a aiki a company d’in please mana Partner... I don’t want to let Daddy down...” Ta k’arashe kaman zatai kuka...
Jinjina kai yayi kana yace “Fine, it’s alright... Kije, zanje na duba Mummy nima anjima... Take care of yourself ok....” Ya k’arashe yana sakar mata murmushi had’ida gyara mata mayafinta da ya zame ya rufe mata jikinta gaba d’aya...
Dubansa take tsananin k’aunarsa na d’awainiya da ita, lokaci guda ta rungumesa tana furta “I love you Partner...”
“I love you too...” Ya fad’i fuskarsa babu yabo babu fallasa....
Ko takan breakfast batabi ba ta fice cikin sauri tana amsa waya tana fad’in gata nan k’arasowa....
Kallo yabi bayanta dashi har ta fice kafin ya sauk’e ajiyan zuciya ya mik’e ya nufi dining table d’in shi kad’ai kad’aici na d’awainiya dashi, har sai yaji yayi missing Shamsu da Mama dashike idan bazai fice office da wuri ba tare suke karya kumallo gaba d’aya saman dining table.. A hankali ya saki murmushi abincin da bai iya ci ba ya mik’e ya haura upstairs ya shirya tsaf ya nufi nasu gidan....
A kitchen ya tadda Mummy tana directing ma’aikatanta abinda zasu dafa lunch don dama ita d’abi’arta kenan sam bata sakewa ma’aikata girkinta dole sai tana supervising nasu wasu abubuwan ma da kanta take don a wajenta Sameer ya soma koyon girki rabin yinin Mummy a kitchen ne shiyasa shima yasan abubuwa da dama gameda kitchen....
Innani ce ta soma hangosa zatai magana ya mata alamu da ido kan tayi shiru, Mummy naci gaba da fad’in “Ina Zilai tazo ta yanka veggies d’in nan banso a barsu haka nan....” Batakai aya ba saiji tai an rungumeta ta baya....
Ta saki murmushi don tasan mutum guda da zai mata haka, ba tareda ta juyo ba ta d’ago hannu ta d’an dunguri kanshi tana fad’in “Yaushe zaka girma ne wai Sameer, ko sai ka haifo min jikokin nawa ne sannan ka girma ka bar masu jikin nawa su ci gaba da tsalle akai....”
Murmushi kwance saman fuskarsa yace “A wajen Mummy na bazan tab’a girma ba ko yara nawa zan haifa, suje jikin nasu Mummy d’in suyi nima su barmin nawa....”
Murmushi tai cikeda jin dad’i kafin suka soma gaisawa, nan Sameer d’in suka gaisa da ma’aikatan kowa na fad’in yayi kewarsa musamman Innani data jima sosai a gidan tun Sameer d’in na yaro...
Nan kuma aka soma haba haba dashi ana tambayarshi mai za’a kawo masa..
Mummy tace “Innani kina mancewa ne wannan ai saidai ya shiga ya dafa da kansa koda yake k’ila yanzu ya daina tinda yayi aure yanada mai mishi...”
Murmushi kawai ya d’anyi baisan dalili ba amma sai yaji maganar Mummy ya masa wani iri, ko don Siyama bata mishi ne.... Duban Innani yayi kana yace a kawo mishi breakfast...
Mummy ta kalleshi da mamaki kana tace “Ba tun jiya kacemin kazo gari ba, ko yanzu ne sauk’ar naka...?”
Girgiza mata kai yayi kana yace “Tun jiya ne, daga gida nake Mummy....”
Bata kuma cewa komai ba sai d’an sanyi da jikinta yayi, anya wannan aure na Sameer na jin dad’inta kuwa, ace miji yazo gari takannas a kasa dafa masa karin kumallo sai yazo gida...? Ita kad’ai take tambayar kanta cikin zuciyarta, tasan hak’uri irin na Sameer shiyasa kwanaki da suka sami sab’ani da Siyama tabi bayan d’iyar k’awarta Siyama daga baya saida taji bata kyauta wa d’anta ba tinda ita ta tayar dashi ta kuma san sarai Sameer mutum ne mai tsananin hak’uri da kai zuciya nesa toh amma katsalanda a rayuwar ma’aurata ma duk baida wani amfani....
Da kanta ta shiga kitchen ta had’o masa delicious ta dawo parlor ta tayasa zama yana ci suna hira, yana mata hiran abokinsa Shamsu da shima ya tab’a zama gidansu, ya k’arada suna gaishesu gaba d’aya...
Yini zubur yayi a gidan har saida Daddy ya dawo suka gaisa suka b’ige da fira suma... Ba shi ya bar gidan sai bayan isha bayan Mummy ta gama cika mishi ciki da abinci...
A b’angaren Siyama kuwa tuntuni ta dawo donma saida ta biya gida ta d’auko pills d’inta da ta mance sannan ta biya eatery ta sai masu abinci Incase Sameer baiyi ba...
Koda ya dawo ta masa tayin abinci ce mata yayi yaci gidan Mummy, bata damu ba taci nata takai sauran kitchen...
Yau dai kafin ya nemeta tayi k’ok’ari takai kanta dashike tasha maganinta na hana d’aukan ciki...
***
Kwanan Sameer biyu ya tattara ya koma Kano ya bar Partner d’insa da kewarsa...
A b’angaren Khalid kuwa baida buri da ya wuce Daddy ya kuma aikensa Kano, shi ko Daddy bai aikesa ba ma shi zaijeshi da zaran aiki ya ragu mishi, Yesmin tana nan zatai kwana biyu a Kaduna kafin ta koma Abuja don tuni Mummynta ta koma ta barta da hud’uban kar ta kuskura ta dawo Abuja ba tareda ta saye zuciyar Khalid ba...
***
Aunty Lami da Hajiyar Hafiz zaune gaban Malam mai bugun k’asa ana masu duba idan Ma’aruf na raye...
Malam ya buga k’asa yayi wasu zane da yatsun hannunsa guda biyu kana ya d’ago ya dubesu..
Har suna had’e baki wajen cewa “Malam yaya shin yana raye ko ya mutu.....??”
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*23*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Malam ya d’ago ya dubesu ba tareda ya furta komai ba, Hajiya tai saurin furta “Malam yaya... Shin kaga Ma’aruf na numfashi a doron k’asa....?”
Kallonta Malam yayi ba tareda ya kuma furta koda kalma ba kana ya iza babbar rigarsa mai tsananin daud’a ya kuma zana layi guda da yatsarsa...
Aunty Lami sai faman yakushin Hajiya take tana k’yafta mata idanu tana fad’in “Ke Haule mu dakata muji ta bakin Malam....”
Gyaran murya Malam yayi kana yace “Abu ne a duhu....”
Suka kalli juna cikeda k’osawa...
Lami ta gyara zama sosai kana tace “Allah gafarta Malam bamu gane ba, kaman yaya abune a duhu...?”
Malam ya kuma sab’a babban garensa kana yace “Kasa bai nuna min komai ba, ban hago tak’aimemen abinda ke wakana ba, zan baku hak’uri ku dawo wani lokaci....”
Cikeda jin haushi Hajiya tace “Yo mai kake nufi kenan Malam, so kake kace muna biyanka a iska, kaga idan bazaka iya duba mana bane sai ka fad’i mana mu tafi wani wajen bawai kace mana bakaga komai ba....”
Duk yanda Aunty Lami ke muskutin Hajiya ta kasa rufe baki sai faman b’araka take...
Malam ya jinjina kai kana yace “Kuna iya zuwa wani wajen a duba maku amma ina mai tabbatar maku K’asa bazata min k’arya ba, duk yanda kukaje iyakacin abinda za’a gaya maku kenan, K’asa da Taurari bazasu min k’arya ba.. Amma tinda kun zab’i zuwa wani wajen sai anjimanku Allah bamu alkhairi...” Ya k’arashe yana k’ok’arin nad’e buzunsa...
Aunty Lami tai saurin katseshi da fad’in “A’a baza’ai haka ba Allah gafarta, yarda da aikinka yasa mukazo nan, tinda kace haka ai sai mu tafi mu dawo wani lokacin....”
Malam ya jinjina kai kana yace “Zan baku rana ku dawo rana itiyau kafin nan na k’irga taurari naga abinda zan iya gani....”
Suka jinjina kai a tare kafin suka mik’e suka masa sallama suka d’au hanyar gida...
Tinda suka fito Hajiya ke sababin cewa wannan bokan neman raina masu hankali yake dama sun nemi wani ne su k’yale tashan wannan gidahumin Malamin...
Aunty Lami tace “Um um Laure mubi a sannu, tinda yace mu dawo ran sati ai sai mu dawo ba wani abu bane....”
Hajiya ta jinjina kai kana tace “Yanzu abinda za’ai kisan yanda zakiyi kisha mana cikin mijinki muji alak’arsa da wannan saurayi da ya firgitaki kin fahimta idan yaso sai musan yanda zamu b’ullowa lamarin....”
Shiru Aunty Lami tai tamkar mai nazari kana tace “Kinfa sanshi kinsan mijina wane irin rikitaccen mutum ne, haka nan yake a tank’ware yawa arnen da, fuskarsa ma kurum bazai bari na iya tambayarsa ba...”
Hajiyar Hafiz ta buga tsaki kana tace “Ai kinji matsalarki shegen tsoron miji, ance ki kai sunansa gaban Malam kin kasa da yanzu kina zuba mulkinki son ranki, ni yanzu kinga duk taurin Alhaji saidai ya ganni ya barni don billahillazi sai nace ayi ayi idan kaw bance ba babu uban da ya isa yi...”
Aunty Lami ta murmusa kana tace “Haule kenan ni fah baso nayi mulki nake ba babban buri na shine na zama tauraruwa a cikin gidana ya kasance kowa ni yake kallo kowa ni yake so wanda da zallan makirci zan iyayin hakan babu taimakon boka balle Malam bawai na mallake mijina na maidashi mijin tace ba, a nan ra’ayinmu yasha banban gaskiya....”
Hajiya ta watsa mata kallo had’ida tab’e baki tace “Ai kinji, wake yayin auren haula bayan kanada masu share maka kuka,ke kikaga zaki iya... Nidai kinsan yanda zakiyi ki binciko mana wannan saurayi musan matakin d’auka akansa.... Ita kuma Aminiyar sirri ba zuba mata idanu zamuyi ba, zuwan takannas zamu mata ta sanar damu abinda tayida Ma’aruf kar mu zama wawaye...”
Da wannan tattaunawa suka rabu, adaidaita guda daman suka d’ale, Hajiya Haule aka soma sauk’ewa kafin aka wuce da Lami....
***