Sashe 29
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Batakai aya ba Najah ta katse ta da fad’in “Hajiya.. Abincinki akace mu dawo miki dashi amarya bataci snnan d’anki kuma kwance magashiyan muka taddasa don har muka shiga muka fito ban tsamman yasan munje ba, sirkarki kuwa ras take donma rawa mukaje muka taddata tana tik’a...” Daga haka sakai Najah tai zata wuce ta bar Hajiya rungume da kwanon k’osai tana k’are masa kallo...
Har Najah ta isa bakin k’ofar parlor ta juyo taceda Hajiya “Aw na mance Amarya tace wainar k’wai da kifi ko kaza zataci had’ida shayi maiji da lafiya...” Tana ida fad’in haka ta saki labulen parlorn ta shige...
Hajiya da zuciyarta ke faman bugu daurewa tai ta shiga masu sababi da fad’in “Yo ko ta fad’i haka ai batai k’arya ba, idan abinda takeso kenan ai sai a mata ba wani abu bane... Kudai shegen rashin hak’uri ne irin naku... Ince d’azun da rawar kanku kuka banne ni zaku kai mata kari don ku saba.. Kunje kuna masifa da rawar kai irin taku da kuka saba yo ba dole ku gundireta ba...” Ta k’arashe tana jefa k’osai guda a baki nan ta hangi Raihanah dake bakin famfo tana wanke wanke a gabanta akai komai, suna had’a idanu Hajiya ta sakar mata dak’uwa tana fad’in “Kin kalli uwarki mayya kawai.. Taso ki wuce ki tafi bakin babban kwalta ki sayo kifi yanzu ki d’aura idanma masu kifin bakin hanya basu fito ba ki wuce kasuwa ko tasha... Taso mana ina miki magana kahura kawai...” A d’ari Raihan ta k’arashe kashe famfon wanda da k’yar ake d’aure bakin hasalima ita kad’ai ta iya rufewa idan bata rufe da kyau ba ta bari ruwa yayita zuba haka zata fice mak’ota d’ebo ruwa a rijiyan mak’ota...
Jiki na rawa ta k’araso wajen Hajiya ta amshi kud’in ta d’auko hijab d’inta ta fice sai zuba sauri take tsoron kada tayi latti Hajiya ta jibgeta...
Daga yanda take tafiyar tana zuba sauri zaka fahimci sam ba’a nitse take ba tsoro da fargaba su suka cika mata zuciya, alla alla take ta samu masu kifin babban kwalta sun fito, aka kuwa yi sa’a mai teburi d’aya ya fito..
Sauri sauri Raiha ta sayi gammo guda na kifin kaman yanda Hajiya ta aiketa ta shiga zuba sauri don ta samu ta isa gida da wuri ga goyon Kausar a bayanta don dama haka take kusan yini da yarinyar a bayanta tana rainonta koda aikin gida zai kasheta tinda yaran Hajiya bayi zasuyi ba..
Kaman daga sama haka yaga giftawarsu ta gabansa, yayi saurin danna birki yana karanto innalillahi...
Cikin sauri Sameer ya fito yana duba mutanen da ya kusa kad’ewa idan zai iya tunawa irin haka ne kwanaki ya kusan faruwa dashi sanda ya kuskuri wata budurwa d’aukeda k’aramar yarinya...
Kausar na kuka Rainaha na kuka, ita Kausar kukan razana take yayinda Raihana ke kukan gammon kifin Hajiya da ya watse cikin culvert mai d’aukeda gurb’ataccen ruwa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*26*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sameer ya k’araso tamkar mai sand’a yana k’ok’arin duk’awa had’ida duban fuskar budurwar nan dake shesshek’ar kuka a hankali tana jijjiga yarinyar dake bayanta, duk sai yaji babu dad’i musamman da yaga gaba d’aya suke kukan babu babbar babu k’aramar, dama shi tuntuni mutum ne wanda kuka ke tsananin d’aga masa hankali musamman yaga mace ko k’aramin yaro na kuka duk yaji hankalinshi ya tashi...
Murya a hankali ya furta “Sannu koh.... Bakuji ciwo ba...?”
Sai sannan Raihanah ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana dubansa, maimakon ta masa magana sai kuma ta k’ara tintsirewa da kuka had’ida kifa kanta bata daina jijjiga Kausar da tuni ta bar kuka ba sai sakin ajiyab zuciya da takeyi.....
Sameer ya d’an shafi sumarsa cikeda damuwa kana ya kuma kai dubansa ga budurwar mai tsnanin k’arancin shekaru a iyaka duban da ya mata....
Duk’awa ya kumayi gabanta wannan karon kana yace “Akwai yanda ke maki ciwo ne....?”
Nanma shiru bata bashi amsa ba saima dad’a had’e hannayenta biyu datai waje guda tana matsan hawaye...
Har ya cire rai bazatace komai ba sai kuma ta shiga girgiza masa kai alamun a’a....
Samun k’warin gwiwar dad’a tanbayarta yayi...
“Inane gidanku...?”
Wannan karon d’ago watery eyes d’inta tai tana duban mutumin sai kuma ta dad’a kai dubanta ga kifin da tuni watse cikin ruwan dotti kana tace “Ni bazanje gida ba Hajiya duka zatamin....”
Yanda tai maganar yasa Sameer kuma dubanta sosai kana yace “Maiyasa zata bigeki.....?”
Sabon kuka ne ya kuma zuwa mata bata iya bashi amsa ba sai nuna masa culvert da ta shigayi tana mai ci gaba da shesshek’an kuka, Sameer yakai dubansa sosai ga culvert d’in yana kallon abinda take k’ok’arin nuna masa, maido da dubansa gareta yayi kana yace “Idan na fahimceki aiken Hajiya ne ya zube a nan koh...?”
Tai saurin jinjina masa kai tana mai share hwayenta...
“A ina ake saida kifin...?”
Ya tambaya yana dubanta...
Alama kurum ta masa da hannu tsallaken titi ba tareda tace komai ba....
Sameer ya jinjina kai kana yace “Just wait for me here kinji koh, I’ll be right back...”
Batace masa komai ba sai sadda kanta k’asa da tai tana matsan sauran hawayenta had’ida tausayin kanta da takeji don tasan yau dole ta daku hannun su Hajiya donma Sahariyya yau tanaji da nata k’unci da ta nad’i na jaki wajenta...
Jim kad’an ya dawo da gammon kifi kusan guda biyar cikin leda kana yace “Shiga mota na kaiku gidan naku...”
Dubansa ta d’anyi kana tace “A’a ni bazan shiga ba an hanamu....”
Sameer ya d’anyi shiru tamkar mai tunani kana yace “Idan na tare maki adaidaita zaki shiga...”
D’ago manyan idanunta masu tsananin haske tai tana dubansa sai kuma ta kauda kai gefe tace “Ai gidanmu babu nisa k’asan layin can ne....” Ta k’arashe tana mai nuni da hannunta...
Sameer yakai dubansa ga yanda tai masa nuni ya d’ago left hand d’insa yana duba time sabida surgery da yakedashi a asibiti, bai kuma ce mata komai ba sai komawa motarsa da yayi ya zaro key d’in had’ida sakata a security lock sannan ya dawo yanda Raihanah ke tsaye tamkar wacce ruwa ya shanye...
Duba guda Sameer ya mata kana yace “Muje ni zanyi maganawa Hajiyar bazata dakeki ba kinji koh...”
Raihanah da k’irjinta ya bada sauti saurin girgiza masa kai tai kana tace “A’a ka barshi kawai zan koma dakaina...”
Kallon da ya mata ya sanyata yin shiru, Sameer ya kuma fad’in “Muje..”
Wannan karon babu musu ta shige gaba yana biye da ita har suka iso layin nasu...
Koda suka iso k’ofar gidan kasa shiga Raihanah tai sai kallon ledae dake hannunsa take alamun tanajin tsoron shiga babu aiken kifin Hajiya...
Sameer na hankalce da ita, mik’a mata ledar hannun nasa yayi yana mai dubanta...
Hannu ta d’an mik’a zata karb’a sai kuma ta fasa..
Sameer ya gyara tsayuwarsa yace “Amsa ki kai mata sai ki sanar da ita ana sallama da ita a waje...”
Girgiza kai Raihana tai kana tace “Kifin gammo gudane ai kawai...”
Sameer ya jinjina kai yace “Babu damuwa ki kai mata ki fad’a mata sak’ona...”
Jiki a sanyaye ta amsa had’ida masa godiya kafin tasa kai zata shige gidan cikeda fargaba da tsoro nan ta jiyo muryarsa yana tambayarta sunanta...
A hankali ta juyo kaman mai tsoron magana tace dashi “Raihanah...”
A zuciyarsa ya maimaita sunan kana yabi bayanta da kallo cikeda tausayawa, sau tari yakansha mamaki idan yaga iyaye na dukan yaransu kaman basusan cewa yara babban kyautace daga Allah wanda ba kowa yake badawa, yanaji a ransa duk randa ya haifi nasa yaran bazai dasa masu tsoronsa cikin zuciyarsu ba saidai tsoron mahaliccinsu, yaransa zasu zama abokansa ta yanda bazasu b’oye masa komai ba zasu sharing komai dashi, rayuwa mai cikeda jin dad’i yake hango masu shida Partner da kuma yaranda zasu haifa in feature...
A hankali ya saki murmushi had’ida daidaita tsayuwarsa yana jiran fitowar Hajiya...
Duk daga nesa Hajiya ke aika mata dak’uwa da ashariya tana fad’in uwar mai ta tsayayi sai yanzu zata dawo, tuni ta janyota ta shiga rank’washi Raihanah na bata hak’uri, tuni su Sahariyya da Najah suka fito kallo suna dariya don dama idan Raihana tayi laifi idan Hajiya na bugunta tsallen da take tamkar ‘yar kenwace ke basu dariya
Cak Hajiya ta tsaya da bugun nata tana kallon damin kifin da tasan bata bata kud’in sayo kifi mai yawa haka ba...
D’ago fuskarta Hajiya tai tana kallo kana tace “Ke tsaya badai karuwanci kike da masu saida kifin ba suke arha maki haka....” Ta shiga doka salati tana tafe hannaye had’ida kuma mak’uro Raiha tana fad’in “Raiha... D’ago ki kalleni don ubanki ki fad’amin mai kike basu suke maki arha... No wonder shiyasa kika dad’e mana kin shige shagon mai kifi ya gama matseki dole ki dawomin da damin kifi toh kuwa a kunnen ubanki don nidai bazaki janyo min zagi a gari ba...”
Su Najah da Sahariyya an tab’o yanda ke masu k’aik’ayi tuni suka fito suma suka mata caa suna binta da kallon k’yama..
Cikin kuka Raihana ke fad’in “Hajiya ki tsaya kiji Hajiya wllhi ba haka bane babu abinda nayi Kausar itace shaidata...”
Haba nan fah su Sahariyya suka kwashe dariyar rainin hankali kana Sahariyya tace “Kunji shegiya wai Kausar shaida a gidan uban wa kika tab’ajin yarinya k’arama ta bada shaida ke annabiya ce kokuwa salon iskancinki ne haka, ma uban wa zaki raina hankali... Hajiya ki kwab’e mata fatari ki gani idan ba’a gama bud’ata waje ba... Shegiya k’aramar karuwa...” Ta k’arashe tana kai mata rank’washi mai tsananin zafi wanda ya sanyata sakin k’ara..
Hajiya na huci take fad’in “Naja mik’o min muciya naci uwarta da kyau sai ta fad’imin uban da take shagon masu saida kifi...”
Raihana ta bud’e baki zatai magana Hajiya ta gwab’e bakin da hannunta Sahariyya ta finciko Kausar daga bayan Raihanah ta ijiyeta k’asa, Kausar ta saki kuka mai k’arfi a daidai sanda Najah ta taho da muciyar tuk’a tuwo ta dank’awa Hajiya, Hajiya ta shiga shima mata tamkar an aikota..
Allah sarki Raihanah da ba’a bata dama tayi bayani ba sai ihun azaba take tana rok’on Hajiya da tai hak’uri zata fad’a... Abin tausayin shine dagaji kasan tsananin azaba ne kurum ya sanyata cewa zata fad’a ita kanta batasan mai take fad’i ba..
Har Najah ta isa bakin k’ofar parlor ta juyo taceda Hajiya “Aw na mance Amarya tace wainar k’wai da kifi ko kaza zataci had’ida shayi maiji da lafiya...” Tana ida fad’in haka ta saki labulen parlorn ta shige...
Hajiya da zuciyarta ke faman bugu daurewa tai ta shiga masu sababi da fad’in “Yo ko ta fad’i haka ai batai k’arya ba, idan abinda takeso kenan ai sai a mata ba wani abu bane... Kudai shegen rashin hak’uri ne irin naku... Ince d’azun da rawar kanku kuka banne ni zaku kai mata kari don ku saba.. Kunje kuna masifa da rawar kai irin taku da kuka saba yo ba dole ku gundireta ba...” Ta k’arashe tana jefa k’osai guda a baki nan ta hangi Raihanah dake bakin famfo tana wanke wanke a gabanta akai komai, suna had’a idanu Hajiya ta sakar mata dak’uwa tana fad’in “Kin kalli uwarki mayya kawai.. Taso ki wuce ki tafi bakin babban kwalta ki sayo kifi yanzu ki d’aura idanma masu kifin bakin hanya basu fito ba ki wuce kasuwa ko tasha... Taso mana ina miki magana kahura kawai...” A d’ari Raihan ta k’arashe kashe famfon wanda da k’yar ake d’aure bakin hasalima ita kad’ai ta iya rufewa idan bata rufe da kyau ba ta bari ruwa yayita zuba haka zata fice mak’ota d’ebo ruwa a rijiyan mak’ota...
Jiki na rawa ta k’araso wajen Hajiya ta amshi kud’in ta d’auko hijab d’inta ta fice sai zuba sauri take tsoron kada tayi latti Hajiya ta jibgeta...
Daga yanda take tafiyar tana zuba sauri zaka fahimci sam ba’a nitse take ba tsoro da fargaba su suka cika mata zuciya, alla alla take ta samu masu kifin babban kwalta sun fito, aka kuwa yi sa’a mai teburi d’aya ya fito..
Sauri sauri Raiha ta sayi gammo guda na kifin kaman yanda Hajiya ta aiketa ta shiga zuba sauri don ta samu ta isa gida da wuri ga goyon Kausar a bayanta don dama haka take kusan yini da yarinyar a bayanta tana rainonta koda aikin gida zai kasheta tinda yaran Hajiya bayi zasuyi ba..
Kaman daga sama haka yaga giftawarsu ta gabansa, yayi saurin danna birki yana karanto innalillahi...
Cikin sauri Sameer ya fito yana duba mutanen da ya kusa kad’ewa idan zai iya tunawa irin haka ne kwanaki ya kusan faruwa dashi sanda ya kuskuri wata budurwa d’aukeda k’aramar yarinya...
Kausar na kuka Rainaha na kuka, ita Kausar kukan razana take yayinda Raihana ke kukan gammon kifin Hajiya da ya watse cikin culvert mai d’aukeda gurb’ataccen ruwa....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*26*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sameer ya k’araso tamkar mai sand’a yana k’ok’arin duk’awa had’ida duban fuskar budurwar nan dake shesshek’ar kuka a hankali tana jijjiga yarinyar dake bayanta, duk sai yaji babu dad’i musamman da yaga gaba d’aya suke kukan babu babbar babu k’aramar, dama shi tuntuni mutum ne wanda kuka ke tsananin d’aga masa hankali musamman yaga mace ko k’aramin yaro na kuka duk yaji hankalinshi ya tashi...
Murya a hankali ya furta “Sannu koh.... Bakuji ciwo ba...?”
Sai sannan Raihanah ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana dubansa, maimakon ta masa magana sai kuma ta k’ara tintsirewa da kuka had’ida kifa kanta bata daina jijjiga Kausar da tuni ta bar kuka ba sai sakin ajiyab zuciya da takeyi.....
Sameer ya d’an shafi sumarsa cikeda damuwa kana ya kuma kai dubansa ga budurwar mai tsnanin k’arancin shekaru a iyaka duban da ya mata....
Duk’awa ya kumayi gabanta wannan karon kana yace “Akwai yanda ke maki ciwo ne....?”
Nanma shiru bata bashi amsa ba saima dad’a had’e hannayenta biyu datai waje guda tana matsan hawaye...
Har ya cire rai bazatace komai ba sai kuma ta shiga girgiza masa kai alamun a’a....
Samun k’warin gwiwar dad’a tanbayarta yayi...
“Inane gidanku...?”
Wannan karon d’ago watery eyes d’inta tai tana duban mutumin sai kuma ta dad’a kai dubanta ga kifin da tuni watse cikin ruwan dotti kana tace “Ni bazanje gida ba Hajiya duka zatamin....”
Yanda tai maganar yasa Sameer kuma dubanta sosai kana yace “Maiyasa zata bigeki.....?”
Sabon kuka ne ya kuma zuwa mata bata iya bashi amsa ba sai nuna masa culvert da ta shigayi tana mai ci gaba da shesshek’an kuka, Sameer yakai dubansa sosai ga culvert d’in yana kallon abinda take k’ok’arin nuna masa, maido da dubansa gareta yayi kana yace “Idan na fahimceki aiken Hajiya ne ya zube a nan koh...?”
Tai saurin jinjina masa kai tana mai share hwayenta...
“A ina ake saida kifin...?”
Ya tambaya yana dubanta...
Alama kurum ta masa da hannu tsallaken titi ba tareda tace komai ba....
Sameer ya jinjina kai kana yace “Just wait for me here kinji koh, I’ll be right back...”
Batace masa komai ba sai sadda kanta k’asa da tai tana matsan sauran hawayenta had’ida tausayin kanta da takeji don tasan yau dole ta daku hannun su Hajiya donma Sahariyya yau tanaji da nata k’unci da ta nad’i na jaki wajenta...
Jim kad’an ya dawo da gammon kifi kusan guda biyar cikin leda kana yace “Shiga mota na kaiku gidan naku...”
Dubansa ta d’anyi kana tace “A’a ni bazan shiga ba an hanamu....”
Sameer ya d’anyi shiru tamkar mai tunani kana yace “Idan na tare maki adaidaita zaki shiga...”
D’ago manyan idanunta masu tsananin haske tai tana dubansa sai kuma ta kauda kai gefe tace “Ai gidanmu babu nisa k’asan layin can ne....” Ta k’arashe tana mai nuni da hannunta...
Sameer yakai dubansa ga yanda tai masa nuni ya d’ago left hand d’insa yana duba time sabida surgery da yakedashi a asibiti, bai kuma ce mata komai ba sai komawa motarsa da yayi ya zaro key d’in had’ida sakata a security lock sannan ya dawo yanda Raihanah ke tsaye tamkar wacce ruwa ya shanye...
Duba guda Sameer ya mata kana yace “Muje ni zanyi maganawa Hajiyar bazata dakeki ba kinji koh...”
Raihanah da k’irjinta ya bada sauti saurin girgiza masa kai tai kana tace “A’a ka barshi kawai zan koma dakaina...”
Kallon da ya mata ya sanyata yin shiru, Sameer ya kuma fad’in “Muje..”
Wannan karon babu musu ta shige gaba yana biye da ita har suka iso layin nasu...
Koda suka iso k’ofar gidan kasa shiga Raihanah tai sai kallon ledae dake hannunsa take alamun tanajin tsoron shiga babu aiken kifin Hajiya...
Sameer na hankalce da ita, mik’a mata ledar hannun nasa yayi yana mai dubanta...
Hannu ta d’an mik’a zata karb’a sai kuma ta fasa..
Sameer ya gyara tsayuwarsa yace “Amsa ki kai mata sai ki sanar da ita ana sallama da ita a waje...”
Girgiza kai Raihana tai kana tace “Kifin gammo gudane ai kawai...”
Sameer ya jinjina kai yace “Babu damuwa ki kai mata ki fad’a mata sak’ona...”
Jiki a sanyaye ta amsa had’ida masa godiya kafin tasa kai zata shige gidan cikeda fargaba da tsoro nan ta jiyo muryarsa yana tambayarta sunanta...
A hankali ta juyo kaman mai tsoron magana tace dashi “Raihanah...”
A zuciyarsa ya maimaita sunan kana yabi bayanta da kallo cikeda tausayawa, sau tari yakansha mamaki idan yaga iyaye na dukan yaransu kaman basusan cewa yara babban kyautace daga Allah wanda ba kowa yake badawa, yanaji a ransa duk randa ya haifi nasa yaran bazai dasa masu tsoronsa cikin zuciyarsu ba saidai tsoron mahaliccinsu, yaransa zasu zama abokansa ta yanda bazasu b’oye masa komai ba zasu sharing komai dashi, rayuwa mai cikeda jin dad’i yake hango masu shida Partner da kuma yaranda zasu haifa in feature...
A hankali ya saki murmushi had’ida daidaita tsayuwarsa yana jiran fitowar Hajiya...
Duk daga nesa Hajiya ke aika mata dak’uwa da ashariya tana fad’in uwar mai ta tsayayi sai yanzu zata dawo, tuni ta janyota ta shiga rank’washi Raihanah na bata hak’uri, tuni su Sahariyya da Najah suka fito kallo suna dariya don dama idan Raihana tayi laifi idan Hajiya na bugunta tsallen da take tamkar ‘yar kenwace ke basu dariya
Cak Hajiya ta tsaya da bugun nata tana kallon damin kifin da tasan bata bata kud’in sayo kifi mai yawa haka ba...
D’ago fuskarta Hajiya tai tana kallo kana tace “Ke tsaya badai karuwanci kike da masu saida kifin ba suke arha maki haka....” Ta shiga doka salati tana tafe hannaye had’ida kuma mak’uro Raiha tana fad’in “Raiha... D’ago ki kalleni don ubanki ki fad’amin mai kike basu suke maki arha... No wonder shiyasa kika dad’e mana kin shige shagon mai kifi ya gama matseki dole ki dawomin da damin kifi toh kuwa a kunnen ubanki don nidai bazaki janyo min zagi a gari ba...”
Su Najah da Sahariyya an tab’o yanda ke masu k’aik’ayi tuni suka fito suma suka mata caa suna binta da kallon k’yama..
Cikin kuka Raihana ke fad’in “Hajiya ki tsaya kiji Hajiya wllhi ba haka bane babu abinda nayi Kausar itace shaidata...”
Haba nan fah su Sahariyya suka kwashe dariyar rainin hankali kana Sahariyya tace “Kunji shegiya wai Kausar shaida a gidan uban wa kika tab’ajin yarinya k’arama ta bada shaida ke annabiya ce kokuwa salon iskancinki ne haka, ma uban wa zaki raina hankali... Hajiya ki kwab’e mata fatari ki gani idan ba’a gama bud’ata waje ba... Shegiya k’aramar karuwa...” Ta k’arashe tana kai mata rank’washi mai tsananin zafi wanda ya sanyata sakin k’ara..
Hajiya na huci take fad’in “Naja mik’o min muciya naci uwarta da kyau sai ta fad’imin uban da take shagon masu saida kifi...”
Raihana ta bud’e baki zatai magana Hajiya ta gwab’e bakin da hannunta Sahariyya ta finciko Kausar daga bayan Raihanah ta ijiyeta k’asa, Kausar ta saki kuka mai k’arfi a daidai sanda Najah ta taho da muciyar tuk’a tuwo ta dank’awa Hajiya, Hajiya ta shiga shima mata tamkar an aikota..
Allah sarki Raihanah da ba’a bata dama tayi bayani ba sai ihun azaba take tana rok’on Hajiya da tai hak’uri zata fad’a... Abin tausayin shine dagaji kasan tsananin azaba ne kurum ya sanyata cewa zata fad’a ita kanta batasan mai take fad’i ba..