Sashe 139
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya Abidah taci gaba da fad’in “Wannan ne dalilin da yasa Alhaji ya tsani d’an uwansa Usman da zuri’arsa, Usman d’an uba ne a wajensu da ya d’auke soyayyar mahaifiyarsa da kuma ‘yanuwansa da suke uwa d’aya uba d’aya daga gareshi, hakan yasa yaji duk duniya baida mak’iyi kaman Usman kuma baida buri da ya wuce yaga Usman ya rayu cikin k’unci.... Mamani na hawaye a wancan lokacin taceda Alhaji taji ta gani tabbas bazata ce komai ba amma kada ya tab’a sanar da Usman wannan sirri nata domin rasa Usman na nufin rasa rayuwarta ne.... Wannan rana hankalina ya tashi sosai da jin wannan batu... Tin daga wannan rana Babu wanda yasan cewa ina bibiyan al’amran Mariya, duk wani shirin asiri da su Haule suke ina lalaltawa hakan yasa asirinsu bai tasiri akan Mariya saidai bokansu yace dasu *Abu a duhu* ba kowa yake b’atawa ba illa ni Abida .... A lokacinda aka haifi Ma’aruf nasan wad’annan azzalumai bazasu k’yale Mariya da d’anta ba tinda sun lashi takobin ganin bayansu nima sai na d’aura d’amaran wargaza dik wani shirinsu... Hakan ya hana Bokayensu ganin haske Saudi abu a duhu, wannan dalili yasa su Haule suka razana matuk’a da hidiman Mariya sukai tinanin tanada wani shirin da yafi nasu k’arfi.... Ganin bazasu daina jifarta da asiri ba yasa na yanke shawarin Bara’atu ta koma wajen Mariya da zama tinda ita Allah yayita mafad’aciya maras sanyi da tsoro ba kaman yanda Mariya ta kasance mafi sanyin hali a cikinmu ba.... Na kuma gargad’i Bara’atu cewa ta saka ido kan zaman da Mariya take a gidan mijinta da mutanen da Allah ya k’addara mata zama tare dasu....
A haka Bara’atu ta karanci Lami ta karanci duk wani wanda ke tareda Mariya... Su Lami da Haule basu daina jifar Mariya da d’anta Ma’aruf da asiri ba, dik asirin da sukai Bara’atu zata sanar dani zan kuma San hanyar da zamubi mu warware..... Kwatsam Mariya ta kuma samun ciki sannan har wannan lokaci basu daina jifarta da d’anta da muggan asirai ba, hakan yasa Bara’atu cewa anya bazamu d’auke Mariya daga wannan gida mai tarin had’ari a gareta ba dashike lokacin suna zama ne duka gida guda gidan marigayi Mahmood Mailafiya...
Duban Bara’atu nai kana Nace “Bara’atu bazamu raba Mariya da mijinta da d’anta ba ga kuma wani rabo ya kuma knno kai, mai yuwa farin cikin Mariya yana a cikin wannan ahalin ne.... Abunda zamuyi zamu b’ullo musu ta hanyar da basu tsammani bane bazamu bari suci gaba da cutar da ‘yaruwarmu da ahalinta ba.... Bara’atu tace min toh ya zamuyi Yaya ga tsohon ciki a jikin Ya Mariya kuma ko sati bamu jima da kwance k’ullin da suka bisne k’ark’ashin bola ba wanda aka linke takarda da harufan sunan Ma’aruf har sau uku dashi... Tabbas wad’annan mutane bazasu k’yaleta da d’anta ba, ga kuma wani rabon na zuwa... Ina tsoro kada a haifosa a wannan duniya mai kewaye da tarin miyagun mugaye...
Duban Bara’atu nai nace ta bani kwana biyu zansan yanda zan b’ullowa al’amarin.... Toh fah daga nan ne na tashi na tafi na samu Mamani... Sosai Mamani taji tsoro da mamakin cewa nasan sirrinta da bataso ya isa kunnen Usman har d’anta yake razaninta dashi.... Zama nai nace ta sanar dani gaskiya idan ba tanaso na tona wannan sirriga Usman ba... A haka Mamani ta sanar dani cewa Usman d’an mijinta ne marigayi, mahaifiyarsa auren zumunci akai mata da Mahmood Mailafiya, tabbas sun zuba kishi sosai a lokacinda suke tare matsayin kishiyoyo, koda aka auro mahaifiyar Usman sai Allah ya basu RABO a tare dikda cewa Mamani akwai d’anta Babba mai shekaru uku shine Alhaji.... Haka nan sukai goyon cikinsu tare tare kaman masu haifan tagwaye, wani ikon Allah wata haihuwarsu d’aya sannan Allah ya nufa suka haihu rana d’aya, toh abinka da zamanin wancan lokaci da ba damuwa da zuwa asibiti akai ba ungozoma guda ta karb’i haihuwarsu su duka biyu a gida, Allah mai yanda yaso sai ita mahaifiyar Usman Allah yai mata cikawa ya raya d’anta ita kuma Mamani Allah ya karb’i nata d’an ya kuma rayata... Allah kenan mai yin yanda yaso babu kuma wanda ya isa ya tambayesa dalili domin kaw shid’In buwayi ne gagara misali.....Ya raya wanda yaso ya kuma kashe wanda yaso... Toh nan ne Mamani ta amshi d’an Hurera data rasu ya maye gurbin nata d’an da shima ya rasu, ta shayar da Usman matsayin d’anta... Yayinda kowa yai zaton cewa Harira da d’anta gaba d’aya suka rasu... Bayan ita Ungozoma d’in data san wannan Sirri babu wanda ya sani harta Alhaji Mahmood bai sani ba, bayan wasu shekaru Ungozoma d’in taso su sanar da Alhaji Mahmood wannan batu amma fur Mamani tak’i tace Usman D’anta ne kuma babu wanda zaisan wannan Sirri akai rashin sa’a d’anta Alhaji ya lab’e yaji tattaunawarsu, Toh nan ne tsanarshiga Usman yai k’amari tinda yaji cewa ashe shid’in bama d’an mahaifiyarsu bane amma tafi fifitashi sama da sauran ‘ya’yanta sannan soyayyar da take masa har ya shafi d’ansa Ma’aruf gashi shi koda Haule ta samu cikin d’anta na fari Hafiz batai d’aukinsa ba sannan bata masa soyayyar da take wa Ma’aruf... Hakan yasa Baba Alhaji da matarsa Haule suka dad’a tsananta k’iyayyarsu kan wannan yaro Ma’aruf...
Na dubi Mamani nace nasan bakiso wannan Sirri naki ya isa ga Usman, kuma nasan kina k’aunar jikanki Ma’aruf baki k’aunar abinda zai samesa... Mamani ta jinjina min kai tace hakane... Na numfasa kad’an kana nace idan haka ne inaso mu k’ulla wani aminci na sirri.... Tace dani kaman yaya kenan...? Nace da ita inaso ki sanar da d’anki cewa lokaci yayi da zai kawar da Ma’aruf.. Kin yarda ya kawar da Ma’aruf amma da sharad’i... Sharad’in shine zai k’yale Usman da sauran zuri’arsa da zai haifa nan gaba shida iyalinsa su rayu cikin aminci...
Da mamaki Mamani ta dubeni kana tace bazata iya bari tanaji tana gani a halak’a Ma’aruf ba, zata iya basa rayuwarta... Nace da ita kaman yanda zaki iya basa rayuwarki toh haka nima zan iya basa tawa rayuwar.. Ki bar min ragamar komai nai miki alk’awari ni kuma bazan bari su salwantar da Ma’aruf ba... Zan sa yai nesa da wannan duniyar da aka jima ana farautar rayuwarsa.... INDA RAI wata rana zai kuma dawowa cikin rayuwarki bayan ya kub’uta daga sharrin wad’anann azzalumai.... Abu guda zaki min shine kisa d’anki ya yarda da sharad’in da zaki gindaya masa cewa zai k’yale Usman da sauran iyalansa su rayu cikin aminci... Kinga daga nan bamuda sauran damuwa... Ma’aruf yayi nesa dasu sannan zasu k’yale ‘yar uwata da ahalinta su rayu cikin aminci babu zullumi da d’ar d’ar d’in cutarwa...”
Sosai Mamani taci kuka jin bazata rayu tareda Ma’aruf ba amma hakan yafi mata idan har zai tsira daga sharrin Baba Alhaji wanda batada ikon magana akai sakamakon babbar makamin da yake dashi na sanin sirrinta... Na fad’a mata tin a wancan lokacin zan rufe sirrinta amma tabbas INDA RAI wataran wannan sirrin zai hak’o kanshi ya bayyana kanshi... Muka samu matsaya da Mamani akan haka, daga nan ni kuma na sami ‘yaruwata Bara’atu nace tasan yanda zatai ta sami yardarsu Haule ta nuna masu itad’in tana taredasu d’ari bisa d’ari za kuma ta taimaka masu su kawarda Ma’aruf....
Hakan kuwa akai Bara’atu ta sami su Haule ta sanar dasu tasan basu k’aunar Mariya kuma suna iayaka k’ok’arinsu ganin sun sabautar da ita da ahalinta, toh asiri dai baya tasiri akan Mariya dan Mahaifinsu yanada wani lak’ani kuma ma ita d’aya ya bayar shiyasa asiri baya kamata, shiyasa dik asirin da suke mata bokayensu Ke sanar dasu basa ganin komai saidai ABU A DUHU... Da shike Allah yaso b’atar masu da tinani sai suka yarda cewa Mariya tanada wani shiri na musamman shiyasa asirinsu bai tasiri akanta da d’anta abinda zasuyi su jefata cikin k’unci shine su kawar da Ma’aruf a doron k’asa... Hakan shine kawai zai k’untatawa Mariya... Koda su Haule suka tamabayeni maiyasa ina ‘yaruwarta zasu yarda su had’e kai da Bara’atu ta zamto Aminiyar su ta sirri sai ce masu tai sabida Mariya itace sanadiyar rugujewar ahalinsu fansa zata d’auka ma ahalinta da suka rasa ta sanadiyar Mariya... Da wannan batu su Haule suka yarda da Bara’atu... Mijin Haule ya sami Haule da batun ya bata wuk’a da nama ta kassara rayuwar Ma’aruf... Haule ta kuma jin dad’i dan ita da mijinta shafi guda suke... Bara’atu tazo ta sameni da batun su Haule suna yunk’urin kassara Ma’aruf daga nan ni kuma muka shirya yanda zamu fitar dashi cikin duniyar da ake k’aunar ganin bayansa.... Da fari mun yanke shawarin Dumba ta tafi dashi can k’asar Mali yai nesa da gida har Allah ya kawo sanda zai dawo don munyi imani INDA RAI DA RABON watarana zai kuma dawo mana...
A haka Bara’atu ta karanci Lami ta karanci duk wani wanda ke tareda Mariya... Su Lami da Haule basu daina jifar Mariya da d’anta Ma’aruf da asiri ba, dik asirin da sukai Bara’atu zata sanar dani zan kuma San hanyar da zamubi mu warware..... Kwatsam Mariya ta kuma samun ciki sannan har wannan lokaci basu daina jifarta da d’anta da muggan asirai ba, hakan yasa Bara’atu cewa anya bazamu d’auke Mariya daga wannan gida mai tarin had’ari a gareta ba dashike lokacin suna zama ne duka gida guda gidan marigayi Mahmood Mailafiya...
Duban Bara’atu nai kana Nace “Bara’atu bazamu raba Mariya da mijinta da d’anta ba ga kuma wani rabo ya kuma knno kai, mai yuwa farin cikin Mariya yana a cikin wannan ahalin ne.... Abunda zamuyi zamu b’ullo musu ta hanyar da basu tsammani bane bazamu bari suci gaba da cutar da ‘yaruwarmu da ahalinta ba.... Bara’atu tace min toh ya zamuyi Yaya ga tsohon ciki a jikin Ya Mariya kuma ko sati bamu jima da kwance k’ullin da suka bisne k’ark’ashin bola ba wanda aka linke takarda da harufan sunan Ma’aruf har sau uku dashi... Tabbas wad’annan mutane bazasu k’yaleta da d’anta ba, ga kuma wani rabon na zuwa... Ina tsoro kada a haifosa a wannan duniya mai kewaye da tarin miyagun mugaye...
Duban Bara’atu nai nace ta bani kwana biyu zansan yanda zan b’ullowa al’amarin.... Toh fah daga nan ne na tashi na tafi na samu Mamani... Sosai Mamani taji tsoro da mamakin cewa nasan sirrinta da bataso ya isa kunnen Usman har d’anta yake razaninta dashi.... Zama nai nace ta sanar dani gaskiya idan ba tanaso na tona wannan sirriga Usman ba... A haka Mamani ta sanar dani cewa Usman d’an mijinta ne marigayi, mahaifiyarsa auren zumunci akai mata da Mahmood Mailafiya, tabbas sun zuba kishi sosai a lokacinda suke tare matsayin kishiyoyo, koda aka auro mahaifiyar Usman sai Allah ya basu RABO a tare dikda cewa Mamani akwai d’anta Babba mai shekaru uku shine Alhaji.... Haka nan sukai goyon cikinsu tare tare kaman masu haifan tagwaye, wani ikon Allah wata haihuwarsu d’aya sannan Allah ya nufa suka haihu rana d’aya, toh abinka da zamanin wancan lokaci da ba damuwa da zuwa asibiti akai ba ungozoma guda ta karb’i haihuwarsu su duka biyu a gida, Allah mai yanda yaso sai ita mahaifiyar Usman Allah yai mata cikawa ya raya d’anta ita kuma Mamani Allah ya karb’i nata d’an ya kuma rayata... Allah kenan mai yin yanda yaso babu kuma wanda ya isa ya tambayesa dalili domin kaw shid’In buwayi ne gagara misali.....Ya raya wanda yaso ya kuma kashe wanda yaso... Toh nan ne Mamani ta amshi d’an Hurera data rasu ya maye gurbin nata d’an da shima ya rasu, ta shayar da Usman matsayin d’anta... Yayinda kowa yai zaton cewa Harira da d’anta gaba d’aya suka rasu... Bayan ita Ungozoma d’in data san wannan Sirri babu wanda ya sani harta Alhaji Mahmood bai sani ba, bayan wasu shekaru Ungozoma d’in taso su sanar da Alhaji Mahmood wannan batu amma fur Mamani tak’i tace Usman D’anta ne kuma babu wanda zaisan wannan Sirri akai rashin sa’a d’anta Alhaji ya lab’e yaji tattaunawarsu, Toh nan ne tsanarshiga Usman yai k’amari tinda yaji cewa ashe shid’in bama d’an mahaifiyarsu bane amma tafi fifitashi sama da sauran ‘ya’yanta sannan soyayyar da take masa har ya shafi d’ansa Ma’aruf gashi shi koda Haule ta samu cikin d’anta na fari Hafiz batai d’aukinsa ba sannan bata masa soyayyar da take wa Ma’aruf... Hakan yasa Baba Alhaji da matarsa Haule suka dad’a tsananta k’iyayyarsu kan wannan yaro Ma’aruf...
Na dubi Mamani nace nasan bakiso wannan Sirri naki ya isa ga Usman, kuma nasan kina k’aunar jikanki Ma’aruf baki k’aunar abinda zai samesa... Mamani ta jinjina min kai tace hakane... Na numfasa kad’an kana nace idan haka ne inaso mu k’ulla wani aminci na sirri.... Tace dani kaman yaya kenan...? Nace da ita inaso ki sanar da d’anki cewa lokaci yayi da zai kawar da Ma’aruf.. Kin yarda ya kawar da Ma’aruf amma da sharad’i... Sharad’in shine zai k’yale Usman da sauran zuri’arsa da zai haifa nan gaba shida iyalinsa su rayu cikin aminci...
Da mamaki Mamani ta dubeni kana tace bazata iya bari tanaji tana gani a halak’a Ma’aruf ba, zata iya basa rayuwarta... Nace da ita kaman yanda zaki iya basa rayuwarki toh haka nima zan iya basa tawa rayuwar.. Ki bar min ragamar komai nai miki alk’awari ni kuma bazan bari su salwantar da Ma’aruf ba... Zan sa yai nesa da wannan duniyar da aka jima ana farautar rayuwarsa.... INDA RAI wata rana zai kuma dawowa cikin rayuwarki bayan ya kub’uta daga sharrin wad’anann azzalumai.... Abu guda zaki min shine kisa d’anki ya yarda da sharad’in da zaki gindaya masa cewa zai k’yale Usman da sauran iyalansa su rayu cikin aminci... Kinga daga nan bamuda sauran damuwa... Ma’aruf yayi nesa dasu sannan zasu k’yale ‘yar uwata da ahalinta su rayu cikin aminci babu zullumi da d’ar d’ar d’in cutarwa...”
Sosai Mamani taci kuka jin bazata rayu tareda Ma’aruf ba amma hakan yafi mata idan har zai tsira daga sharrin Baba Alhaji wanda batada ikon magana akai sakamakon babbar makamin da yake dashi na sanin sirrinta... Na fad’a mata tin a wancan lokacin zan rufe sirrinta amma tabbas INDA RAI wataran wannan sirrin zai hak’o kanshi ya bayyana kanshi... Muka samu matsaya da Mamani akan haka, daga nan ni kuma na sami ‘yaruwata Bara’atu nace tasan yanda zatai ta sami yardarsu Haule ta nuna masu itad’in tana taredasu d’ari bisa d’ari za kuma ta taimaka masu su kawarda Ma’aruf....
Hakan kuwa akai Bara’atu ta sami su Haule ta sanar dasu tasan basu k’aunar Mariya kuma suna iayaka k’ok’arinsu ganin sun sabautar da ita da ahalinta, toh asiri dai baya tasiri akan Mariya dan Mahaifinsu yanada wani lak’ani kuma ma ita d’aya ya bayar shiyasa asiri baya kamata, shiyasa dik asirin da suke mata bokayensu Ke sanar dasu basa ganin komai saidai ABU A DUHU... Da shike Allah yaso b’atar masu da tinani sai suka yarda cewa Mariya tanada wani shiri na musamman shiyasa asirinsu bai tasiri akanta da d’anta abinda zasuyi su jefata cikin k’unci shine su kawar da Ma’aruf a doron k’asa... Hakan shine kawai zai k’untatawa Mariya... Koda su Haule suka tamabayeni maiyasa ina ‘yaruwarta zasu yarda su had’e kai da Bara’atu ta zamto Aminiyar su ta sirri sai ce masu tai sabida Mariya itace sanadiyar rugujewar ahalinsu fansa zata d’auka ma ahalinta da suka rasa ta sanadiyar Mariya... Da wannan batu su Haule suka yarda da Bara’atu... Mijin Haule ya sami Haule da batun ya bata wuk’a da nama ta kassara rayuwar Ma’aruf... Haule ta kuma jin dad’i dan ita da mijinta shafi guda suke... Bara’atu tazo ta sameni da batun su Haule suna yunk’urin kassara Ma’aruf daga nan ni kuma muka shirya yanda zamu fitar dashi cikin duniyar da ake k’aunar ganin bayansa.... Da fari mun yanke shawarin Dumba ta tafi dashi can k’asar Mali yai nesa da gida har Allah ya kawo sanda zai dawo don munyi imani INDA RAI DA RABON watarana zai kuma dawo mana...