Sashe 142
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya Abidah kuka take sosai tana k’ank’ame da Engr yayinda shima Engr d’in ya kasa sakinta, sosai shima ya k’ank’ameta yana kuka tamkar ba shi d’inba... Allahu Akbar yau ina Babansa yaga wannan rana mai tarin alkhairi a garesa.... Cikin murya irinta mai kuka take furta “Ma’aruf d’ah na.... Ma’aruf ka dawo.. Ka dawo gareni.... Da gaske kaine ba mafarki nake ba.... Da gaske kaine nake rik’e dakai yau.... Da gaske bazan farka daga wannan mafarki ba.....!!” Kuka ya kuma cin k’arfinta...
Cikin kuka shima Engr yake jinjina kai yana mai furta “Ammmah nah.... Ni ne da gaske ni ne.... Ni ne Ma’aruf d’inki.... Ba mafarki kike ba ni ne right in front of you... Ubangijinmu ya cika Rahamarsa a garemu, Ya sake had’amu bayan wasu shekaru... Bayan na mance rayuwar da mukai a baya, bayan na mance komai gameda ahalina.... Amma Ke d’in jigoce da zuciyata da ruhi bazasu tab’a mancewa ba, randa dik sukai arba da kyakkyawar fuskarki dole su tina hakan.... Ammah na tino komai... Kallon fuskarki ya maidoda tinanin yaron da ya b’ace sama da shekaru talatin da bakwai baya...!” Zuciyoyi suka kuma raunana... Allah Akbar abin godiya, baka jin komai wajen sai sautin fitar kuka daga can k’asan zukata.... Lallai wannan ahali yau rana ce mai matuk’ar mahimmanci a garesu... Daula data fito dan tambayar ta ina zatai alwala dan already magrib ya sako kai, tin bayan sallan la’asar ake gudanar da wannan warware warware basu suka ida warwaran ba sai goshin sallan magrib, abubuwa da dama ne suka auku tsakanin sallan la’asar da kuma sallan Magrib....
Ganin mutane cirko cirko yasa Daula shan jinin jikinta har sai take tinanin dama bata fito ba ashe, sam batai tsammanin ganin mutane haka a tsakar gidan ba dikda cewa gida ne na biki amma batai zaton ganin manyan mutane haka ba harda maza, kuma ya dukkan alamu mihimmin abu suke tattaunawa, ga wani irin yanayi da d’aukacin fuskokinsu Ke ciki..... Har tasa kai zata juya ta hango wani tamkar Yayanta rungume da wata mata yana share mata hawaye., Yanayin data gansa ciki bata tab’a ganinsa cikin irin yanayin ba tsawon shekarun da sukai tare....
Jiki a matuk’ar sanyaye Daula ta soma takowa tana mai bin jama’an dake wajen da duba a matuk’ar d’arare... Toh lafiya... Badai wani abin bane ya sami Khalid ko Daddy tinda tasan hakan ne kawai zai kawo Yayanta gidan sirakan Khalid... Toh amma tambayar anan shine wacece Matar da Engr Ke rungumeda ita ya kasa sakinta....
“Yaya...!” Ta furta tana mai dubansa jiki a sanyaye sanda ta k’araso garesu... Sai sannan Ya Abida ta karkato tana duban wacce tai magana sakamakon sinkayo murya irinta mahaifiyarsu da tai, su Mamy da Bara’atu bugun zuciyarsu ya kuma k’aruwa sanda suke kuma dubanta, tabbas sunji da kyau Yaya ta kira Ma’aruf da bai jima da bayyana masu ba.... Kodai hasashensu ne ya zamto gaskiya...? Basukaiga bashi amsa ba sukaga Engr Ma’aruf ya nufeta yana kuma janyo hannunta lokaci guda yake furta “Daula finally... Yau mun had’udasu... Come zo, zo kigani da idanunki.....!” Gaba d’aya kallo guda zaka masa ka fahimci har yanzu Shock d’insa bai sakesa ba dikda juriya da k’arfin hali da yake k’ok’arin nunawa....
Daula da jikinta ya gama sanyi duban Engr take tana duban mutanen da ya kawota gabansu mata guda uku Mahaifiyar Nabilah saiko wasu guda biyu wad’anda kallo guda zaka masu ka fahimci ‘yanuwan juna ne dan ga wani sihirtaccen kamanni da sukedashi.... Ganinsu su uku haka a gabanta take ya haifar mata da wani irin fad’uwan gaba, taji k’irjinta tamkar an sauk’e mata guduma... Kai tsaye bazatace ta tab’a sanin masu irin fuskokinsu ba amma sai tanaji can k’asan zuciyarta kaman sunsan juna tinda jimawa, like they’re connected somehow.... Cikin rud’ani take duban Engr da ya kasa sakin hannunta kana tace “Yaya what is going on here...? Is something wrong...? Wani abu ne ya samu Daddy da Khalid...? Please talk to me...!” Ta k’arashe cikin tsananin nuna damuwa, yayinda Yaya Abida, Mamy da kuma Aunty Bara’atu suka kasa d’auke idanunsu daga barin dubanta.... Wannan tabbas ‘yaruwarsu ce Fatima, domin kaw mahaifiyarsu ziryan suke kallo a gabansu.... Engr kansa kasa furta komai yai sai kallonsu su hud’u d’in da yake yau Allah ya kuma had’asu gaba d’aya... Sameer da sassanyar murmushi ta kasa barin fuskarsa takowa yai kad’an ya tsaya daga gefen Engr wani ikon Allah sai kamanninsu da Engr ya fito k’arara... K’wayan idanunsu yai shige da juna dan irin k’wayan idanun su Mamy suka d’auko... Sai yanzu suke fahimtar abubuwan da sukaji gameda juna had’uwarsu ta fari ashe sud’in tushe ne guda...
Abbah dake gefe matsan k’walla ya kumayi farin cikin da yake ciki ya gaza b’oyuwa, dole ne ma ya taya Mariya Farin ciki bayan irin gwagwarmayar rayuwa data fuskanta, a hankali ya silale ya fice sanda zuciyarsa ta shiga tino masa abubuwan da yaji gameda Mamaninsa, babban abinda yafi d’aga masa hankali tana sane da duka wannan ta d’auki karan tsana da tsangwama ta d’aura kan Mariyarsa bama ita kad’ai ba harda Zulfa’u da take jinjira ce a lokacin kuma ba ita ta haifo kanta a wannan rana ba, Mamani bata tsaya a nan ba tasa shima kansa ya dinga ganin laifin Mariya duk da sunan yana biyayyawa mahaifiyarsa...Shin ta ina zai soma d’aukan girman hakkin Mariya da Zulfa’u....Dole ne ya nemi waje ya keb’e shikad’ai, Mariya yau d’in cikin Farin ciki take bai kamata ya aza mata nasa damuwar ba, bayan tilin iftila’in data fuskanta a rayuwa yau d’in ta cancanci farin ciki... A daidai hanyar fita idanunsa suka sauk’a kan Lami dake sanne sannen kai tamkar tsohuwar munafuka... Idanunsu kaw suka sark’e waje guda... Duba guda Abbah yai mata ya d’auke kansa kana yai shigewarsa.... Wani irin k’ugi da cikin Lami yai da ace akwai wani gefenta tabbas da sai yaji wannan sauti... Suna murnan yau zai kansancega Mariya da ‘yaruwarta ranan tozarta ranan bak’in ciki sai gashi ya faru akansu, sai gashi ya juye ya koma kansu, ashe farin ciki mai d’orewa da aukaci burin samu a yau d’in ashe ba nasu bane, wacce suka kafa mata tarkon bak’in cikin ashe itace dai mai samun farin ciki.... Lami taji duniyar gaba d’aya tai mata d’aci...Ji tai inama ana iya maida hannun agogo baya tabbas da ta maida ta gyara kuramuren da tai, tabbas da bata biyema Haule sukai son zuciya ba... Yau wa gari ya waya...? Ita batada tsuntsu batada tarko, ko Abbah bai koreta ba bata tinanin zata iya ci gaba da zama tana fuskantar Mariya da Ma’aruf harma dashi kanshi Abban... Ita ba zuri’a ne da ita a gidan ba balle su kasance tareda ita... She’s all alone now, Tai imani Haule ta jima tana munafunatarta kenan dikda cewa tana nuna mata tare suke aikata komai, ashe tana b’oye mata wasu abubuwan... Sai yanzu ta fahimci nufin Haule na aurawa Ma’aruf d’iyarta Sahariyya Wato ita da mijinta idan Ma’aruf ya auri d’iyarsu su sun tsira ita kad’ai za’a bari a rana.... Lallai Haule ta cika makira butulu....! Tamkar kazar da aka tsamo cikin ruwan zafi haka Lami ta janye k’afufunta ta nufi nata sashen zuciyarta na mata d’aci.... Ga goggonayen Kazaure sai b’alla mata harara had’ida Allah wadar suke har Lami ta bar wajen....
Su Baffah Wada da Baffah Ado kuwa sun kasa aminta da wannan al’amari da ya bayyana kansa yau, koda ace mahaifiyarsu tsananin soyayyar Usman yasa ta rufe sirrin cewa shid’in ba d’anta bane sunaga Ya Usman ya cancanci yasan gaskiyar Al’amari yasan wacece mahaifiyarsa ko dan ya dinga isar da addu’arsa gareta, girman mahaifiya ya wuce wasa koda ace haihuwarsa kawai tai rainonsa da shayarwansa dik na wuyan Mamani amma dikda haka ya cancanci yasan asalin labarin, hakan baikai ya baiwa Mamani dama ta rufe wannan babban Sirri a gareshi ba... Ya Usman mutumin k’warai ne d’an uwa da kowa zai alfahari dashi, shid’in shine katangan family d’insu shine kuma Uba a garesu... Tsananin tausayin d’an uwan nasu ya kamasu, suna gani Baba Alhaji ya rab’a ta gefensu ya fice sim sim cikeda borin kunya... Suma d’in waje suka nufa dan gabatar da sallahn magrib suna fatan su tadda Abbah a masallaci su kuma supporting d’insa a irin wannan lokaci mai matuk’ar wahala a gareshi... Sameer da Engr ma a tare suka fice suka nufi masallaci jama’a ‘yan unguwa sai kawo masa gaisuwarsu suke suna fad’in yau ga his Excellency har unguwarsu kaikace already yaci zab’en ne sabida yanda jama’a Ke tururuwar zuwa gaidashi, har wad’nda basa zuwa wannan masallacin yau saida sukaje... Sameer kaw na taredashi sai sakin murmushi yake yanajin dad’i har k’asan zuciyarsa na kasancewarsa tareda d’an uwansa...
A cikin gida kaw banda tafasa babu abinda k’irjin Haule keyi, tabbas da za’a tsaga k’irjin Haule watak’ila aji yanda zuciyarta ke tafarfasa sabida tsananin k’unan zuciya... Ji take tamkar ta k’arasa ta shak’e Mariya da ahalinta gaba d’aya su mutu ta huta da wannan bak’in rana da take gani.... Idanunta suka sauk’a kan Yaya Abida yanda ta had’e ‘Yanuwanta gaba d’ai ta rungumesu gaba d’ai suna hawayen Farin ciki ga annashuwa da annuri da ya kasa barin fuskokinsu.... Haule tamkar zakanya haka take huci tana dubansu yanda kasan zatai tsalle ta wantsalo ta capkosu ta cinye d’aya bayan d’aya haka nan take dubansu, tamkar d’an wasan Dambe a filin kokawa haka Haule Ke bud’e hannaye tana haki tana duban bayin Allahn nan da duniyarsu ta yalwatu da Albarka... Wato Bara’atu da Abida sun cuceta sun jima suna tarwatsa duk wani shirin da take... Idanunta suka sauk’a kan Bara’atu da itace ta munafuncesu ta k’ulla aminci k’arya dasu... Tabbas sai yanzu take ganin wautansu.. (Niko nace Haule ai shi mugunta fitsarin fako ne... Kuma kece dai baki sani ba amma dik kalan asirinki da imani da ‘yan tsubbu da kikai bawa baya tab’a yiwa d’anuwasa bawa abinda Allah bai k’addara masa ba.... Asiri da sihiri gaskiya ne tinda har yai tasiri akan fiyayyen halitta babu wanda yafi k’arfin sammu ko sihiri ya kamasa saidai duk wannan zai faru ne da izinin Ubangiji... Mariya batada wani makari sai Allah data rik’a Wanda yafi k’arfin bokayanku da malaman tsubbunku... Su Haule sai a koma islamiyya a yak’i jahilci idan kinada sauran RABO)...
Cikin kuka shima Engr yake jinjina kai yana mai furta “Ammmah nah.... Ni ne da gaske ni ne.... Ni ne Ma’aruf d’inki.... Ba mafarki kike ba ni ne right in front of you... Ubangijinmu ya cika Rahamarsa a garemu, Ya sake had’amu bayan wasu shekaru... Bayan na mance rayuwar da mukai a baya, bayan na mance komai gameda ahalina.... Amma Ke d’in jigoce da zuciyata da ruhi bazasu tab’a mancewa ba, randa dik sukai arba da kyakkyawar fuskarki dole su tina hakan.... Ammah na tino komai... Kallon fuskarki ya maidoda tinanin yaron da ya b’ace sama da shekaru talatin da bakwai baya...!” Zuciyoyi suka kuma raunana... Allah Akbar abin godiya, baka jin komai wajen sai sautin fitar kuka daga can k’asan zukata.... Lallai wannan ahali yau rana ce mai matuk’ar mahimmanci a garesu... Daula data fito dan tambayar ta ina zatai alwala dan already magrib ya sako kai, tin bayan sallan la’asar ake gudanar da wannan warware warware basu suka ida warwaran ba sai goshin sallan magrib, abubuwa da dama ne suka auku tsakanin sallan la’asar da kuma sallan Magrib....
Ganin mutane cirko cirko yasa Daula shan jinin jikinta har sai take tinanin dama bata fito ba ashe, sam batai tsammanin ganin mutane haka a tsakar gidan ba dikda cewa gida ne na biki amma batai zaton ganin manyan mutane haka ba harda maza, kuma ya dukkan alamu mihimmin abu suke tattaunawa, ga wani irin yanayi da d’aukacin fuskokinsu Ke ciki..... Har tasa kai zata juya ta hango wani tamkar Yayanta rungume da wata mata yana share mata hawaye., Yanayin data gansa ciki bata tab’a ganinsa cikin irin yanayin ba tsawon shekarun da sukai tare....
Jiki a matuk’ar sanyaye Daula ta soma takowa tana mai bin jama’an dake wajen da duba a matuk’ar d’arare... Toh lafiya... Badai wani abin bane ya sami Khalid ko Daddy tinda tasan hakan ne kawai zai kawo Yayanta gidan sirakan Khalid... Toh amma tambayar anan shine wacece Matar da Engr Ke rungumeda ita ya kasa sakinta....
“Yaya...!” Ta furta tana mai dubansa jiki a sanyaye sanda ta k’araso garesu... Sai sannan Ya Abida ta karkato tana duban wacce tai magana sakamakon sinkayo murya irinta mahaifiyarsu da tai, su Mamy da Bara’atu bugun zuciyarsu ya kuma k’aruwa sanda suke kuma dubanta, tabbas sunji da kyau Yaya ta kira Ma’aruf da bai jima da bayyana masu ba.... Kodai hasashensu ne ya zamto gaskiya...? Basukaiga bashi amsa ba sukaga Engr Ma’aruf ya nufeta yana kuma janyo hannunta lokaci guda yake furta “Daula finally... Yau mun had’udasu... Come zo, zo kigani da idanunki.....!” Gaba d’aya kallo guda zaka masa ka fahimci har yanzu Shock d’insa bai sakesa ba dikda juriya da k’arfin hali da yake k’ok’arin nunawa....
Daula da jikinta ya gama sanyi duban Engr take tana duban mutanen da ya kawota gabansu mata guda uku Mahaifiyar Nabilah saiko wasu guda biyu wad’anda kallo guda zaka masu ka fahimci ‘yanuwan juna ne dan ga wani sihirtaccen kamanni da sukedashi.... Ganinsu su uku haka a gabanta take ya haifar mata da wani irin fad’uwan gaba, taji k’irjinta tamkar an sauk’e mata guduma... Kai tsaye bazatace ta tab’a sanin masu irin fuskokinsu ba amma sai tanaji can k’asan zuciyarta kaman sunsan juna tinda jimawa, like they’re connected somehow.... Cikin rud’ani take duban Engr da ya kasa sakin hannunta kana tace “Yaya what is going on here...? Is something wrong...? Wani abu ne ya samu Daddy da Khalid...? Please talk to me...!” Ta k’arashe cikin tsananin nuna damuwa, yayinda Yaya Abida, Mamy da kuma Aunty Bara’atu suka kasa d’auke idanunsu daga barin dubanta.... Wannan tabbas ‘yaruwarsu ce Fatima, domin kaw mahaifiyarsu ziryan suke kallo a gabansu.... Engr kansa kasa furta komai yai sai kallonsu su hud’u d’in da yake yau Allah ya kuma had’asu gaba d’aya... Sameer da sassanyar murmushi ta kasa barin fuskarsa takowa yai kad’an ya tsaya daga gefen Engr wani ikon Allah sai kamanninsu da Engr ya fito k’arara... K’wayan idanunsu yai shige da juna dan irin k’wayan idanun su Mamy suka d’auko... Sai yanzu suke fahimtar abubuwan da sukaji gameda juna had’uwarsu ta fari ashe sud’in tushe ne guda...
Abbah dake gefe matsan k’walla ya kumayi farin cikin da yake ciki ya gaza b’oyuwa, dole ne ma ya taya Mariya Farin ciki bayan irin gwagwarmayar rayuwa data fuskanta, a hankali ya silale ya fice sanda zuciyarsa ta shiga tino masa abubuwan da yaji gameda Mamaninsa, babban abinda yafi d’aga masa hankali tana sane da duka wannan ta d’auki karan tsana da tsangwama ta d’aura kan Mariyarsa bama ita kad’ai ba harda Zulfa’u da take jinjira ce a lokacin kuma ba ita ta haifo kanta a wannan rana ba, Mamani bata tsaya a nan ba tasa shima kansa ya dinga ganin laifin Mariya duk da sunan yana biyayyawa mahaifiyarsa...Shin ta ina zai soma d’aukan girman hakkin Mariya da Zulfa’u....Dole ne ya nemi waje ya keb’e shikad’ai, Mariya yau d’in cikin Farin ciki take bai kamata ya aza mata nasa damuwar ba, bayan tilin iftila’in data fuskanta a rayuwa yau d’in ta cancanci farin ciki... A daidai hanyar fita idanunsa suka sauk’a kan Lami dake sanne sannen kai tamkar tsohuwar munafuka... Idanunsu kaw suka sark’e waje guda... Duba guda Abbah yai mata ya d’auke kansa kana yai shigewarsa.... Wani irin k’ugi da cikin Lami yai da ace akwai wani gefenta tabbas da sai yaji wannan sauti... Suna murnan yau zai kansancega Mariya da ‘yaruwarta ranan tozarta ranan bak’in ciki sai gashi ya faru akansu, sai gashi ya juye ya koma kansu, ashe farin ciki mai d’orewa da aukaci burin samu a yau d’in ashe ba nasu bane, wacce suka kafa mata tarkon bak’in cikin ashe itace dai mai samun farin ciki.... Lami taji duniyar gaba d’aya tai mata d’aci...Ji tai inama ana iya maida hannun agogo baya tabbas da ta maida ta gyara kuramuren da tai, tabbas da bata biyema Haule sukai son zuciya ba... Yau wa gari ya waya...? Ita batada tsuntsu batada tarko, ko Abbah bai koreta ba bata tinanin zata iya ci gaba da zama tana fuskantar Mariya da Ma’aruf harma dashi kanshi Abban... Ita ba zuri’a ne da ita a gidan ba balle su kasance tareda ita... She’s all alone now, Tai imani Haule ta jima tana munafunatarta kenan dikda cewa tana nuna mata tare suke aikata komai, ashe tana b’oye mata wasu abubuwan... Sai yanzu ta fahimci nufin Haule na aurawa Ma’aruf d’iyarta Sahariyya Wato ita da mijinta idan Ma’aruf ya auri d’iyarsu su sun tsira ita kad’ai za’a bari a rana.... Lallai Haule ta cika makira butulu....! Tamkar kazar da aka tsamo cikin ruwan zafi haka Lami ta janye k’afufunta ta nufi nata sashen zuciyarta na mata d’aci.... Ga goggonayen Kazaure sai b’alla mata harara had’ida Allah wadar suke har Lami ta bar wajen....
Su Baffah Wada da Baffah Ado kuwa sun kasa aminta da wannan al’amari da ya bayyana kansa yau, koda ace mahaifiyarsu tsananin soyayyar Usman yasa ta rufe sirrin cewa shid’in ba d’anta bane sunaga Ya Usman ya cancanci yasan gaskiyar Al’amari yasan wacece mahaifiyarsa ko dan ya dinga isar da addu’arsa gareta, girman mahaifiya ya wuce wasa koda ace haihuwarsa kawai tai rainonsa da shayarwansa dik na wuyan Mamani amma dikda haka ya cancanci yasan asalin labarin, hakan baikai ya baiwa Mamani dama ta rufe wannan babban Sirri a gareshi ba... Ya Usman mutumin k’warai ne d’an uwa da kowa zai alfahari dashi, shid’in shine katangan family d’insu shine kuma Uba a garesu... Tsananin tausayin d’an uwan nasu ya kamasu, suna gani Baba Alhaji ya rab’a ta gefensu ya fice sim sim cikeda borin kunya... Suma d’in waje suka nufa dan gabatar da sallahn magrib suna fatan su tadda Abbah a masallaci su kuma supporting d’insa a irin wannan lokaci mai matuk’ar wahala a gareshi... Sameer da Engr ma a tare suka fice suka nufi masallaci jama’a ‘yan unguwa sai kawo masa gaisuwarsu suke suna fad’in yau ga his Excellency har unguwarsu kaikace already yaci zab’en ne sabida yanda jama’a Ke tururuwar zuwa gaidashi, har wad’nda basa zuwa wannan masallacin yau saida sukaje... Sameer kaw na taredashi sai sakin murmushi yake yanajin dad’i har k’asan zuciyarsa na kasancewarsa tareda d’an uwansa...
A cikin gida kaw banda tafasa babu abinda k’irjin Haule keyi, tabbas da za’a tsaga k’irjin Haule watak’ila aji yanda zuciyarta ke tafarfasa sabida tsananin k’unan zuciya... Ji take tamkar ta k’arasa ta shak’e Mariya da ahalinta gaba d’aya su mutu ta huta da wannan bak’in rana da take gani.... Idanunta suka sauk’a kan Yaya Abida yanda ta had’e ‘Yanuwanta gaba d’ai ta rungumesu gaba d’ai suna hawayen Farin ciki ga annashuwa da annuri da ya kasa barin fuskokinsu.... Haule tamkar zakanya haka take huci tana dubansu yanda kasan zatai tsalle ta wantsalo ta capkosu ta cinye d’aya bayan d’aya haka nan take dubansu, tamkar d’an wasan Dambe a filin kokawa haka Haule Ke bud’e hannaye tana haki tana duban bayin Allahn nan da duniyarsu ta yalwatu da Albarka... Wato Bara’atu da Abida sun cuceta sun jima suna tarwatsa duk wani shirin da take... Idanunta suka sauk’a kan Bara’atu da itace ta munafuncesu ta k’ulla aminci k’arya dasu... Tabbas sai yanzu take ganin wautansu.. (Niko nace Haule ai shi mugunta fitsarin fako ne... Kuma kece dai baki sani ba amma dik kalan asirinki da imani da ‘yan tsubbu da kikai bawa baya tab’a yiwa d’anuwasa bawa abinda Allah bai k’addara masa ba.... Asiri da sihiri gaskiya ne tinda har yai tasiri akan fiyayyen halitta babu wanda yafi k’arfin sammu ko sihiri ya kamasa saidai duk wannan zai faru ne da izinin Ubangiji... Mariya batada wani makari sai Allah data rik’a Wanda yafi k’arfin bokayanku da malaman tsubbunku... Su Haule sai a koma islamiyya a yak’i jahilci idan kinada sauran RABO)...