Sashe 144
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A fusace Hafiz ya mik’e yana huci yake nuna Magaji da d’an yatsa “Zan maka kashedi na k’arshe daga yau kada ka sake cemin ga abinda zanyi tinda kai ba Ubana bane..!!!” Daga haka yasa kai ya shige fuuu tamkar zai kifa....
Jinjina kai Magaji yai cikeda mamaki had’ida tausayawa abokin nasa kana ya numfasa yace a fili “Eh lallai na yara kwanyarka ya tab’a Hafiz...” Magaji ya tina a da Hafiz ya sami Zulfa’u a b’agas dan dangin kyauta ya sameta yaita wulak’antata yana muzguna mata sai gashi yanzu da dik wani abinda ya mallaka bazai sameta ba, ta riga ta kufce masa, rayuwa kenan... D’an hakin da ka raina watarana shike tsole maka ido... Tabbas haka ne gashi ya faru kan abokinsa ya gani....
***
Har lokacin bai d’aga wayar ba saima k’ura ma wayar idanu da yai, shi harga Allah yanzu har tinanin d’aukan wayar Ammi yake, yasan maganar bazai wuce kan wannan mayyar yarinyar ba... Nabilah ta d’an dubesa taga yai k’urima waya, kaman ta tambayeshi ko lafiya sai kuma tai shiru had’ida maida idanunta kan yatsuna hannunta da taketa faman juya zoben dake yatsarta guda.... Tana a haka ta sinkayo muryarsa yana gaisuwa had’ida ambato Ammi.... Wani irin bugu k’irjinta yai tamkar an ije guduma, ta tuna karonsu da mahaifiyar Khalid gashi har yanzu basuyi wani tak’amaimen magana da Khalid d’inba balle taji ya matsayin aurensu wajen family d’insa.... Tana ganin yanda tin bayan gaisuwa ya k’urama waje guda idanu alamun daga d’aya b’angaren akwai abindake faruwa, dan shiru yai kurum yana saurarenta...
Ammi kaw taci gaba da bambamin masifa “Kan me zakai tafiya bazakai sallama da Yesmin ba, kuma tsaban wulak’anci da raini irin naka Khalid ka tafi har Abuja dik kwanakin nan ka kasa zuwa gidansu Yesmin ka gaida Aunt d’inka... Ya maka daidai, Allah ya baka sa’a kaci gaba da dik abinda kake....”
Khalid shaye da mamakin irin rainin dake tsakaninsa da Yesmin Wato ma k’ararsa takai wajen Ammi lallai yarinyar nan bata sansa ba har yanzu, amma ta nemi sanin ko shi wanene yanzu... Kasancewar ga Nabilah wajen kuma baiso ta fahimci akwai wata matsala ya sanyashi cewa “Ammi ban zauna bane, kiyi hak’uri zan kiraki back sai muyi maganar...”
A fusace tace “Khalid don’t you dare hang up on me, ban gama maka magana ba kana jina koh... Ba aiki ba idan uwar aiki ne ya tareka ka kirata ka bata hak’uri ku sasanta...”
Dunk’ule hannayensa kurum yake sabida tsananin tafasa da zuciyarsa keyi, wllhi sai ya cire rainin dake tsakaninsa da Yesmin hardai bata daina had’asa da mahaifiyarsa ba....
K’ok’arin saita kansa yai kana yace “Shikenan Ammi zanyi yanda kikace....”
Ammi tace “Yauwa yanzu dai naji batu... Allah shi maka Albarka.... Ga sets d’in akwatina da nai order sun iso, anjima Siyama zata d’auki pictures ta tura maka...” Bata jira amanarsa ba sukai sallama....
Shiru yai yana shafa wayarsa na d’an wani lokaci har saida Nabila ta d’an saci kallonsa, ko ba’ace ba kasan yanada damuwa dan duk k’ok’arinsa ya b’oye hakan zuciyarda ta damu dashi dole ta iya karanto hakan.... D’ago idanu tai tana k’ok’arin karatarsa Wannan karon idanunsu suka sark’e waje guda domin kaw shima d’in ita yake duba... Murmushi ya saki ganin tayi saurin maida idanunta k’asa, ya d’anyi gyaran murya kad’an yace “Wai ni teddy bear wannan sanne sannen da ake min na minene...? You know nafi sabo da masifarki, wannan sanne kai da shiru d’in duk ban saba dasu ba, ko sai mun tafi Kaduna ne a tsfeni ya k’arashe yana kwanto da fuskarsa dab nata.... Aiko kaman jira take ta jefa masa muguwar harara kana ta kuma kauda kai gefe...
Khalid ya murmusa kad’an yace “Yauwa better kinga da kika min wannan kallon yanzu na yarda teddy bear d’itace ba’a canza min ita ba...”
Wannan karon murmushi ta d’anyi ba tareda ta dubesa ba....
Shima murmushin saman fuskarsa yake dubanta kana yace “So Amarya ya taro...?”
A hankali ta amsa masada “Alhamdulillah..!” A tak’aice...
D’an gyara murya yai had’ida daidaita zamansa kana yace “Masha Allah...!” Gaba d’aya tattaro natsuwarsa ya kumayi kana yaci gaba da fad’in “Teddy bear... I know you’ve a lot of questions to ask, an saka bikinmu and you didn’t hear from me, banzo ba banyi waya ba, stuff like that... And you’ve every right to be mad at me... I’m sorry kinji koh... And I promise randa dik aka kaiki gidana I’ll explain everything to you kinji koh...”
Ita dai bata iya d’agowa ta dubesa ba har lokacin idanunta nakan zobenta da take juyawa... Idanun Khalid suka sauk’a kan abinda take, sosai lallen hannunta ya masa kyau special red one d’in da akai a fingers sosai suka masa kyau... Bata ankara ba saijin hannayensa tai saman nata... Tai saurin d’agowa tana dubansa shid’inma ita yake duba....
“kinji abinda nace...?” Ya tambaya yana tsareta da idanu ga k’irjinta dake matuk’ar bugu gashi yak’i sakin hannayenta saima murza yatsun da yake a hankali....A hankali ta jinjina masa kai alamun Eh dik wani iri take jinta, cikin dabara take k’ok’arin janye yatsun hannunta shiko Khalid yak’i saki saima dad’a d’an matsesu da yai ya nuna mata k’arfi kad’an... Ta d’ago idanunta masu cikeda tsoro wannan karon tana dubansa, Wato dai dik masifarta dai zai nuna mata k’arfinsu ba d’aya bane... Ya saki murmushi yana duban yanda dik ta wani daburce, kauda shirun yai da fad’in “K’unshin nan yayi kyau teddy bear... Yana gogewa a sake min wani dan inaso sosai...”
Harara ta d’an jefa masa wannan karon... “Ni ka sakemin hannu naje kafin a soma nemata....” Tai maganar tana turo baki....
Kallon d’an bakin nata da ya k’ware wajen iya tsiwa da masifa yake bai daina murza ‘yan yatsun hannun nata ba yake fad’in “Babu wanda zai nemeki sunsan da waye kike tare... Besides ko d’aukanki nai daga nan muka wuce babu mai tuhumata saidaima ace nayi daidai... Ko bazaki yarda ki bini bane...?” Ya k’arashe maganar sanda yake zame zoben da taketa wasa dashi a yatsarta...
Gajeran harara ta kuma galla masa kana tace “Tab, aiko kaini sukai yanzu bazan zauna ba dan sai na dawo na ida exams d’ina...”
Khalid ya murmusa yace “Meye a ciki kullum sai na kawoki kiyi ai... Saura nawa ne ki gama...?”
“Monday in sha Allah nake gamawa, saura last paper ne...!”
Khalid ya jinjina kai a hankali kana yace “Kinga zaman kano ya kamani.. Dan k’afarki k’afata bani barin garin nan without you teddy bear... So gwarama ki sakama ranki...” Ya k’arashe yana mai janyo wata k’aramar shopping bag dake gefen k’afarsa k’asa...
Ita dai kauda kanta gefe kurum tai, sinkayo muryarsa tai yana fad’in “Ni zan wuce, zan fara biyawa wajen Daddy first before na shige masauk’i tinda kink’i yarda ki bini.... Tashi muje Kimin rakiya...!”
Mik’ewa tai tana gyara mayafinta ta shiga bin bayansa a nitse... Saida suka kai k’ofa kana ya juyo yana dubanta yanda take takowa a natse da alama bata saba da d’aura zani ba, ya tako kusanta kad’an kana ya d’an rage murya yace “Being matar aure suites you teddy bear... Kinyi kyau sosai...” Nan ma bata amsa shi sai sakin murmushi da tai a hankali, Khalid ya kuma matsowa a hankali kana ya d’an rank’wafo saitin fuskarta, k’irjin Nabilah yaci gaba da bugawa jin d’umin numfashinsu kusan na juna, murya can k’asan mak’oshi yake furta “Anything for your Bear..?” Yanda yai maganar cikin salo na kashe murya saida ya kuma haifar mata da fad’uwan gaba ga numfashinsa dab saman fuskarta, saurin janye fuskarta tai a d’an daburce tace dashi “Saida safe...!”
Khalid ya girgiza kai yace “Ba wannan ba...”
Bugun zuciyarta ya k’aru ganin yana kuma matso da fuskarsa kusan nata, ji tai tamkar ta hankad’asa amma batada wannan k’arfin, can k’asar zuciyarta kurum take addu’an abinda zai karkata hankalinsa... Aiko kaman daga sama wayarsa ta soma ruri, ya gyara tsayuwarsa yana mai zaro wayar... Wannan karon dagaji da abokinsa Baffah suke maganan dan taji yana cewa su had’u GRA yanzu zai tafi wajen Daddy..... Daga nan paper bag d’in hannunsa ya mik’a mata, tai kicin kicin da fuska alamun bata son amsa saidai yanda taga ya matuk’ar tsarewa ya sanyata amsa tana mai masa godiya dikda batasan minene ciki ba...
“Inda na isa masauk’i zan kira, and monday kar kowa ya kaiki sch zanzo na kaiki da kaina kinji koh...”
Jinjina masa kai kurum tai tana satan kallon yanda ya mak’ala ring d’inta a ‘yar yatsan hannunsa k’arama dikda haka bai isa k’asa ba tasan neman maganane kawai ya sanyashi yin hakan, can k’asan zuciyarta murmushi take ita kanta tasan itada Khalid hali yazo d’aya they’re both very stubborns ita kaw yanzu ko musu bata iya masa balle tsiwar data saba yi masa... Sukai sallama Khalid ya tafi da kewar matarsa...
Ita kaw har ta shige gidan k’irjihta bai daina bugu ba, Yusrah dake jiranta parlor nan ta sakata gaba da zolaya Nabilar na aika mata harara, batabi takan Yusrah ba dan cike take da haushinta, ta isa ta bud’e paper bag d’in kwalin wayace d’an ubansu k’irar Samsung hardasu sim da komai, ta saki murmushi had’ida lumshe idanu tana shak’an k’amshinsa da ya kama ‘yar jakar... A haka Yusrah ta shigo ta taddata..
***
Jinjina kai Magaji yai cikeda mamaki had’ida tausayawa abokin nasa kana ya numfasa yace a fili “Eh lallai na yara kwanyarka ya tab’a Hafiz...” Magaji ya tina a da Hafiz ya sami Zulfa’u a b’agas dan dangin kyauta ya sameta yaita wulak’antata yana muzguna mata sai gashi yanzu da dik wani abinda ya mallaka bazai sameta ba, ta riga ta kufce masa, rayuwa kenan... D’an hakin da ka raina watarana shike tsole maka ido... Tabbas haka ne gashi ya faru kan abokinsa ya gani....
***
Har lokacin bai d’aga wayar ba saima k’ura ma wayar idanu da yai, shi harga Allah yanzu har tinanin d’aukan wayar Ammi yake, yasan maganar bazai wuce kan wannan mayyar yarinyar ba... Nabilah ta d’an dubesa taga yai k’urima waya, kaman ta tambayeshi ko lafiya sai kuma tai shiru had’ida maida idanunta kan yatsuna hannunta da taketa faman juya zoben dake yatsarta guda.... Tana a haka ta sinkayo muryarsa yana gaisuwa had’ida ambato Ammi.... Wani irin bugu k’irjinta yai tamkar an ije guduma, ta tuna karonsu da mahaifiyar Khalid gashi har yanzu basuyi wani tak’amaimen magana da Khalid d’inba balle taji ya matsayin aurensu wajen family d’insa.... Tana ganin yanda tin bayan gaisuwa ya k’urama waje guda idanu alamun daga d’aya b’angaren akwai abindake faruwa, dan shiru yai kurum yana saurarenta...
Ammi kaw taci gaba da bambamin masifa “Kan me zakai tafiya bazakai sallama da Yesmin ba, kuma tsaban wulak’anci da raini irin naka Khalid ka tafi har Abuja dik kwanakin nan ka kasa zuwa gidansu Yesmin ka gaida Aunt d’inka... Ya maka daidai, Allah ya baka sa’a kaci gaba da dik abinda kake....”
Khalid shaye da mamakin irin rainin dake tsakaninsa da Yesmin Wato ma k’ararsa takai wajen Ammi lallai yarinyar nan bata sansa ba har yanzu, amma ta nemi sanin ko shi wanene yanzu... Kasancewar ga Nabilah wajen kuma baiso ta fahimci akwai wata matsala ya sanyashi cewa “Ammi ban zauna bane, kiyi hak’uri zan kiraki back sai muyi maganar...”
A fusace tace “Khalid don’t you dare hang up on me, ban gama maka magana ba kana jina koh... Ba aiki ba idan uwar aiki ne ya tareka ka kirata ka bata hak’uri ku sasanta...”
Dunk’ule hannayensa kurum yake sabida tsananin tafasa da zuciyarsa keyi, wllhi sai ya cire rainin dake tsakaninsa da Yesmin hardai bata daina had’asa da mahaifiyarsa ba....
K’ok’arin saita kansa yai kana yace “Shikenan Ammi zanyi yanda kikace....”
Ammi tace “Yauwa yanzu dai naji batu... Allah shi maka Albarka.... Ga sets d’in akwatina da nai order sun iso, anjima Siyama zata d’auki pictures ta tura maka...” Bata jira amanarsa ba sukai sallama....
Shiru yai yana shafa wayarsa na d’an wani lokaci har saida Nabila ta d’an saci kallonsa, ko ba’ace ba kasan yanada damuwa dan duk k’ok’arinsa ya b’oye hakan zuciyarda ta damu dashi dole ta iya karanto hakan.... D’ago idanu tai tana k’ok’arin karatarsa Wannan karon idanunsu suka sark’e waje guda domin kaw shima d’in ita yake duba... Murmushi ya saki ganin tayi saurin maida idanunta k’asa, ya d’anyi gyaran murya kad’an yace “Wai ni teddy bear wannan sanne sannen da ake min na minene...? You know nafi sabo da masifarki, wannan sanne kai da shiru d’in duk ban saba dasu ba, ko sai mun tafi Kaduna ne a tsfeni ya k’arashe yana kwanto da fuskarsa dab nata.... Aiko kaman jira take ta jefa masa muguwar harara kana ta kuma kauda kai gefe...
Khalid ya murmusa kad’an yace “Yauwa better kinga da kika min wannan kallon yanzu na yarda teddy bear d’itace ba’a canza min ita ba...”
Wannan karon murmushi ta d’anyi ba tareda ta dubesa ba....
Shima murmushin saman fuskarsa yake dubanta kana yace “So Amarya ya taro...?”
A hankali ta amsa masada “Alhamdulillah..!” A tak’aice...
D’an gyara murya yai had’ida daidaita zamansa kana yace “Masha Allah...!” Gaba d’aya tattaro natsuwarsa ya kumayi kana yaci gaba da fad’in “Teddy bear... I know you’ve a lot of questions to ask, an saka bikinmu and you didn’t hear from me, banzo ba banyi waya ba, stuff like that... And you’ve every right to be mad at me... I’m sorry kinji koh... And I promise randa dik aka kaiki gidana I’ll explain everything to you kinji koh...”
Ita dai bata iya d’agowa ta dubesa ba har lokacin idanunta nakan zobenta da take juyawa... Idanun Khalid suka sauk’a kan abinda take, sosai lallen hannunta ya masa kyau special red one d’in da akai a fingers sosai suka masa kyau... Bata ankara ba saijin hannayensa tai saman nata... Tai saurin d’agowa tana dubansa shid’inma ita yake duba....
“kinji abinda nace...?” Ya tambaya yana tsareta da idanu ga k’irjinta dake matuk’ar bugu gashi yak’i sakin hannayenta saima murza yatsun da yake a hankali....A hankali ta jinjina masa kai alamun Eh dik wani iri take jinta, cikin dabara take k’ok’arin janye yatsun hannunta shiko Khalid yak’i saki saima dad’a d’an matsesu da yai ya nuna mata k’arfi kad’an... Ta d’ago idanunta masu cikeda tsoro wannan karon tana dubansa, Wato dai dik masifarta dai zai nuna mata k’arfinsu ba d’aya bane... Ya saki murmushi yana duban yanda dik ta wani daburce, kauda shirun yai da fad’in “K’unshin nan yayi kyau teddy bear... Yana gogewa a sake min wani dan inaso sosai...”
Harara ta d’an jefa masa wannan karon... “Ni ka sakemin hannu naje kafin a soma nemata....” Tai maganar tana turo baki....
Kallon d’an bakin nata da ya k’ware wajen iya tsiwa da masifa yake bai daina murza ‘yan yatsun hannun nata ba yake fad’in “Babu wanda zai nemeki sunsan da waye kike tare... Besides ko d’aukanki nai daga nan muka wuce babu mai tuhumata saidaima ace nayi daidai... Ko bazaki yarda ki bini bane...?” Ya k’arashe maganar sanda yake zame zoben da taketa wasa dashi a yatsarta...
Gajeran harara ta kuma galla masa kana tace “Tab, aiko kaini sukai yanzu bazan zauna ba dan sai na dawo na ida exams d’ina...”
Khalid ya murmusa yace “Meye a ciki kullum sai na kawoki kiyi ai... Saura nawa ne ki gama...?”
“Monday in sha Allah nake gamawa, saura last paper ne...!”
Khalid ya jinjina kai a hankali kana yace “Kinga zaman kano ya kamani.. Dan k’afarki k’afata bani barin garin nan without you teddy bear... So gwarama ki sakama ranki...” Ya k’arashe yana mai janyo wata k’aramar shopping bag dake gefen k’afarsa k’asa...
Ita dai kauda kanta gefe kurum tai, sinkayo muryarsa tai yana fad’in “Ni zan wuce, zan fara biyawa wajen Daddy first before na shige masauk’i tinda kink’i yarda ki bini.... Tashi muje Kimin rakiya...!”
Mik’ewa tai tana gyara mayafinta ta shiga bin bayansa a nitse... Saida suka kai k’ofa kana ya juyo yana dubanta yanda take takowa a natse da alama bata saba da d’aura zani ba, ya tako kusanta kad’an kana ya d’an rage murya yace “Being matar aure suites you teddy bear... Kinyi kyau sosai...” Nan ma bata amsa shi sai sakin murmushi da tai a hankali, Khalid ya kuma matsowa a hankali kana ya d’an rank’wafo saitin fuskarta, k’irjin Nabilah yaci gaba da bugawa jin d’umin numfashinsu kusan na juna, murya can k’asan mak’oshi yake furta “Anything for your Bear..?” Yanda yai maganar cikin salo na kashe murya saida ya kuma haifar mata da fad’uwan gaba ga numfashinsa dab saman fuskarta, saurin janye fuskarta tai a d’an daburce tace dashi “Saida safe...!”
Khalid ya girgiza kai yace “Ba wannan ba...”
Bugun zuciyarta ya k’aru ganin yana kuma matso da fuskarsa kusan nata, ji tai tamkar ta hankad’asa amma batada wannan k’arfin, can k’asar zuciyarta kurum take addu’an abinda zai karkata hankalinsa... Aiko kaman daga sama wayarsa ta soma ruri, ya gyara tsayuwarsa yana mai zaro wayar... Wannan karon dagaji da abokinsa Baffah suke maganan dan taji yana cewa su had’u GRA yanzu zai tafi wajen Daddy..... Daga nan paper bag d’in hannunsa ya mik’a mata, tai kicin kicin da fuska alamun bata son amsa saidai yanda taga ya matuk’ar tsarewa ya sanyata amsa tana mai masa godiya dikda batasan minene ciki ba...
“Inda na isa masauk’i zan kira, and monday kar kowa ya kaiki sch zanzo na kaiki da kaina kinji koh...”
Jinjina masa kai kurum tai tana satan kallon yanda ya mak’ala ring d’inta a ‘yar yatsan hannunsa k’arama dikda haka bai isa k’asa ba tasan neman maganane kawai ya sanyashi yin hakan, can k’asan zuciyarta murmushi take ita kanta tasan itada Khalid hali yazo d’aya they’re both very stubborns ita kaw yanzu ko musu bata iya masa balle tsiwar data saba yi masa... Sukai sallama Khalid ya tafi da kewar matarsa...
Ita kaw har ta shige gidan k’irjihta bai daina bugu ba, Yusrah dake jiranta parlor nan ta sakata gaba da zolaya Nabilar na aika mata harara, batabi takan Yusrah ba dan cike take da haushinta, ta isa ta bud’e paper bag d’in kwalin wayace d’an ubansu k’irar Samsung hardasu sim da komai, ta saki murmushi had’ida lumshe idanu tana shak’an k’amshinsa da ya kama ‘yar jakar... A haka Yusrah ta shigo ta taddata..
***