Sashe 11
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aunty Lami tace “Hafiz kam ai d’an albarka ne tinda ya zage yake cimin uban yarinyar nan da kyau yanzu babu wacce ta tsayamin a wuya kaman wancan yarinya figeggiya marar ta idon nan...”
“Nabilah koh...?” Inji Hajiya dake yamutsa fuska...
“Keda kika sani, shegiyar yarinya gaba d’aya ta tsayamin a wuya tamin k’ebebe na rasa ta yanda zan b’ullo ma lamarinta.....”
Hajiya tayi k’wafa kana tace “Kar ki damu k’awata itama haka zamu samo hanyar da zamu sabautar da rayuwarta, idan Mariya taga yaranta gaba d’aya suna wahala a gidan aure itama hankalinta sam bazai kwanta ba tinda dai dama itama ba dad’in takeji ba...”
Aunty Lami ta jinjina kai kana tace “Shikenan ni zan wuce sai kinji wayata yanda muka kaya da sirkarki...”
Suka kuma tafe hannaye had’ida shewa kafin Lami ta fice....
***
Ammi na k’arasowa yanda take wayar Siyamar ta d’au ruri, tamkar wacce aka zabura haka ta mik’e ta d’au wayar tana dubawa, hannayenta har rawa suke, hotonsa da ya bayyana da sunan Partner ya sanyatayin k’urima wayar, tun jiya take neman layinsa baya shiga tun bayan da ta kira taji isarsa, ta kira Sultan ma don taji ko lafiya saidai Sultan d’in ya sanar da ita sun rabu tun da rana don shi Abuja ya wuce...
A hankali ta saita kanta kafin ta d’aga wayar....
“Partner....” Ya fad’i daga d’aya b’angaren cikin sassanyar muryarsa...
Maimakon tayi magana sai kukan da ta sake masa....
Sameer yasan hakan ka iya faruwa, cikin kwantar da hankali ya soma fad’in “Siyama what’s wrong, meke faruwa...?”
Cikin kuka take fad’in “Really Partner..? Are you seriously asking me that question...? Kasan sau nawa nayi trying layinka baya shiga, I was so worried about you, amma kai da alama baka damu kasan halin da ka barni ciki ba....” Ta k’arashe cikin tsananin b’acin rai...
A hankali ya shafi sumarsa had’ida fuzar da iska kana yace “I’m sorry... Ki daina kuka kinji, I’m at work right now, we talk later kinji... I love you....” Daga haka bai jira cewarta ba ya katse wayar...
Da tsananin mamaki take duban wayar.... Bata daina duban wayar ba take fad’in “He hangup on me....” Tayi saurin juyowa ta dubi Ammi dake zaune gefenta ta mata k’uri kana tace “Ammi Sameer ya bar sona, kin gani fah kashe wayar yayi, aikinsa yafi mahimmanci a wajensa fiyedani....”
Rungumota Ammi tayi kana tace “Siyama don Allah ki kwantar da hankalinki ni irin wannan soyayya da kikewa Sameer har tsoro yake bani, shifa namiji ba’a nuna masa soyayya irin haka sabida b’acin rana, nasha fad’a miki ki koyi son abu baya baya irin wannan ne randa ya bijiro miki da halinsu na maza sai ki shiga damuwa koma ki jawa kanki wani cutan...”
Shiru tayi tana duban Ammi zuciyarta na gaya mata wani abu, kardai maganganun Ammi su tabbata watarana Sameer ya rabu da ita.... Take taji gabanta yayi mugun fad’uwa lallai kuwa zata iya rasa rayuwarta idan irin wannan ranar tazo....
Duban Ammi ta kumayi kana tace “Ammi kina ganin Sameer zai iya rabuwa dani...?”
Ammi ta sauk’e ajiyan zuciya kana tace “Bance zai rabu dake ba Siyama amma ki sani ita rayuwar nan komai ka iya faruwa, ba lallaine rayuwarmu ta tafi yanda muka tsara muke kuma so ba, wasu lokutan dole a samu sauyin lamari, kuma dole musa a ranmu komai ka iya faruwa ballanta namiji da sam baida tabbas, kina ganin abinda Babanku ya min yaje yayi aurensa a can wata k’asar ba tareda sanina ba, ba don zuwan social media ba k’ilada har yanzu bamusan nada wata matar ba... Kuma yanzu da haihuwa ta shiga tsakaninsu haka zaku tashi bakusan kunada wasu ‘yan uwa ba... Ke ya kamata kifi kowa d’aukan darasi tinda kece mutum ta farko da kika gano Daddynku has another wife....”
Tsoro da fargaba suka kuma kama Siyama, wannan dalili dama shiyasa ta zamto very paranoid, duk yanda mijinta yake tsoro da damuwar abunda ka iya zuwa yazo shike damunta, damuwarta kar Mijinta ya mata irin abinda mahaifinta yayiwa mahaifiyarta, so tari takan yarda Sameer na tsananin k’aunarta amma idan ta tuna yanda suka taso suka tadda iyayensu cikeda k’aunar juna sam bazakayi tunanin Daddy zai iya k’ara aure ba tareda sanin Ammi ba, wannan dalili yasa wani sa’ain take samun shakku dukda irin kula da soyayya da Sameer ke nuna mata, don bazata mance ba lokacin data gano Daddy nada wata matar ta hanyar facebook har saida tafi mahaifiyarta shiga tashin hankali, da k’yar ta yafewa magaifin nata don da ta d’au alwashin barin gidansa ne na har abada, shi kuwa a duniya yaransa sune rayuwarsa....
Da wannan tunani da maganganun Ammi yasa jikin Siyama yin matuk’ar sanyi, k’ok’arin danne zuciyarta tayi had’ida kashe wayar gaba d’aya don karma ta kasa jurewa ta kuma neman layin Sameer....
****
Tun daga waje yayi sallamada muk’arabban nasa don ba k’aramin gajjiya yayi ba burinsa ya shiga gida ya huta, yinin yau ranar sunyisa ne suna yawon campaign k’auyuka k’auyuka....
Baiyi mamakin ganinsu zube a parlor ba ko wacce ta rungume teddy bear d’inta tana bacci, k’aramar mai kimanin shekaru uku kwance cinyar ‘yar matashiyar mai kimanin shekaru shida su duka suna bacci, shi kuwa babban mai kimanin shekaru goma yana can gefe da alama shima gajjiya da buga game d’in yayi har bacci yayi awon gaba dashi....
A hankali yasoma takowa cikin parlorn had’ida k’urawa yaran nasa idanu cikeda tsananin tausayi da b’acin rai, har abada baijin Muhibbah zata samu lokacinsa dana yaransu, a baya yakan sakama ransa cewa INDA RAI da rabon ta daina a gaba amma ya lura hakan abune mai matuk’ar wahala, wannan shine rayuwar da Muhibbah ta girma akai ta kuma saba, so tari a baya sukan shirya tafiya k’asashe da ‘yan uwanta da iyayenta ba tareda saninsa ba wasu lokutan ma saidai yaga ana processing visa da sunan zasuyi tafiya Dad ya shirya tafiya zuwa k’asa kaza da yaransa gaba d’aya, bai isa kuma ya nuna k’in amincewarsa ba ko rashin yardarsa sai nasa mahaifin yayi fushi dashi, dashike Muhimma d’iyace ga aminin mahaifinsa, tun a lokutan baya kenan kafin mahaifinsa ya rasu, sannan lokacin da mahaifinsa ya kusa rasuwa saida ya kuma masa kashedi akan ya rik’e Muhibba ko mai zata masa idan har yana son gamawa da duniya lafiya wannan dalili yasa duk wani abunda Muhibbah zatayi yake k’ok’arin kawarda kai, yakai ya kawo yanzu bada ‘yan uwanta take yawon k’asashen dataga dama ba da k’awayenta gogaggun ‘yan bariki take, dama sam zaman gidan kam batayi rayuwar yaran da komai Nannies ke masu, a baya kafin commitments su masa yawa shi da kansa yake kulada yaransa idan ta tafi gantalinta....
K’aramar ya soma d’agawa da niyyar kaisu makwancinsu nan ko ya hangi busassun hawaye kwance a fuskarta, ta kuwa yi saurin k’ank’ameshi tana ambaton Daddy alamun da kukan tayi bacci, tsam ya rungumeta had’ida kwantar da ita saman kafad’unsa yana jijjjigata yana lallashi alamun yanaso ta koma baccin kaman daga sama yaji k’aran takalminta mai tsini waya manne a kunne tana aikin waya da k’awaye kaman yanda ta saba, suna kuma zuzutata da haukatata da sunan First Lady.....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*11*
Yana jin yanda ta nufi upstairs tana rangad’a kirawa ma’aikatan gidan, sam batayi tsammanin samunshi a sashenta ba dukda cewa taga motocinsa waje ga securities da suka k’aru hakan ya tabbatar mata yana gida....
Ta cikin k’ofar glass da ya raba staircase da cikin parlorn ta hango bayansa rungume da k’aramar ‘yarta mai suna Najma, saida ta juya idanunta kafin ta soma takowa ta shigo cikin parlorn tana fad’in “Ya akayi Murja ta barsu sukayi bacci a parlor, Gosh! I really don’t know what’s wrong with her, saida na fad’a mata ta tabbata ta kaisu d’akunansu don mai zata barsu zube a nan...?”
Tunda ta soma magana k’ala bai ce mata ba har Murja ta k’araso a guje cikeda d’imauta ganin irin muguwar kallo da uwar gijiyar tata ke aika mata....
Aiko kafin ta samu zarafin magana tun daga nesa Muhibbah ta tsareta da fad’in “Murja what’s meaning of all this, me nace miki kafin na fita... Ta yaya zaki bar min yara zube a nan kaman sun rasa gatansu, kinacan kin sake bakida hanci kina shegen kallon nan naki koh...?”
Cikin sark’ewar murya take fad’in “Haj... Hajiya kiyi hak’uri dama Irfaan ne yace zaiyi game bazai kwanta ba shine k’annen ke kuka saidai su zauna dashi shiyasa.....”
Bata kai aya ba Muhibbah ta kuma darara mata tsawa...
“Ni dallah rufe min baki before I lose my patience completely...”
Cikin kid’ima ta kuma nufo mahaifin yaran zata karb’i k’aramar jiki na rawa....
Girgiza mata kai yayi kana yace “Jeki abunki...” Ya fad’i a tak’aice
Cikin risinawa ta kuma basu hak’uri da alk’awarin hakan bazai kuma faruwa ba kana ta fice....
Kafesa da idanu Muhibbah tayi ganin kota kanta baibi ba ya nufi upstairs da d’iyarsa....
Cak ya tsaya da tafiyar nasa sanda ya sinkayo muryarta tana fad’in “Meye ma’anar abunda kayi kenan... Yaya zan baiwa mai aikina umarni kace ta barshi...? Kuma dai kasan ba iya d’aukan yaran nan zanyi ba, don babu wanda zan iya d’agawa cikinsu...”! Ta k’arashe tana jifa da jakkanta saman kujera.....
Baice komai ba haka nan bai juyo ya dubeta ba yaci gaba da tafiyarsa... Haka ya dinga sintirin kai yaran d’akunan baccinsu had’ida tofa masu azkar na bacci kana ya sauk’o don tafiya sashensa, har lokacin Muhibbah na make saman kujera tana faman ci gaba da waya...
Baice mata ci kanki ba ya sunkuya ya d’auki agogonsa da links dinsa saman center table....
Tab’e baki tayi sanda ya fice kana ta mik’e ta nufi d’akinta don shirin bacci....
Kaman ko yaushe saida tayi wanka ta shafa mayukan k’amshinta masu tafiya da hankalin mijinta duk kalan fushin da yake ciki, tayi wasu ‘yan kimtse kimtsen da take kafin bacci kana ta nufi sashen mijin nata....
Bata sameshi cikin d’akin ba hakan ya tabbatar mata cewa band’aki yake don tana iya jiyo zuban ruwa daga yanda take kwance saman gadonsa....
Sam bai kula da ita ba don hankalinsa naga warware hannun jallabiyar dake jikinsa da alama alwala ya d’auro...
“Nabilah koh...?” Inji Hajiya dake yamutsa fuska...
“Keda kika sani, shegiyar yarinya gaba d’aya ta tsayamin a wuya tamin k’ebebe na rasa ta yanda zan b’ullo ma lamarinta.....”
Hajiya tayi k’wafa kana tace “Kar ki damu k’awata itama haka zamu samo hanyar da zamu sabautar da rayuwarta, idan Mariya taga yaranta gaba d’aya suna wahala a gidan aure itama hankalinta sam bazai kwanta ba tinda dai dama itama ba dad’in takeji ba...”
Aunty Lami ta jinjina kai kana tace “Shikenan ni zan wuce sai kinji wayata yanda muka kaya da sirkarki...”
Suka kuma tafe hannaye had’ida shewa kafin Lami ta fice....
***
Ammi na k’arasowa yanda take wayar Siyamar ta d’au ruri, tamkar wacce aka zabura haka ta mik’e ta d’au wayar tana dubawa, hannayenta har rawa suke, hotonsa da ya bayyana da sunan Partner ya sanyatayin k’urima wayar, tun jiya take neman layinsa baya shiga tun bayan da ta kira taji isarsa, ta kira Sultan ma don taji ko lafiya saidai Sultan d’in ya sanar da ita sun rabu tun da rana don shi Abuja ya wuce...
A hankali ta saita kanta kafin ta d’aga wayar....
“Partner....” Ya fad’i daga d’aya b’angaren cikin sassanyar muryarsa...
Maimakon tayi magana sai kukan da ta sake masa....
Sameer yasan hakan ka iya faruwa, cikin kwantar da hankali ya soma fad’in “Siyama what’s wrong, meke faruwa...?”
Cikin kuka take fad’in “Really Partner..? Are you seriously asking me that question...? Kasan sau nawa nayi trying layinka baya shiga, I was so worried about you, amma kai da alama baka damu kasan halin da ka barni ciki ba....” Ta k’arashe cikin tsananin b’acin rai...
A hankali ya shafi sumarsa had’ida fuzar da iska kana yace “I’m sorry... Ki daina kuka kinji, I’m at work right now, we talk later kinji... I love you....” Daga haka bai jira cewarta ba ya katse wayar...
Da tsananin mamaki take duban wayar.... Bata daina duban wayar ba take fad’in “He hangup on me....” Tayi saurin juyowa ta dubi Ammi dake zaune gefenta ta mata k’uri kana tace “Ammi Sameer ya bar sona, kin gani fah kashe wayar yayi, aikinsa yafi mahimmanci a wajensa fiyedani....”
Rungumota Ammi tayi kana tace “Siyama don Allah ki kwantar da hankalinki ni irin wannan soyayya da kikewa Sameer har tsoro yake bani, shifa namiji ba’a nuna masa soyayya irin haka sabida b’acin rana, nasha fad’a miki ki koyi son abu baya baya irin wannan ne randa ya bijiro miki da halinsu na maza sai ki shiga damuwa koma ki jawa kanki wani cutan...”
Shiru tayi tana duban Ammi zuciyarta na gaya mata wani abu, kardai maganganun Ammi su tabbata watarana Sameer ya rabu da ita.... Take taji gabanta yayi mugun fad’uwa lallai kuwa zata iya rasa rayuwarta idan irin wannan ranar tazo....
Duban Ammi ta kumayi kana tace “Ammi kina ganin Sameer zai iya rabuwa dani...?”
Ammi ta sauk’e ajiyan zuciya kana tace “Bance zai rabu dake ba Siyama amma ki sani ita rayuwar nan komai ka iya faruwa, ba lallaine rayuwarmu ta tafi yanda muka tsara muke kuma so ba, wasu lokutan dole a samu sauyin lamari, kuma dole musa a ranmu komai ka iya faruwa ballanta namiji da sam baida tabbas, kina ganin abinda Babanku ya min yaje yayi aurensa a can wata k’asar ba tareda sanina ba, ba don zuwan social media ba k’ilada har yanzu bamusan nada wata matar ba... Kuma yanzu da haihuwa ta shiga tsakaninsu haka zaku tashi bakusan kunada wasu ‘yan uwa ba... Ke ya kamata kifi kowa d’aukan darasi tinda kece mutum ta farko da kika gano Daddynku has another wife....”
Tsoro da fargaba suka kuma kama Siyama, wannan dalili dama shiyasa ta zamto very paranoid, duk yanda mijinta yake tsoro da damuwar abunda ka iya zuwa yazo shike damunta, damuwarta kar Mijinta ya mata irin abinda mahaifinta yayiwa mahaifiyarta, so tari takan yarda Sameer na tsananin k’aunarta amma idan ta tuna yanda suka taso suka tadda iyayensu cikeda k’aunar juna sam bazakayi tunanin Daddy zai iya k’ara aure ba tareda sanin Ammi ba, wannan dalili yasa wani sa’ain take samun shakku dukda irin kula da soyayya da Sameer ke nuna mata, don bazata mance ba lokacin data gano Daddy nada wata matar ta hanyar facebook har saida tafi mahaifiyarta shiga tashin hankali, da k’yar ta yafewa magaifin nata don da ta d’au alwashin barin gidansa ne na har abada, shi kuwa a duniya yaransa sune rayuwarsa....
Da wannan tunani da maganganun Ammi yasa jikin Siyama yin matuk’ar sanyi, k’ok’arin danne zuciyarta tayi had’ida kashe wayar gaba d’aya don karma ta kasa jurewa ta kuma neman layin Sameer....
****
Tun daga waje yayi sallamada muk’arabban nasa don ba k’aramin gajjiya yayi ba burinsa ya shiga gida ya huta, yinin yau ranar sunyisa ne suna yawon campaign k’auyuka k’auyuka....
Baiyi mamakin ganinsu zube a parlor ba ko wacce ta rungume teddy bear d’inta tana bacci, k’aramar mai kimanin shekaru uku kwance cinyar ‘yar matashiyar mai kimanin shekaru shida su duka suna bacci, shi kuwa babban mai kimanin shekaru goma yana can gefe da alama shima gajjiya da buga game d’in yayi har bacci yayi awon gaba dashi....
A hankali yasoma takowa cikin parlorn had’ida k’urawa yaran nasa idanu cikeda tsananin tausayi da b’acin rai, har abada baijin Muhibbah zata samu lokacinsa dana yaransu, a baya yakan sakama ransa cewa INDA RAI da rabon ta daina a gaba amma ya lura hakan abune mai matuk’ar wahala, wannan shine rayuwar da Muhibbah ta girma akai ta kuma saba, so tari a baya sukan shirya tafiya k’asashe da ‘yan uwanta da iyayenta ba tareda saninsa ba wasu lokutan ma saidai yaga ana processing visa da sunan zasuyi tafiya Dad ya shirya tafiya zuwa k’asa kaza da yaransa gaba d’aya, bai isa kuma ya nuna k’in amincewarsa ba ko rashin yardarsa sai nasa mahaifin yayi fushi dashi, dashike Muhimma d’iyace ga aminin mahaifinsa, tun a lokutan baya kenan kafin mahaifinsa ya rasu, sannan lokacin da mahaifinsa ya kusa rasuwa saida ya kuma masa kashedi akan ya rik’e Muhibba ko mai zata masa idan har yana son gamawa da duniya lafiya wannan dalili yasa duk wani abunda Muhibbah zatayi yake k’ok’arin kawarda kai, yakai ya kawo yanzu bada ‘yan uwanta take yawon k’asashen dataga dama ba da k’awayenta gogaggun ‘yan bariki take, dama sam zaman gidan kam batayi rayuwar yaran da komai Nannies ke masu, a baya kafin commitments su masa yawa shi da kansa yake kulada yaransa idan ta tafi gantalinta....
K’aramar ya soma d’agawa da niyyar kaisu makwancinsu nan ko ya hangi busassun hawaye kwance a fuskarta, ta kuwa yi saurin k’ank’ameshi tana ambaton Daddy alamun da kukan tayi bacci, tsam ya rungumeta had’ida kwantar da ita saman kafad’unsa yana jijjjigata yana lallashi alamun yanaso ta koma baccin kaman daga sama yaji k’aran takalminta mai tsini waya manne a kunne tana aikin waya da k’awaye kaman yanda ta saba, suna kuma zuzutata da haukatata da sunan First Lady.....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*11*
Yana jin yanda ta nufi upstairs tana rangad’a kirawa ma’aikatan gidan, sam batayi tsammanin samunshi a sashenta ba dukda cewa taga motocinsa waje ga securities da suka k’aru hakan ya tabbatar mata yana gida....
Ta cikin k’ofar glass da ya raba staircase da cikin parlorn ta hango bayansa rungume da k’aramar ‘yarta mai suna Najma, saida ta juya idanunta kafin ta soma takowa ta shigo cikin parlorn tana fad’in “Ya akayi Murja ta barsu sukayi bacci a parlor, Gosh! I really don’t know what’s wrong with her, saida na fad’a mata ta tabbata ta kaisu d’akunansu don mai zata barsu zube a nan...?”
Tunda ta soma magana k’ala bai ce mata ba har Murja ta k’araso a guje cikeda d’imauta ganin irin muguwar kallo da uwar gijiyar tata ke aika mata....
Aiko kafin ta samu zarafin magana tun daga nesa Muhibbah ta tsareta da fad’in “Murja what’s meaning of all this, me nace miki kafin na fita... Ta yaya zaki bar min yara zube a nan kaman sun rasa gatansu, kinacan kin sake bakida hanci kina shegen kallon nan naki koh...?”
Cikin sark’ewar murya take fad’in “Haj... Hajiya kiyi hak’uri dama Irfaan ne yace zaiyi game bazai kwanta ba shine k’annen ke kuka saidai su zauna dashi shiyasa.....”
Bata kai aya ba Muhibbah ta kuma darara mata tsawa...
“Ni dallah rufe min baki before I lose my patience completely...”
Cikin kid’ima ta kuma nufo mahaifin yaran zata karb’i k’aramar jiki na rawa....
Girgiza mata kai yayi kana yace “Jeki abunki...” Ya fad’i a tak’aice
Cikin risinawa ta kuma basu hak’uri da alk’awarin hakan bazai kuma faruwa ba kana ta fice....
Kafesa da idanu Muhibbah tayi ganin kota kanta baibi ba ya nufi upstairs da d’iyarsa....
Cak ya tsaya da tafiyar nasa sanda ya sinkayo muryarta tana fad’in “Meye ma’anar abunda kayi kenan... Yaya zan baiwa mai aikina umarni kace ta barshi...? Kuma dai kasan ba iya d’aukan yaran nan zanyi ba, don babu wanda zan iya d’agawa cikinsu...”! Ta k’arashe tana jifa da jakkanta saman kujera.....
Baice komai ba haka nan bai juyo ya dubeta ba yaci gaba da tafiyarsa... Haka ya dinga sintirin kai yaran d’akunan baccinsu had’ida tofa masu azkar na bacci kana ya sauk’o don tafiya sashensa, har lokacin Muhibbah na make saman kujera tana faman ci gaba da waya...
Baice mata ci kanki ba ya sunkuya ya d’auki agogonsa da links dinsa saman center table....
Tab’e baki tayi sanda ya fice kana ta mik’e ta nufi d’akinta don shirin bacci....
Kaman ko yaushe saida tayi wanka ta shafa mayukan k’amshinta masu tafiya da hankalin mijinta duk kalan fushin da yake ciki, tayi wasu ‘yan kimtse kimtsen da take kafin bacci kana ta nufi sashen mijin nata....
Bata sameshi cikin d’akin ba hakan ya tabbatar mata cewa band’aki yake don tana iya jiyo zuban ruwa daga yanda take kwance saman gadonsa....
Sam bai kula da ita ba don hankalinsa naga warware hannun jallabiyar dake jikinsa da alama alwala ya d’auro...