Sashe 66
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har bayan ficewarsu Akram Hafiz bai daina cewa Zulfa’u sabida maza ta soma aikin gidan radio ba, yana fincika daga hannun Aunty B yana fad’in idan k’arya yake ba sabida maza take aikin ba ta tashi ta musa...
Tsananin zafi da zuciyar Zulfa’u keyi batasan sanda ta mik’e tana huci take fad’in “Idan sabida maza nakeyi meye naka a ciki, meye ruwanka a ciki, shin ka mance ni yanzu ba matarka bace... Ka mance hakan Ya Hafiz...? Ka mance inada dama da zan tsaya da duk namijin danaga dama, ka mance inada dama da zan baiwa duk wani namiji mai son aurena k’ofa... Ka mance babu iddarka akaina..? Ka mance babu kome a sakinmu...? Idan har ka mance duka wad’annan, well let me remind you...” Kuka sosai ya kufce mata sanda taci gaba da fad’in cikin rawar murya “Badon kar nace babu sauran alak’a da ya had’amu ba tinda gudan jinin dake tsakaninmu Allah ya karb’i abinsa... Amma saidai kai d’in d’anuwana ne na jini duk yanda naje nazo... Kuma har abada bazan daina baka girmanka na Yaya a gareni ba... Ka tsaya a madakacinka don’t cross your limits...” Tana ida fad’in haka tasa hannu ta goge hawayen da suka jik’a mata fuska kana ta shige cikin gida....
Mamy ta take mata baya cikin sauri yayinda Aunty B ta saki murmushin jin dad’i ganin yanda Zulfa’unta ta takewa Hafiz burki, kallon yayi daidai ta raka Hafiz dashi kana ta shige ta barsa nan tsaye tamkar wanda ruwa ya shanye...
Jiki babu laka ya fice daga gidan abubuwan da Zulfa’u ta fad’i sunai masa yawo a kwanya....
***
Driving yake suna tattauna lamarin Hafiz shida Yusuf, Yusuf yace “A gaskiya da gani tasha wahalan zama da wannan mahaukacin.... Kai kaga yanda yayi jifa da ita kuwa...?”
Akram da zuciyarsa ke masa zogi ya fuzar da iska a karo na babu adadi kana yace “Badon ina tunanin she’s still grieving na rashin ‘yarta da tayi ba wllhi kaji na rantse da na koyawa mutumin nan hankali yanda nan gaba duk macen da ya kasance da ita zai girmamata ya darajata....”
Yusuf ya dara kana yace “Mutumina nasan halinka ai don naga irin duban da kake masa, toh ya kadai ganta hankalinka ya kwanta...”
Sai lokacin Akram ya saki murmushi a hankali sanda traffic light ya nuna masu koren wuta alamun an basu hannu kana yace “Kajika da wata magana... Kaga muje na ajeka na wuce I’m sure oga na can na jirana...”
Yusuf yai dariya yace “His excellency zakace.... Kodashike kaje ganin her excellency na birnin zuciyarka ne don haka bazaka amsa query ba...”
Nan ma murmushin kawai Akram ya kumayi kana ya d’auki hanyar unguwarsu domin sauk’e Yusuf...
***
MUTALLAB’S
Tsaye yake gaban full length mirror yana d’aura agogo a tsintsiyar hannunsa sanda ta turo k’ofan d’akin ta shigo fuska a turb’une....
Kallo take kan faman binsa dashi yanda yayi banza da ita tamkar baisan wata halitta na tsaye wajen ba, yayi kyau sosai cikin jampan nasa mai ruwan toka da ya bita da bak’ar hula zubin damanga.... Sai sassayanyar k’amshinsa dake dakan hancinta tinda ta shigo d’akin wanda babu wai tayi kewarsa sosai....
Ganin zai d’auki wayarsa dake gefen bedside ya sata yin sauri tasha gabansa tana rik’e da kunkumi tana watsa masa mugun kallo take fad’in “Ma’aruf let’s end this game now, wane irin rayuwa kakeyi... Ka sanar dani gaskiya azumi kakeyi kokuwa bin mata ka fara da yasa ka kasa nemata....?”
Idan hulan dake bisa kanshi ya amsa toh shakka babu shima zai amsa.... Duba d’aya ya mata ya d’auke kansa yana k’ok’arin rab’an gefenta d’iyarsa k’arama ta shigo tana fad’in “Daddy nima zan bika... Please don’t say no, kaga Uncle Akram yace gobe dani za’aje....” Ta k’arashe baki a ture....
Rage tsawonsa yayi ya kamo yarinyar ya zauna bakin gado had’ida d’aurata bisa cinyarsa guda kana yace “Yara basa zuwa Kiddy ki zauna a gida kinji koh...”
Mak’e kafad’anta guda tai kana tace “But I don’t want to Daddy, ni banson zama da Mummy bana sonta....”
Zuciyar Muhibba ta kuma yin zafi takaiwa yarinyar dake kwance jikin Babanta harara kana tace “Wannan wane irin wulak’anci ne ina maka magana kayi banza dani kana biyewa yarinya salon a koyawa yara k’in uwarsu tun suna yara...”
Baice mata komai ba sai d’aga Najma da yayi ya mata ‘yan dabaru ta hak’ura ta fice wajen ‘yan uwanta...
Dawowa d’akin yayi ya tadda Muhibba tsaye tana faman huci, dukda zafi da zuciyarsa ke masa hakan baisa yace mata komai ba sai d’aukan d’aya wayar salulansa da yayi ya nufo downstairs....
Cikin tsananin fushi da takaicin yayi banza da ita ta biyo bayanshi tana fad’in “Ni Wllhi sai ka fad’a min wacece shegiyar da kake cin amanata da ita... Wllhi sai ka fad’a min....” Ta k’arashe cikin muryar kuka....
Tsaye yayi yana dubanta don yanzu abubuwan Muhibba sam basa bashi mamaki,
“Ki d’auka a duk yanda ya miki, banida matsala da wannan, duk abinda shed’anin zuciyarki ya raya miki toh ki d’auka a haka, wannan ke ta shafa bani ba... Zan miki kashedi guda d’aya koda wasa kada ki kuskura ki sako yaranmu cikin wannan matsalan, this is between us do not involve them.... Na fad’a miki tun ba yau ba I can take care of them with or without you.... So kada ma ki fara dasawa yara cewa an koya masu tsanarki, ke da kanki kika zab’i hakan.... So na fad’a miki kada ki kuskura idan ba haka zakiga other side d’ina da har yau baki tab’a gani ba.....” Yana ida fad’in hakan yasa kai ya fice cikin sauri zuciyarsa na tsananin masa zafi....
Kallo tabisa dashi had’ida fashewa da wani irin kuka....
***
A can asibiti wajen Abbah kuwa da mamaki yake kuma duban Aunty Lami kana yace “Lami Kausar jikata kike nufi...?”
Aunty Lami ta jinjina kai tace “K’warai kuwa bansan dalilinsu na b’oye maka ba....” Ta k’arashe tana juya idanu...
Abbah ya rik’e bangaren k’irjinsa dake masa zafi sosai, ya sauk’o daga saman gado yana tambayarta ina takalmansa... Har lokacin hannunsa na dafe da k’irjinsa....
Aunty Lami fad’i take “A’ah Alhaji ina zakaje... Ina zakaje a haka... Ka tsaya likita yazo ya sallameka...”
Abbah fad’i yake “A’a Lami ahalina suna buk’atana dole naje na gansu bazan tsaya jiran likita ba....” Ya k’arashe maganan jiri na k’ok’arin aikasa k’asa...
Aunty Lami ta bud’e murya tace “Alhaji..!!”
A daidai lokacin da Sameer ya shigo ya furta “Abbah..!!” Da k’arfin gaske baisan sanda ya isa ya rik’esa ba....
Zaro idanu waje tai k’afafunta na tsananin rawa, yawun bakinta cak ya kafe lokaci guda ganin hasashenta na neman tabbata bata ida karaya ba saida ta sinkayo muryar Abbah na fad’iwa Sameer “Ma’aruf gida zanje...!”
K’iris ya rage Aunty Lami bata saki fitsari a jikinta ba, da za’a tsaga jikinta tabbas da zai wuya a sami jini sabida yanda ta daskare lokaci guda....
A hankali ta furta “Ma’aruuf ne..!!!”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*54*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Abbah fad’i yake “Ma’aruf meyasa kuka b’oyemin mutuwar jikata, kan wane dalili.... Na riga na warke maza ka kaini gida... Muje banson na sake yini a wajen nan balle kwana....”
Sameer ya rik’e shi sosai yana fad’in “Calm down Abbah please... Mu jura likita yazo ya duba idan za’a iya sallaman naka... Please Abbah...”
Girgiza masa kai Abbah yaci gaba dayi yana fad’in “A’a Ma’aruf na warke, ka d’aukeni kawai mubar wajen nan...”
Har wannan lokacin Aunty Lami bata dawo cikin hayyacinta ba, abubuwan da suka faru baya suke faman yawo a kanyarta... Ma’aruf ya dawo, yaron da suka salwantar da rayuwarsa da k’arfin gaske gashi Allah ya dawo dashi, tabbas dawowarsa barazana ne ga rayukansu.... Cikin mintoci k’ank’ani tai wad’annan tunanin....
“Lami kirawo likitan ya bani takardan shaidar sallamar, jeki kirashi ya sallameni...”
Sai sannan Aunty Lami ta dawo daga duniyar data tafi... Cikin rawar murya take furta “To...Na’am... To Toh Alhaji ....” Cikin sauri ta fice daga d’akin ba tareda ta dubi b’angaren da Sameer ke tsaye ba, tamkar wacce k’aya ke sokinta haka ta fice daga d’akin...
Sameer ya bita da kallo zuciyarsa na raya masa wani abin musamman da ya fahimci itace ta sanarwa Abbah mutuwar tilon jikarsa....
Sam Aunty Lami batasan yanda take jefa k’afafunta ba, ko kirawo likitan bata iya tayi ba, tsintar kanta tai a bakin kwalta ba tareda sanin ta fito waje ba tsananin rud’ani da tashin hankali had’ida zullumi da fargaba data tsinci kanta ciki....
A daidaita ta tare ta hau cikin sauri ko ciniki bata tsayayi ba tamkar wacce ake biyeda ita a guje haka ta shige adaidaitan....
Da k’yar ta iya lalumo kalamai saman harshenta taceda mai adaidaita ka yanda zaya kaita....
A bakin layin su Hajiya ta sauk’a sai faman zuba haki da gumi take sanda ta fad’a cikin gidan tagajan magajan tamkar wacce aka jehota....
Hajiya na zaune bakin murhu da shike ‘yan gaisuwa sun d’auke k’afa... Firgit ta mik’e had’ida dafe k’irji tana fad’in “Lami lafiya na ganki haka...? Meke faruwa Lami...?”
Naja’atu dake zaune daga can gefe tana wanke wanke kallon mamaki take bin Aunty Lami dashi ganin hawaye kwance saman fuskarta gashi gaba d’aya a birkice take tamkar wacce aka biyota a guje....
Lami naci gaba da waige waige ta kamo hannayen Hajiya cikin daburcewa take fad’in “Haule shikenan... Shikenan mukam Haule tamu tazo k’arshe....”
Hajiya ta waiga taga babu mai kallonsu don ko kulada Najah dake wajen wanke wanke ma batai ba, tai saurin janyo hannun Lami suka shige madafi cikin sauri.....
Naja’atu tai saurin d’auraye hannayenta ta take masu baya had’ida lab’ewa jikin k’ofar kitchen d’in....
Hajiya Haule na muzurai take tambayar Aunty Lami...
“Lami wai meke faruwane ya na ganki haka....?”
Aunty Lami na goge gumin da ya wanke mata fuska take fad’in “Ma’aruf ya dawo Haule... Shikenan kashinmu ta bushe... Haule idan muddin asirinmu ya tonu Alhaji Usman Mailafiya tsireni zaiyi shikenan na rabu da masoyina Haule... Wayyo Allah na wllhi ban tab’a danasani irinta yau ba Haule...” Ta k’arashe murya cikeda tsananin tsoro...
Hajiya ta zaro idanu waje had’ida dafe k’irji tace “Lami kina nufin kicemin hasashenmu ya tabbata wannan likitan shine Ma’aruf...?”
Tsananin zafi da zuciyar Zulfa’u keyi batasan sanda ta mik’e tana huci take fad’in “Idan sabida maza nakeyi meye naka a ciki, meye ruwanka a ciki, shin ka mance ni yanzu ba matarka bace... Ka mance hakan Ya Hafiz...? Ka mance inada dama da zan tsaya da duk namijin danaga dama, ka mance inada dama da zan baiwa duk wani namiji mai son aurena k’ofa... Ka mance babu iddarka akaina..? Ka mance babu kome a sakinmu...? Idan har ka mance duka wad’annan, well let me remind you...” Kuka sosai ya kufce mata sanda taci gaba da fad’in cikin rawar murya “Badon kar nace babu sauran alak’a da ya had’amu ba tinda gudan jinin dake tsakaninmu Allah ya karb’i abinsa... Amma saidai kai d’in d’anuwana ne na jini duk yanda naje nazo... Kuma har abada bazan daina baka girmanka na Yaya a gareni ba... Ka tsaya a madakacinka don’t cross your limits...” Tana ida fad’in haka tasa hannu ta goge hawayen da suka jik’a mata fuska kana ta shige cikin gida....
Mamy ta take mata baya cikin sauri yayinda Aunty B ta saki murmushin jin dad’i ganin yanda Zulfa’unta ta takewa Hafiz burki, kallon yayi daidai ta raka Hafiz dashi kana ta shige ta barsa nan tsaye tamkar wanda ruwa ya shanye...
Jiki babu laka ya fice daga gidan abubuwan da Zulfa’u ta fad’i sunai masa yawo a kwanya....
***
Driving yake suna tattauna lamarin Hafiz shida Yusuf, Yusuf yace “A gaskiya da gani tasha wahalan zama da wannan mahaukacin.... Kai kaga yanda yayi jifa da ita kuwa...?”
Akram da zuciyarsa ke masa zogi ya fuzar da iska a karo na babu adadi kana yace “Badon ina tunanin she’s still grieving na rashin ‘yarta da tayi ba wllhi kaji na rantse da na koyawa mutumin nan hankali yanda nan gaba duk macen da ya kasance da ita zai girmamata ya darajata....”
Yusuf ya dara kana yace “Mutumina nasan halinka ai don naga irin duban da kake masa, toh ya kadai ganta hankalinka ya kwanta...”
Sai lokacin Akram ya saki murmushi a hankali sanda traffic light ya nuna masu koren wuta alamun an basu hannu kana yace “Kajika da wata magana... Kaga muje na ajeka na wuce I’m sure oga na can na jirana...”
Yusuf yai dariya yace “His excellency zakace.... Kodashike kaje ganin her excellency na birnin zuciyarka ne don haka bazaka amsa query ba...”
Nan ma murmushin kawai Akram ya kumayi kana ya d’auki hanyar unguwarsu domin sauk’e Yusuf...
***
MUTALLAB’S
Tsaye yake gaban full length mirror yana d’aura agogo a tsintsiyar hannunsa sanda ta turo k’ofan d’akin ta shigo fuska a turb’une....
Kallo take kan faman binsa dashi yanda yayi banza da ita tamkar baisan wata halitta na tsaye wajen ba, yayi kyau sosai cikin jampan nasa mai ruwan toka da ya bita da bak’ar hula zubin damanga.... Sai sassayanyar k’amshinsa dake dakan hancinta tinda ta shigo d’akin wanda babu wai tayi kewarsa sosai....
Ganin zai d’auki wayarsa dake gefen bedside ya sata yin sauri tasha gabansa tana rik’e da kunkumi tana watsa masa mugun kallo take fad’in “Ma’aruf let’s end this game now, wane irin rayuwa kakeyi... Ka sanar dani gaskiya azumi kakeyi kokuwa bin mata ka fara da yasa ka kasa nemata....?”
Idan hulan dake bisa kanshi ya amsa toh shakka babu shima zai amsa.... Duba d’aya ya mata ya d’auke kansa yana k’ok’arin rab’an gefenta d’iyarsa k’arama ta shigo tana fad’in “Daddy nima zan bika... Please don’t say no, kaga Uncle Akram yace gobe dani za’aje....” Ta k’arashe baki a ture....
Rage tsawonsa yayi ya kamo yarinyar ya zauna bakin gado had’ida d’aurata bisa cinyarsa guda kana yace “Yara basa zuwa Kiddy ki zauna a gida kinji koh...”
Mak’e kafad’anta guda tai kana tace “But I don’t want to Daddy, ni banson zama da Mummy bana sonta....”
Zuciyar Muhibba ta kuma yin zafi takaiwa yarinyar dake kwance jikin Babanta harara kana tace “Wannan wane irin wulak’anci ne ina maka magana kayi banza dani kana biyewa yarinya salon a koyawa yara k’in uwarsu tun suna yara...”
Baice mata komai ba sai d’aga Najma da yayi ya mata ‘yan dabaru ta hak’ura ta fice wajen ‘yan uwanta...
Dawowa d’akin yayi ya tadda Muhibba tsaye tana faman huci, dukda zafi da zuciyarsa ke masa hakan baisa yace mata komai ba sai d’aukan d’aya wayar salulansa da yayi ya nufo downstairs....
Cikin tsananin fushi da takaicin yayi banza da ita ta biyo bayanshi tana fad’in “Ni Wllhi sai ka fad’a min wacece shegiyar da kake cin amanata da ita... Wllhi sai ka fad’a min....” Ta k’arashe cikin muryar kuka....
Tsaye yayi yana dubanta don yanzu abubuwan Muhibba sam basa bashi mamaki,
“Ki d’auka a duk yanda ya miki, banida matsala da wannan, duk abinda shed’anin zuciyarki ya raya miki toh ki d’auka a haka, wannan ke ta shafa bani ba... Zan miki kashedi guda d’aya koda wasa kada ki kuskura ki sako yaranmu cikin wannan matsalan, this is between us do not involve them.... Na fad’a miki tun ba yau ba I can take care of them with or without you.... So kada ma ki fara dasawa yara cewa an koya masu tsanarki, ke da kanki kika zab’i hakan.... So na fad’a miki kada ki kuskura idan ba haka zakiga other side d’ina da har yau baki tab’a gani ba.....” Yana ida fad’in hakan yasa kai ya fice cikin sauri zuciyarsa na tsananin masa zafi....
Kallo tabisa dashi had’ida fashewa da wani irin kuka....
***
A can asibiti wajen Abbah kuwa da mamaki yake kuma duban Aunty Lami kana yace “Lami Kausar jikata kike nufi...?”
Aunty Lami ta jinjina kai tace “K’warai kuwa bansan dalilinsu na b’oye maka ba....” Ta k’arashe tana juya idanu...
Abbah ya rik’e bangaren k’irjinsa dake masa zafi sosai, ya sauk’o daga saman gado yana tambayarta ina takalmansa... Har lokacin hannunsa na dafe da k’irjinsa....
Aunty Lami fad’i take “A’ah Alhaji ina zakaje... Ina zakaje a haka... Ka tsaya likita yazo ya sallameka...”
Abbah fad’i yake “A’a Lami ahalina suna buk’atana dole naje na gansu bazan tsaya jiran likita ba....” Ya k’arashe maganan jiri na k’ok’arin aikasa k’asa...
Aunty Lami ta bud’e murya tace “Alhaji..!!”
A daidai lokacin da Sameer ya shigo ya furta “Abbah..!!” Da k’arfin gaske baisan sanda ya isa ya rik’esa ba....
Zaro idanu waje tai k’afafunta na tsananin rawa, yawun bakinta cak ya kafe lokaci guda ganin hasashenta na neman tabbata bata ida karaya ba saida ta sinkayo muryar Abbah na fad’iwa Sameer “Ma’aruf gida zanje...!”
K’iris ya rage Aunty Lami bata saki fitsari a jikinta ba, da za’a tsaga jikinta tabbas da zai wuya a sami jini sabida yanda ta daskare lokaci guda....
A hankali ta furta “Ma’aruuf ne..!!!”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*54*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Abbah fad’i yake “Ma’aruf meyasa kuka b’oyemin mutuwar jikata, kan wane dalili.... Na riga na warke maza ka kaini gida... Muje banson na sake yini a wajen nan balle kwana....”
Sameer ya rik’e shi sosai yana fad’in “Calm down Abbah please... Mu jura likita yazo ya duba idan za’a iya sallaman naka... Please Abbah...”
Girgiza masa kai Abbah yaci gaba dayi yana fad’in “A’a Ma’aruf na warke, ka d’aukeni kawai mubar wajen nan...”
Har wannan lokacin Aunty Lami bata dawo cikin hayyacinta ba, abubuwan da suka faru baya suke faman yawo a kanyarta... Ma’aruf ya dawo, yaron da suka salwantar da rayuwarsa da k’arfin gaske gashi Allah ya dawo dashi, tabbas dawowarsa barazana ne ga rayukansu.... Cikin mintoci k’ank’ani tai wad’annan tunanin....
“Lami kirawo likitan ya bani takardan shaidar sallamar, jeki kirashi ya sallameni...”
Sai sannan Aunty Lami ta dawo daga duniyar data tafi... Cikin rawar murya take furta “To...Na’am... To Toh Alhaji ....” Cikin sauri ta fice daga d’akin ba tareda ta dubi b’angaren da Sameer ke tsaye ba, tamkar wacce k’aya ke sokinta haka ta fice daga d’akin...
Sameer ya bita da kallo zuciyarsa na raya masa wani abin musamman da ya fahimci itace ta sanarwa Abbah mutuwar tilon jikarsa....
Sam Aunty Lami batasan yanda take jefa k’afafunta ba, ko kirawo likitan bata iya tayi ba, tsintar kanta tai a bakin kwalta ba tareda sanin ta fito waje ba tsananin rud’ani da tashin hankali had’ida zullumi da fargaba data tsinci kanta ciki....
A daidaita ta tare ta hau cikin sauri ko ciniki bata tsayayi ba tamkar wacce ake biyeda ita a guje haka ta shige adaidaitan....
Da k’yar ta iya lalumo kalamai saman harshenta taceda mai adaidaita ka yanda zaya kaita....
A bakin layin su Hajiya ta sauk’a sai faman zuba haki da gumi take sanda ta fad’a cikin gidan tagajan magajan tamkar wacce aka jehota....
Hajiya na zaune bakin murhu da shike ‘yan gaisuwa sun d’auke k’afa... Firgit ta mik’e had’ida dafe k’irji tana fad’in “Lami lafiya na ganki haka...? Meke faruwa Lami...?”
Naja’atu dake zaune daga can gefe tana wanke wanke kallon mamaki take bin Aunty Lami dashi ganin hawaye kwance saman fuskarta gashi gaba d’aya a birkice take tamkar wacce aka biyota a guje....
Lami naci gaba da waige waige ta kamo hannayen Hajiya cikin daburcewa take fad’in “Haule shikenan... Shikenan mukam Haule tamu tazo k’arshe....”
Hajiya ta waiga taga babu mai kallonsu don ko kulada Najah dake wajen wanke wanke ma batai ba, tai saurin janyo hannun Lami suka shige madafi cikin sauri.....
Naja’atu tai saurin d’auraye hannayenta ta take masu baya had’ida lab’ewa jikin k’ofar kitchen d’in....
Hajiya Haule na muzurai take tambayar Aunty Lami...
“Lami wai meke faruwane ya na ganki haka....?”
Aunty Lami na goge gumin da ya wanke mata fuska take fad’in “Ma’aruf ya dawo Haule... Shikenan kashinmu ta bushe... Haule idan muddin asirinmu ya tonu Alhaji Usman Mailafiya tsireni zaiyi shikenan na rabu da masoyina Haule... Wayyo Allah na wllhi ban tab’a danasani irinta yau ba Haule...” Ta k’arashe murya cikeda tsananin tsoro...
Hajiya ta zaro idanu waje had’ida dafe k’irji tace “Lami kina nufin kicemin hasashenmu ya tabbata wannan likitan shine Ma’aruf...?”