Sashe 110
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Agogon hannunsa yake dubawa lokaci guda yake furta “Is pointless talking to you, bazaka tab’a canzawa ba Shamsu kai komai a rayuwa shiririta ka d’aukesa...” Ganin da gaske Sameer tafiya zai yasa Shamsu kamo hannunsa ya maidasa ya zaunar yana fad’in “Haba surgeon abin bai kai nan ba, kasan dai dole na tab’a haline zauna, lets talk...”
Kallon ko inkula Sameer ya aika masa sanda yake zama bisa sofar..... Zamansa yai daidai da soma kiran wayarsa, hannu yasa ya ciro wayar dake aljihun wandonsa, mamakine ya cikasa ganin mai kiran nasa...
Shamsu ya da yaga yayiwa screen d’in waya k’uri yace “Ya dai lafia....?”
Sameer yace “Kana maganar Siyama kaga ga Daddynta na kira...” Ya k’arashe maganar yana mai receiving call d’in, dikda cewa yanajin bai kyauta ba don tin bayan da Siyama ta tafi bai sanar da Daddyn komai ba....
Bayan sun gaisa cikeda mutuntawa Daddy yace “Sameer inason ganinka....”
Duban Shamsu Sameer ya d’anyi Shamsun ma Shi yake duba, jin Sameer yai shiru daga d’aya b’angaren ya sa Daddy ci gaba da fad’in “Ina Kano karka damu basai kaje Kaduna ba, ina nan Tahir kazo ka sameni...”
Harce har na had’ewa yake furta “O... Ok Daddy, zanzo yanzu in sha Allah...”
Daddy yace “Good, saikazo.....”
Datse kiran yai yana mai duban Shamsu...
Shamsu ya d’aga masa gira alamun tambaya...
Fuzar da iska kad’an yai kana yace “I’ve to go, Daddy keson ganina yana nan Kano.... Allah sa ba maganan Siyama zaimin ba don gaskiya zanji kunya tinda ni banje na sameshi ba shi ya taho ya sameni...”
“Kaima kasan bazai wuce hakan ba, bacin haka mai zaisa ya nemeka har Kano...” Shamsu yace yana mai mik’ewa tsaye shima....
Girgiza kai Sameer yake a hankali tamkar wanda yai nisa cikin tunani kana yace “I don’t know... Kaga bara naje na sameshi naji ko menene..” Ya mik’a masa hannu suka d’anyi handshake kana Shamsu yace “Shikenan Abokina sai munyi magana... Zamu had’u later idan kana hospital ne ma sai ka fad’a mun...”
“Ok until later..” Sameer yace kafin ya fice....
***
Daddy ya gyara zama sosai yana mai ci gaba da furta “Sameer, sam ban kiraka nan akan maganar matarka Siyama ba don nasan iyaka hak’uri kayi da Siyama, ni kaina shaida ne don a baya komai tayi bayanta nakebi bana considering d’inka.... Sameer kayi hak’uri ka yafeni bisa duk abubuwan da na maka baya because of my selfishness...”
Cikin sauri Sameer ya d’ago yana duban Daddyn Siyama, lokaci guda yake girgiza kai yana mai furta “No Daddy, dan Allah ka daina rok’ona gafara, baka tab’a mun komai ba ni, har kwanan gobe Uba kake min koda bani auren Siyama sabida kaid’in Abokin Daddy na ne....”
Daddy yai murmushi cikeda jin dad’i kana yace “Allah ya maka albarka Sameer...”
Sameer ya amsada Ameen a hankali, Daddy yaci gaba da fad’in “Wato Sameer abinda yasa na kiraka ba komai bane face kan maganar Khalid da k’anwarka Nabilah... Nasan kasanda batun....”
Wannan karon mamaki ne sosai ya nuna a fuskan Sameer don sam bai kawo hakan a zuciyarsa ba, baiyi zaton mak’asudin zuwan Daddyn ba kenan....Jinjina kai yayi yana mai d’aura murmushi kad’an saman fuskarsa...
Daddy ya jinjina kai yace “Alhamdulillah..” Saida ya kuma gyara zamansa kana yaci gaba da fad’in “Inaso kamin jagora wajen mahaifinka na nemawa d’ah na Khalid aurenta....”
Shiru ne ya d’an ratsa tsakani har saida Daddy yace “Akwai matsala ne....?”
Girgiza kai Sameer yai kana yace “A’a babu matsala Daddy ni zan maka jagora har wajen Abbah na, bakada matsala idan don wannan ne... A koda yaushe fatanmu shine zab’in Alkhairi...”
Daddy ya murmusa kana yace “Toh Alhamdulillah, yanzu na baka wuk’a da nama inaso kafin na bar garin nan na sami mahaifinka muyi magana ta manya, sai ka soma tuntub’arsa muji yaushe yake free, sai ya bamu rana...”
Sameer ya jinjina kai a hakali yace “Shikenan Daddy zan tuntub’esa kaman yana kace...”
Daddy yai masa godiya kafin sukai sallama Sameer ya fice.....
***
Kallon ko inkula Sameer ya aika masa sanda yake zama bisa sofar..... Zamansa yai daidai da soma kiran wayarsa, hannu yasa ya ciro wayar dake aljihun wandonsa, mamakine ya cikasa ganin mai kiran nasa...
Shamsu ya da yaga yayiwa screen d’in waya k’uri yace “Ya dai lafia....?”
Sameer yace “Kana maganar Siyama kaga ga Daddynta na kira...” Ya k’arashe maganar yana mai receiving call d’in, dikda cewa yanajin bai kyauta ba don tin bayan da Siyama ta tafi bai sanar da Daddyn komai ba....
Bayan sun gaisa cikeda mutuntawa Daddy yace “Sameer inason ganinka....”
Duban Shamsu Sameer ya d’anyi Shamsun ma Shi yake duba, jin Sameer yai shiru daga d’aya b’angaren ya sa Daddy ci gaba da fad’in “Ina Kano karka damu basai kaje Kaduna ba, ina nan Tahir kazo ka sameni...”
Harce har na had’ewa yake furta “O... Ok Daddy, zanzo yanzu in sha Allah...”
Daddy yace “Good, saikazo.....”
Datse kiran yai yana mai duban Shamsu...
Shamsu ya d’aga masa gira alamun tambaya...
Fuzar da iska kad’an yai kana yace “I’ve to go, Daddy keson ganina yana nan Kano.... Allah sa ba maganan Siyama zaimin ba don gaskiya zanji kunya tinda ni banje na sameshi ba shi ya taho ya sameni...”
“Kaima kasan bazai wuce hakan ba, bacin haka mai zaisa ya nemeka har Kano...” Shamsu yace yana mai mik’ewa tsaye shima....
Girgiza kai Sameer yake a hankali tamkar wanda yai nisa cikin tunani kana yace “I don’t know... Kaga bara naje na sameshi naji ko menene..” Ya mik’a masa hannu suka d’anyi handshake kana Shamsu yace “Shikenan Abokina sai munyi magana... Zamu had’u later idan kana hospital ne ma sai ka fad’a mun...”
“Ok until later..” Sameer yace kafin ya fice....
***
Daddy ya gyara zama sosai yana mai ci gaba da furta “Sameer, sam ban kiraka nan akan maganar matarka Siyama ba don nasan iyaka hak’uri kayi da Siyama, ni kaina shaida ne don a baya komai tayi bayanta nakebi bana considering d’inka.... Sameer kayi hak’uri ka yafeni bisa duk abubuwan da na maka baya because of my selfishness...”
Cikin sauri Sameer ya d’ago yana duban Daddyn Siyama, lokaci guda yake girgiza kai yana mai furta “No Daddy, dan Allah ka daina rok’ona gafara, baka tab’a mun komai ba ni, har kwanan gobe Uba kake min koda bani auren Siyama sabida kaid’in Abokin Daddy na ne....”
Daddy yai murmushi cikeda jin dad’i kana yace “Allah ya maka albarka Sameer...”
Sameer ya amsada Ameen a hankali, Daddy yaci gaba da fad’in “Wato Sameer abinda yasa na kiraka ba komai bane face kan maganar Khalid da k’anwarka Nabilah... Nasan kasanda batun....”
Wannan karon mamaki ne sosai ya nuna a fuskan Sameer don sam bai kawo hakan a zuciyarsa ba, baiyi zaton mak’asudin zuwan Daddyn ba kenan....Jinjina kai yayi yana mai d’aura murmushi kad’an saman fuskarsa...
Daddy ya jinjina kai yace “Alhamdulillah..” Saida ya kuma gyara zamansa kana yaci gaba da fad’in “Inaso kamin jagora wajen mahaifinka na nemawa d’ah na Khalid aurenta....”
Shiru ne ya d’an ratsa tsakani har saida Daddy yace “Akwai matsala ne....?”
Girgiza kai Sameer yai kana yace “A’a babu matsala Daddy ni zan maka jagora har wajen Abbah na, bakada matsala idan don wannan ne... A koda yaushe fatanmu shine zab’in Alkhairi...”
Daddy ya murmusa kana yace “Toh Alhamdulillah, yanzu na baka wuk’a da nama inaso kafin na bar garin nan na sami mahaifinka muyi magana ta manya, sai ka soma tuntub’arsa muji yaushe yake free, sai ya bamu rana...”
Sameer ya jinjina kai a hakali yace “Shikenan Daddy zan tuntub’esa kaman yana kace...”
Daddy yai masa godiya kafin sukai sallama Sameer ya fice.....
***