Sashe 53
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Toh sai mai idan kayi k’ararta ita ta haifa maka d’iyar da zata k’waceta haka kurum, shikenan yanzu tasa d’iyarka bata ganin darajarka, yanzu sam Raiha bazata d’aukeka matsayin mahaifi ba biyayya kuwa saidai tayiwa Manu tinda gidanshi ta koma da zama...” Ta k’arashe tana aika masa harara....
Sauk’e ajiyan zuciya Baba Alhaji yayi yana mai girgiza kai alamun a’a yake fad’in “A’a Haule banda maganar kotu idan an kwana biyu dai lokacin Mamani ta huce zanje na d’auko d’iyata...”
Tsuka Hajiya ta buga had’ida kad’e masa buje ta mik’e tana fad’in “Aikin banza aikin wofi, k’ato da kai ka bari k’aninka da mahaifiyarka suna maka k’ak’a gida, toh wllhi nidai bazan kashe kaina da aikin gidan nan ba, kuma sanin kanka ne ma’aikata basu jure zaman gidan nan don haka duk abinda kaji ka gani kai ka sayo da kud’inka ehe...” Ta wuce fuu kaman zata tashi sama....
Tana isa d’aki ta tadda Kausar tayi kashi jikinta sai tangaririya ake da ita tsakanin Sahariyya da Najah an rasa mai wanke mata kowa cewa take wllhi bazatayi ba...
K’atutun bak’in ciki ya tokari Hajiya don sam basusan d’awainiyar yarinyar ba tinda ubanta ya ajeta gidan sai Raihanah...
Hajiya tai k’wafa tace “Kunsan Allah bazan lamunta wannan sangarci naku ba, kuna gani dai ubanku ya kasa dawo da Raiha gidan nan kun barni a kitchen ina fama da hayak’i da sunan ina maku girki, toh d’awainiyar Kausar d’inma ni ce kukeso na d’auka ko kuwa...?”
Kafin takai aya Sahariyya dake mak’ale da earpiece a kunne tace “Wllhi Hajiya nidai bazan wanke kashin d’iyarda ban haifa ba, ai ubanta na raye maiyasa baza’a maidata gidan ubanta ba matar tasa taje can tai d’awainiyarta amma wllhi badai ni ba kinji na rantse bazanyi ba...”
Hajiya ta kafeta da idanu had’ida yin k’wafa, ta dawoda dubantaga Najah wanda a nan take tunanin samun sauk’i...
Tab’e baki Naja’atu ma tai tace “Wllhi nima banzayi ba saidai tayi tsutsa....” Tana ida fad’in haka ta fice abinta...
Sahariyya kuwa gyara kwanciyarta tai ta ci gaba da chatting d’inta...
A dole Hajiya ta d’auki Kausar ta nufi bayi da ita tayo mata wanka ta shiryata gashi Raiha ta sabarwa yarinyar da goyo haka Hajiya ta sab’ata ta nufi kitchen k’arasa dafa abinci don bazata iya barin yaranta su Sahariyya da yunwa ba.....
***
Washe gari suna breakfast suna shek’ewa da dariya, Yesmin tace “Ai na fad’a miki cousin after everything I planned for bazai kuma duban yanda take ba, ita kanta bazata kuma fatan sake ganinshi ba, na tabbata by now ta tsaneshi ta tsani saninshi da tayi shiyasa nace miki ni nasan hanya mafi sauk’i da zamubi...”
Siyama ta kuma darawa kana tace “Kai cousin ai bansan kin iya makirci har haka ba na tabbata Ammi taji batun nan har kyauta sai tai miki...” Dariya suka kumayi a tare had’ida tafe hannaye daidai lokacinda Sameer ya fito cikin shirin fita aiki...
Yesmin ta gaidashi ya amsa babu yabo babu fallasa...
Siyama ta bishi da kallo don tun daren jiya ta lura tamkar wani abin na damunsa saidai sam bai sanar da ita ga abindake damunshi ba itama bataja maganan ba don yanzu gaba d’aya ya canza mata kaman ba Partner d’inta da suke sharing komai a baya ba, tun bayan sab’anin da suka samu Sameer ya canza mata sosai...
Ganin zai fice ya d’an sanyata bud’e murya tace “Partner breakfast fah...?”
A d’an kaikaice ya dubeta kana yace “No zanci a office I’m late already....”
D’an jim tai kana tace “Alright a dawo lafiya....”
Kai kurum ya jinjina mata had’ida k’ak’aro murmushi ya sakar mata kana ya fice...
Tinda ya doshi lab d’in gabansa ke matuk’ar fad’uwa yana tunanin abinda zai gani...
Koda ma’aikacin lab d’in ya mik’a masa zungureriyar takardan da k’yar ya iya sa hannu ya amsa...
Ya juyata yafi sau uku kafin ya soma k’ok’arin bud’ewa yana tunanin wannan takardar ka iya canza rayuwarsa ta har abada...
Da basmala saman bakinsa ya bud’e takardan ya ciro paper d’in dake linke ciki ya shiga warwarewa....
A hankali Sameer ya soma bin takardan yana karantawa daki daki...
Jiri ne yaji na neman kadashi sanda yayi araba da cewa yana d’aukeda jinin wannan bawan Allah kashi casa’in da tara cikin d’ari ma’ana da gaske Abbah shine mahaifinsa na asali....
Wasu irin zafafan hawaye suka shiga gangarowa Sameer wanda baisan na murna bane ko akasin haka....
Lokaci guda ya silale saman benci dake gefe a wajen hawaye naci gaba da gangaro masa.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*43*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Jiki a matuk’ar sanyaye Sameer ya mik’e ya nufi d’akin da aka kwantar da Abbah, Mamy na gefe saman abin sallah da alama sallar walha take shiko Abbah bacci yake domin kaw idnunsa a rufe suke....
Rakub’ewa Sameer yayi jikin k’ofar yana kallonsu sabbin hawaye na gangaro masa, ganin Abbah na k’ok’arin motsawa alamun zai farka ya sanyashi saurin komawa da baya yana mai rintse idanunsa masu zuban ruwa, wad’annan bayin Allah sune iyayensa, su sukai sanadiyan zuwansa duniya, sai yanzu yake fahimtar dlilan da sukasa yake jinsu matuk’a cikin zuciyarsa, sai yanzu yake fahimtar abubuwa da dama da yaji gameda wad’annan bayin Allah, a hankali ya linke takardan ya jefa cikin aljihunsa, Yana fitowa ne ya kusa cin karo da wata matashiyar mace tana tafe tana kuka da alama d’akin da Abbah yake ta nufa...
Su duka biyu sukai tsaye suna duban juna sannan ko wannensu hawayene kwance saman kyakkyawar fuskokinsu, ko ba’ace maka ba kaga ‘yan uwan juna, kowa ya kasa baiwa d’an uwansa hanya sai kallon juna da suke su duka biyun, k’arasowar wata madaidaiciyar mace data d’an data ne ya sanya Sameer kaucewa yana k’ok’arin basu hanya, for the first time da Aunty B ta kuma yin tozali da fuskar nephew d’inta da ya b’ace shekaru talatin baya, k’irjinta yai wani irin yankewa ya fad’i, wannan fuskar Ma’aruf ce tsantsan take hangowa, har ya gifta ta gefensu ya wuce Aunty B bata daina binsa da kallo ba Zulfa’u kaw tuni ta shige cikin d’akin hankali tashe ta fad’a kan Mamy tana kuka...
Aunty B ta take mata baya jiki a sanyaye tana son tambayar Zulfa’u wanene mutumin data gansu tare...
Sosai Mamy ta rungume Zulfah tana hawaye itama a daidai lokacinda Abbah ya fito daga band’aki, tausayin d’iyarsa da matarsa ya rufesa...
Zulfah taci gaba da fad’in “Mamy ina Abbah na, Mamy ku yafeni dan Allah, wllhi banyi nufin tada hankulanku ba sai don k’ok’arin gujema faruwar hakan, Mamy dan Allah ku yafe mun..” Ta k’arashe cikin shesshek’ar kuka...
Daga bayanta take jiyo muryar Abbah yanda yake fad’in “Zulfa’u baki mana komai ba face biyayya idan akwai wanda zai rok’i gafararki toh kuwa babu shakka mune musamman ni mahaikinki, ni nayi sanadiyar jefa rayuwarki cikin k’unci, na tauye maki hakkinki da addinin musulunci ya baki, na tilasta maki kasancewa da mutumin da baki k’aunarsa mutumin da yaso salwantar da rayuwarki, ki yafeni Zulfa’u ku yafeni daga ke har mahaifiyarki....” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya irinta mai kuka...
Jiki a sanyaye Zulfa’u ta taso ta k’araso gaban mahaifinta ta duk’a k’asa, cikin hawaye take furta “Abbah ka daina neman gafarata domin kuwa ni baka min komai ba, aurena da Yaya Hafiz k’addarane hakan Allah ya hukunta sai ya faru a shafin rayuwata, Abbah na tabbata burinka ka sama min abokin rayuwa na k’warai ne shiyasa ka zab’ar min Ya Hafiz... Dan Allah Abbah ka daina bani hak’uri kaji Abbah nah...”
Abbah ya kifa kansa yana fidda hawaye masu tsananin ban tausayi...
Itama Mamyn hawaye ke ci gaba da kwararo mata, d’aya daga cikin ranakun da take mafarkin kasancewarsu a rayuwarta, yau ga mijinta ya gane kuskurensa a rayuwa, Allahu Akbar... Wannan shine INDA RAI DA RABO, Sam mai rai kada ya yanke tsammanin yankewar rahamar Ubangijinsa domin shi d’in mai canza al’amra ne a duk sanda yazo, Allahu kasa mu dace, Ameen thumma Ameen...
Hawayen da Aunty B ke mak’alewa ya shiga d’igo mata, sosai suka bata tausayi sanda Zulfa’u taci gaba da sanar da iyayenta irin taimakon da Aunty Bara’atu tai mata, tsawon lokacin nan da Hafiz ya saketa tana zaune hannun Aunty Bara’atu....
Hakan sosai ya faranta ran Abbah da Mamy sukaita jerowa Aunty B godiya tana nuna masu ai Zulfa’u d’iyartace don tai mata wannan ba komai bane hasalima ma kanta tayi....
Aunty Lami tai tsaye daga bakin k’ofa tana kallonsu, zuciyarta kaman zata fito ta fashe sabida tsananin takaici da k’unci, ala dole ta saita kanta ta shiga da sallama hannunta d’aukeda kwandon abinci....
A b’angaren Sameer kuwa kai tsaye office d’insu Shamsu ya wuce....
Daga yanda Shamsu ya gansa yasan babu lafiya, kamosa yai ya zaunar saman kujera mai kallon nasa yana tambayarsa ya akai.....
Sameer bai iya ce masa komai ba sai hawaye dake ci gaba da gangaro masa...
Shamsu ya d’an fuzar da iska kana ya mik’e ya dawo kusan Sameer d’in ya janyo wata kujerar ya zauna, dafa Sameer yai yana mai ci gaba da nazarinsa, murya a kwance yace “Sameer please talk to me.... Meke faruwa....?”
Har lokacin Sameer d’in bai iya ce masa komai ba sai zaro takardan gwajin DNA da yai ya damk’a hannun Shamsu hawaye masu d’umi suna ci gaba da gangaro masa...
Shamsu ya bisa da kallon mamaki kana ya shiga k’ok’arin warware takardan....
Tsananin Shock Shamsu ya tsinci kansa ciki, ya d’ago ya kuma duban Sameer wanda har lokacin kansa ke kife k’asa yana d’igan hawaye....
Da gaske dai wad’annan bayin Allah sune biological parents d’in Sameer, wannan shine ikon Allah, toh ya akai hakan ta kasance....? Ya akai tsawon shekarun nan basu sani ba, mai ya raba Sameer da iyayensa na asali..? Tambayoyin dake yawo a kwanyar Shamsu... Yana cikin tunanin ne ya jiyo muryar Sameer mai cikeda tsnanin rauni yana fad’in “Sune iyayena Shamsu, Alhaji Usman shine mahaifina.... Shamsu bansan mai nakeji ba a halin yanzu, shin jefar dani sukai ko kuwa kyautar dani sukai...?
Shin meye asalin labarina... Mecece gaskiyarta....? Shamsu I need to find out...” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya...
Shamsu ya dafasa cikeda tausayawa, saida ya sauk’e ajiyan zuciya kana yace “Toh yanzu ta ina zaka fara abokina... Shin ka sanar da Abbah cewa shine mahaifinka, kaine d’ansu da ya b’ace...?”
Sauk’e ajiyan zuciya Baba Alhaji yayi yana mai girgiza kai alamun a’a yake fad’in “A’a Haule banda maganar kotu idan an kwana biyu dai lokacin Mamani ta huce zanje na d’auko d’iyata...”
Tsuka Hajiya ta buga had’ida kad’e masa buje ta mik’e tana fad’in “Aikin banza aikin wofi, k’ato da kai ka bari k’aninka da mahaifiyarka suna maka k’ak’a gida, toh wllhi nidai bazan kashe kaina da aikin gidan nan ba, kuma sanin kanka ne ma’aikata basu jure zaman gidan nan don haka duk abinda kaji ka gani kai ka sayo da kud’inka ehe...” Ta wuce fuu kaman zata tashi sama....
Tana isa d’aki ta tadda Kausar tayi kashi jikinta sai tangaririya ake da ita tsakanin Sahariyya da Najah an rasa mai wanke mata kowa cewa take wllhi bazatayi ba...
K’atutun bak’in ciki ya tokari Hajiya don sam basusan d’awainiyar yarinyar ba tinda ubanta ya ajeta gidan sai Raihanah...
Hajiya tai k’wafa tace “Kunsan Allah bazan lamunta wannan sangarci naku ba, kuna gani dai ubanku ya kasa dawo da Raiha gidan nan kun barni a kitchen ina fama da hayak’i da sunan ina maku girki, toh d’awainiyar Kausar d’inma ni ce kukeso na d’auka ko kuwa...?”
Kafin takai aya Sahariyya dake mak’ale da earpiece a kunne tace “Wllhi Hajiya nidai bazan wanke kashin d’iyarda ban haifa ba, ai ubanta na raye maiyasa baza’a maidata gidan ubanta ba matar tasa taje can tai d’awainiyarta amma wllhi badai ni ba kinji na rantse bazanyi ba...”
Hajiya ta kafeta da idanu had’ida yin k’wafa, ta dawoda dubantaga Najah wanda a nan take tunanin samun sauk’i...
Tab’e baki Naja’atu ma tai tace “Wllhi nima banzayi ba saidai tayi tsutsa....” Tana ida fad’in haka ta fice abinta...
Sahariyya kuwa gyara kwanciyarta tai ta ci gaba da chatting d’inta...
A dole Hajiya ta d’auki Kausar ta nufi bayi da ita tayo mata wanka ta shiryata gashi Raiha ta sabarwa yarinyar da goyo haka Hajiya ta sab’ata ta nufi kitchen k’arasa dafa abinci don bazata iya barin yaranta su Sahariyya da yunwa ba.....
***
Washe gari suna breakfast suna shek’ewa da dariya, Yesmin tace “Ai na fad’a miki cousin after everything I planned for bazai kuma duban yanda take ba, ita kanta bazata kuma fatan sake ganinshi ba, na tabbata by now ta tsaneshi ta tsani saninshi da tayi shiyasa nace miki ni nasan hanya mafi sauk’i da zamubi...”
Siyama ta kuma darawa kana tace “Kai cousin ai bansan kin iya makirci har haka ba na tabbata Ammi taji batun nan har kyauta sai tai miki...” Dariya suka kumayi a tare had’ida tafe hannaye daidai lokacinda Sameer ya fito cikin shirin fita aiki...
Yesmin ta gaidashi ya amsa babu yabo babu fallasa...
Siyama ta bishi da kallo don tun daren jiya ta lura tamkar wani abin na damunsa saidai sam bai sanar da ita ga abindake damunshi ba itama bataja maganan ba don yanzu gaba d’aya ya canza mata kaman ba Partner d’inta da suke sharing komai a baya ba, tun bayan sab’anin da suka samu Sameer ya canza mata sosai...
Ganin zai fice ya d’an sanyata bud’e murya tace “Partner breakfast fah...?”
A d’an kaikaice ya dubeta kana yace “No zanci a office I’m late already....”
D’an jim tai kana tace “Alright a dawo lafiya....”
Kai kurum ya jinjina mata had’ida k’ak’aro murmushi ya sakar mata kana ya fice...
Tinda ya doshi lab d’in gabansa ke matuk’ar fad’uwa yana tunanin abinda zai gani...
Koda ma’aikacin lab d’in ya mik’a masa zungureriyar takardan da k’yar ya iya sa hannu ya amsa...
Ya juyata yafi sau uku kafin ya soma k’ok’arin bud’ewa yana tunanin wannan takardar ka iya canza rayuwarsa ta har abada...
Da basmala saman bakinsa ya bud’e takardan ya ciro paper d’in dake linke ciki ya shiga warwarewa....
A hankali Sameer ya soma bin takardan yana karantawa daki daki...
Jiri ne yaji na neman kadashi sanda yayi araba da cewa yana d’aukeda jinin wannan bawan Allah kashi casa’in da tara cikin d’ari ma’ana da gaske Abbah shine mahaifinsa na asali....
Wasu irin zafafan hawaye suka shiga gangarowa Sameer wanda baisan na murna bane ko akasin haka....
Lokaci guda ya silale saman benci dake gefe a wajen hawaye naci gaba da gangaro masa.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*43*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Jiki a matuk’ar sanyaye Sameer ya mik’e ya nufi d’akin da aka kwantar da Abbah, Mamy na gefe saman abin sallah da alama sallar walha take shiko Abbah bacci yake domin kaw idnunsa a rufe suke....
Rakub’ewa Sameer yayi jikin k’ofar yana kallonsu sabbin hawaye na gangaro masa, ganin Abbah na k’ok’arin motsawa alamun zai farka ya sanyashi saurin komawa da baya yana mai rintse idanunsa masu zuban ruwa, wad’annan bayin Allah sune iyayensa, su sukai sanadiyan zuwansa duniya, sai yanzu yake fahimtar dlilan da sukasa yake jinsu matuk’a cikin zuciyarsa, sai yanzu yake fahimtar abubuwa da dama da yaji gameda wad’annan bayin Allah, a hankali ya linke takardan ya jefa cikin aljihunsa, Yana fitowa ne ya kusa cin karo da wata matashiyar mace tana tafe tana kuka da alama d’akin da Abbah yake ta nufa...
Su duka biyu sukai tsaye suna duban juna sannan ko wannensu hawayene kwance saman kyakkyawar fuskokinsu, ko ba’ace maka ba kaga ‘yan uwan juna, kowa ya kasa baiwa d’an uwansa hanya sai kallon juna da suke su duka biyun, k’arasowar wata madaidaiciyar mace data d’an data ne ya sanya Sameer kaucewa yana k’ok’arin basu hanya, for the first time da Aunty B ta kuma yin tozali da fuskar nephew d’inta da ya b’ace shekaru talatin baya, k’irjinta yai wani irin yankewa ya fad’i, wannan fuskar Ma’aruf ce tsantsan take hangowa, har ya gifta ta gefensu ya wuce Aunty B bata daina binsa da kallo ba Zulfa’u kaw tuni ta shige cikin d’akin hankali tashe ta fad’a kan Mamy tana kuka...
Aunty B ta take mata baya jiki a sanyaye tana son tambayar Zulfa’u wanene mutumin data gansu tare...
Sosai Mamy ta rungume Zulfah tana hawaye itama a daidai lokacinda Abbah ya fito daga band’aki, tausayin d’iyarsa da matarsa ya rufesa...
Zulfah taci gaba da fad’in “Mamy ina Abbah na, Mamy ku yafeni dan Allah, wllhi banyi nufin tada hankulanku ba sai don k’ok’arin gujema faruwar hakan, Mamy dan Allah ku yafe mun..” Ta k’arashe cikin shesshek’ar kuka...
Daga bayanta take jiyo muryar Abbah yanda yake fad’in “Zulfa’u baki mana komai ba face biyayya idan akwai wanda zai rok’i gafararki toh kuwa babu shakka mune musamman ni mahaikinki, ni nayi sanadiyar jefa rayuwarki cikin k’unci, na tauye maki hakkinki da addinin musulunci ya baki, na tilasta maki kasancewa da mutumin da baki k’aunarsa mutumin da yaso salwantar da rayuwarki, ki yafeni Zulfa’u ku yafeni daga ke har mahaifiyarki....” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya irinta mai kuka...
Jiki a sanyaye Zulfa’u ta taso ta k’araso gaban mahaifinta ta duk’a k’asa, cikin hawaye take furta “Abbah ka daina neman gafarata domin kuwa ni baka min komai ba, aurena da Yaya Hafiz k’addarane hakan Allah ya hukunta sai ya faru a shafin rayuwata, Abbah na tabbata burinka ka sama min abokin rayuwa na k’warai ne shiyasa ka zab’ar min Ya Hafiz... Dan Allah Abbah ka daina bani hak’uri kaji Abbah nah...”
Abbah ya kifa kansa yana fidda hawaye masu tsananin ban tausayi...
Itama Mamyn hawaye ke ci gaba da kwararo mata, d’aya daga cikin ranakun da take mafarkin kasancewarsu a rayuwarta, yau ga mijinta ya gane kuskurensa a rayuwa, Allahu Akbar... Wannan shine INDA RAI DA RABO, Sam mai rai kada ya yanke tsammanin yankewar rahamar Ubangijinsa domin shi d’in mai canza al’amra ne a duk sanda yazo, Allahu kasa mu dace, Ameen thumma Ameen...
Hawayen da Aunty B ke mak’alewa ya shiga d’igo mata, sosai suka bata tausayi sanda Zulfa’u taci gaba da sanar da iyayenta irin taimakon da Aunty Bara’atu tai mata, tsawon lokacin nan da Hafiz ya saketa tana zaune hannun Aunty Bara’atu....
Hakan sosai ya faranta ran Abbah da Mamy sukaita jerowa Aunty B godiya tana nuna masu ai Zulfa’u d’iyartace don tai mata wannan ba komai bane hasalima ma kanta tayi....
Aunty Lami tai tsaye daga bakin k’ofa tana kallonsu, zuciyarta kaman zata fito ta fashe sabida tsananin takaici da k’unci, ala dole ta saita kanta ta shiga da sallama hannunta d’aukeda kwandon abinci....
A b’angaren Sameer kuwa kai tsaye office d’insu Shamsu ya wuce....
Daga yanda Shamsu ya gansa yasan babu lafiya, kamosa yai ya zaunar saman kujera mai kallon nasa yana tambayarsa ya akai.....
Sameer bai iya ce masa komai ba sai hawaye dake ci gaba da gangaro masa...
Shamsu ya d’an fuzar da iska kana ya mik’e ya dawo kusan Sameer d’in ya janyo wata kujerar ya zauna, dafa Sameer yai yana mai ci gaba da nazarinsa, murya a kwance yace “Sameer please talk to me.... Meke faruwa....?”
Har lokacin Sameer d’in bai iya ce masa komai ba sai zaro takardan gwajin DNA da yai ya damk’a hannun Shamsu hawaye masu d’umi suna ci gaba da gangaro masa...
Shamsu ya bisa da kallon mamaki kana ya shiga k’ok’arin warware takardan....
Tsananin Shock Shamsu ya tsinci kansa ciki, ya d’ago ya kuma duban Sameer wanda har lokacin kansa ke kife k’asa yana d’igan hawaye....
Da gaske dai wad’annan bayin Allah sune biological parents d’in Sameer, wannan shine ikon Allah, toh ya akai hakan ta kasance....? Ya akai tsawon shekarun nan basu sani ba, mai ya raba Sameer da iyayensa na asali..? Tambayoyin dake yawo a kwanyar Shamsu... Yana cikin tunanin ne ya jiyo muryar Sameer mai cikeda tsnanin rauni yana fad’in “Sune iyayena Shamsu, Alhaji Usman shine mahaifina.... Shamsu bansan mai nakeji ba a halin yanzu, shin jefar dani sukai ko kuwa kyautar dani sukai...?
Shin meye asalin labarina... Mecece gaskiyarta....? Shamsu I need to find out...” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya...
Shamsu ya dafasa cikeda tausayawa, saida ya sauk’e ajiyan zuciya kana yace “Toh yanzu ta ina zaka fara abokina... Shin ka sanar da Abbah cewa shine mahaifinka, kaine d’ansu da ya b’ace...?”