Sashe 54
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
D’ago rinannun idanunsa yai yana duban Shamsu kana ya girgiza kai yace “Not yet, ban sanar da kowa ba face kai, sannan bazan tunk’ari Alhaji Usman da batunba sai naje Kaduna na dawo, inada d’umbin tambayoyi da nakeson yima Mummy da Daddy...” Daga haka mik’ewa yayi yana mai furta “Zan wuce Kaduna yanzu In sha Allah...”
Shamsu ya mik’e cikin sauri ya take masa baya yana fad’in “Sameer are you sure you can drive...?” Yayi maganar cikeda kulawa...
K’ak’aro murmushi Sameer yai ya sakar masa kana ya jinjina kai a hankali yace “Kar ka damu abokina Insha Allah zan iya...”
Cikeda nuna damuwa Shamsu yace “Toh ko dai nai driving naka ne...?”
Nanma girgiza kai yai yana mai sakin murmushi yace “I’ll be fine Shamsu ka daina damuwa...”
Nannauyan ajiyan zuciya Shamsu ya sauk’e kana yace “Shikenan if you insist, drive safe abokina.....”
Sameer ya jinjina kai kafin suka soma sauk’owa daga benen..
Har wajen da ya aje motarsa Shamsu ya masa rakiya yana mai masa fatan sauk’a lafiya da samun nasara...
***
Idan kaga Hajiya a kwanaki biyun nan da babu Raihanah duk ta fice hayyacinta tayi wajaga wajaga, ‘ya’yanta Sahariyya da Naja’atu sam babu mai taimaka mata da aikin gida cikinsu, ga hidimar Kausar dake gabanta...
Tana zaune ta ida sanwar abincin rana ga Kausar da tun daren jiya ke kuka sabida tsananin zafin jikin da take fama dashi, da alama yarinyar batada lafiya, gaba d’aya Hajiya bata samu wadataccen barci ba ta tsaya jinyar Kausar, abin ya mata yawa kanta na neman zaucewa... Kaman wacce aka sinkaya haka ta mik’e ta sab’a Kausar a baya ta fice...
Bata zarce ko ina ba sai gidan Hafiz....
Tun bayan bikin sai yau Hajiya ta taka gidan Hafiz dukda cewa ita Sawwamar bata tab’a d’aukan k’afafu taje gaida sirakanta ba iyayen mijinta...
Hajiya bugun duniya tayi ba’a bud’e k’ofa ba ga Kausar dake sab’e a bayanta tana ci gaba da aikin kuka, sai faman jijjiga yarinyar take....
Bayan shud’ewar wasu mintoci taji ana k’ok’arin bud’e k’ofar don har ta cire rai baza’a bud’e ba ta soma neman mai adaidaita...
A yatsine Sawwama ke dubanta tana wani kanne idanu alamun tashinta kenan daga bacci....
Hajiya baki sake take duban Sawwama domin kaw babu sitirar kirki jikinta don sanye take cikin kayanta na bacci..
Ta kasa furta koda kalma guda sai duban Sawwama da take babu ko k’yafta idanu...
Banda watsa mata kallon wulak’anci Sawwama bata komai, ta lura da mamakin da ya kama Hajiya don haka ta kuma juya jikinta alamun ta kalleta da kyau kana tace “Lafiya...? Bashi ko Tara...?!” Yanda tai maganar cikeda isa da izza yasa Hajiya saurin saita kanta kana ta shiga wage baki tana yak’e tace “Baki shaidani bane...? Nice Hajiya mahaifiyar mijinki....”
Saida Sawwama ta kuma binta da wani wulak’antaccen kallon kana ta d’anyi gajeren dariya tace “Na ganeki mana, shiyasa nake tambayarki, bashi ko tara...? Idan kaw babu d’aya daga ciki uwar mai kikazo mana gida da asubahin fari.....?”
Gwiwoyin Hajiya suka sake tai k’ok’arin k’ak’aro murmushi tace “Kodai baki lura bane ai gari ya waye tuntuni azahar muke hari...”
Nanma tsuka Sawwama tai tana wani juya idanu had’ida jijjiga ita kad’ai kana tace “Toh naji gari ya waye, yanzu dai ki sanar dani mai ya kawoki....”
Hajiya da k’atutun bak’in ciki ya tokare mata mak’oshi harara ta wurgawa Sawwama sanda ta saci kallonta taga wani gefen take duba, tana maido da dubanta ga Hajiya tai saurin saita kanta tanaci gaba da murmushin yak’e wanda bahaushe ke cewa tafi kuka ciwo...
“Aidai da kin bari mun shiga daga ciki, bai kamata matar aure ta lek’o har waje haka ba....”
Dakatar da ita Sawwama tai ta hanyar d’aga hannu kana tace “A’a a’a idan wa’azi kikeso maza ki tafi bakin kasuwa ko tasha ba’a nan ba, don na tabbata wa’azinki bazai karb’u a masallaci ba balle nace kije can ki haye mumbari.... Idan kuma sa ido ne ya kawoki toh ki wanke idanunki da kyau don kinada kallo bakiga komai ba tukun.....!” Ta k’arashe cikin salo na juya idanu...
Baki sake Hajiya ke kallon ikon Allah, kalan rashin mutuncin da bata tab’a gani ba tsawon rayuwarta...
K’arasowar Hafiz wajen ne yasa Hajiya saurin sadda kanta tana mai k’ok’arin saita kanta don bataso ya gano tsantsan tashin hankalin data fad’a, gwara tai k’ok’arin shanye wulak’ancin Sawwama da dai ace ta zama loser....
Yana shafa kai yake duban Hajiyar kana ya saci kallon Sawwama...
Tsuka Sawwama tai ta shige ciki abinta tana binsa da wawan kallo...
Hafiz tamkar wanda dodonsa ya gifta Sawwama na shigewa yai saurin k’arasowa ga Hajiya yana fad’in “Hajiya sannu da zuwa, ya kika tsaya daga waje, shigo daga ciki mana....” Ya k’arashe yana bata hanya...
Kallonsa kurum Hajiya keyi tana hango kalan rama da bak’i da yayi, da ace bataima d’an nata farin sani ba tabbas da tace canzashi akai...
Hankalin Hajiya idan yayi dubu ya tashi...
Tai saurin tare Hafiz da tambaya...
“Hafiz mai ya sameka ciwo ne kayi....?” Tai maganar cikeda tsoro da fargaba...
D’an shafa kansa yai had’ida k’ak’aro murmushi kana yace “A’a Hajiya lafiyata lau mu k’arasa ciki.....” Yai maganar yana mai k’ara sauri don kar Hajiya ta kuma jefo masa wata tambayar....
Da k’yar Hajiya Haule ke iya jan k’afafunta da suka mata mugun sanyi har Hafiz ya yaye labulen parlorn suka shige....
Sawwama na hakimce saman doguwar kujera mai d’aukan mutum uku, k’afafu d’aya bisa d’aya sai faman shafa wayarta take...
Cikeda d’ari Hajiya ta soma lalumar kujera zata zauna Hafiz na fad’in “Bismillah Hajiya zauna mana...”
Kaman mai tsoron kujeran haka take k’ok’arin zama....
Aiko Sawwama kaman jira take ta tari Hajiya da fad’in “A’a a’a ina zaki zauna.... Kinga sauk’a k’asan tile ba kowani shirgi ke d’ale min kujera ba....!” Hajiya ta saki baki tana jira taga hukuncin da Hafiz zai d’auka saima kauda kai gefe dataga yayi yana sosa k’eya...
Shikenan an shanye mata d’ah...
Duban Sawwama da kyau tai wannan karon domin kaw tazo wuya...
Da ‘yar yatsa Hajiya ke nunata kana tace “Amma ke dai bakida mutunci bakida kunya... Ni zaki duba ki wulak’anta in tsuguna in haifi mijinki ki wulak’antani... Kai kuma kana tsaye kana kallo ana min cin kashi baka kikkifawa ‘yar jakar uba mari ba... Toh wllhi kunyi kad’an daga kai har ita... Bokan naki ma yayi kad’an...”
Sawwama ta katseta da fad’in “Ki sake kirata maras kunya zan nuna miki rashin kunya tsirarta don na lura har yau baki tab’a ganin rashin kunya zindir d’inta ba mai sutura kike gani...”
Hajiya ta shiga zaro idanu waje hannaye dafe da k’irji har lokacin bakinta sake yake wai donma Kausar tayi bacci a bayanta...
“Allah....! Eh lallai ikon Allah.... Kai Hafiz saketa ka rubuta saki nace banso ta k’ara ko sakan guda a gidan nan....”
Hafiz ya dubi Sawwama dake faman aika masa harara kana ya maidoda dubansaga Hajiya yace “Hajiya gaskiya kiyi hak’uri bazan iya sakin matata ba gaskiya....”
Hajiya ta dafe k’irji tana fad’in “Na shiga uku ni Haule.... Hafizu ni nake baka umarni kana cewa bazakayi ba...?” Saiga hawaye na gangarowa daga idanun Hajiya..
Jinjina mata kai Hafiz yayi yace “K’warai kuwa Hajiya idan nabi naki bazan zauna da ko wata mace a duniya ba tinda bakida aiki sai datse min igiyoyin aurena gaskiya bazan saki matata ba...” Ya k’arashe yana hura hanci...
Hajiya batasan sanda ta shiga kwance goyon Kausar ba ta dangwala masu yarinyar gabansu tana fad’in “Ga d’iyarka sai kasan gidan uwar da zaka kaita amma bani ba... Shanyayyen banza da wofi... Ke kuma mu zuba nidake, har gaban bokan naki sai kin tafi kina kuka... Haule kikeji baki santa ba...!” Daga haka saita mayafinta tai ta fice tana huci yayinda Sawwama ta saki baki tana kallon Kausar dake kuka Hafiz d’inma Hajiya yabi da kallo har ta fice ga kukan Kausar da ya gauraye gidan gaba d’aya...
“Kaga ka tsayar da ita ka bata yarinyar nan don wllhi bazan iya raino ba kaima ka sani, ba a gidan nan ba wllhi....!” Daga haka sa kai tai ta shige d’aki kaman zata tashi sama...
Jiki a sanyaye Hafiz ya duk’a ya d’auki d’iyarsa ya aza a kafad’a yana jijjigata a hankali wasu irin tunani da wani abu mai kamada tausayi na yawo a kwanyarsa amma shi kansa bazai iya cewa ga abinda yakeji ba....
Har Hajiya ta shigo gida bata daina ashariya tana dannawa Sawwama da uwarta Magajiya tsinuwa ba... Sahariyya da Najah suka kalli juna lokaci guda suka shek’e da dariya don dama sunsan hakan zata faru idan dai Sawwama ce...
Hajiya ta wurga masu harara tana jifa da mayafinta take fad’in “Ku kuma fah uban mai ya baku dariya....?”
Suka kuma tintsirewa da dariya..
Hajiya tai k’wafa tace “Aikin banza aikin wofi kuma kuji na fad’a maku wllhi dole ku shiga kitchen ku girka abinci na gaji da bautan ‘ya’yan da ba gani suke ba... Duk fad’i tashin nan kanku nake amma yau wai Hafiz na gani aka d’ibemin albarka wanda tinda uwata ta haifeni ba’a tab’a min irinta ba ya kasa tab’uka komai.. Ohni Haule na shiga uku....!” Ta k’arashe tana mai kamo bakin zaninta tana share hawayen dake zubo mata...
Sahariyya ta tab’e baki ta shige d’aki tana fad’in “Wllhi idan za’a mutu a gidan nan bazanyi girki ba...”
Najah ma tab’e bakin tai tace “Nidai Allah ya gani karatu nake bazan iya aikatau d’in gidan nan ba...” Ta k’arashe tana mai ficewa waje...
Hajiya tabi d’iyoyin nata da kallo had’ida kurma sabon kuka tana furta ta shiga uku....
***
Suna zaune a lambun dake bayan d’akin Abbah a asibitin suna tartaunawa irinta uwa da d’iya wanda suka jima basuyi ba...
Mamy ta kuma kamo hannayen Zulfa’u tace “Kar ki damu In sha Allahu zamu ceto rayuwar Kausar daga hannun wad’annan azzalumai, duk yanda zamuyi In sha Allah rik’on Kausar zai dawo hannunmu kinji koh, ki kwantar da hankalinki...”
Zulfah ta k’ak’aro murmushi tana mai jinjina kai tace “Toh Mamyna... Allah ya k’addara faruwan hakan...”
Mamy ta amsa da Ameen a daidai lokacinda Aunty Lami ta k’araso wajen tana sakin murmushin da iyakacinta fatar baki....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*44*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
KADUNA
Shamsu ya mik’e cikin sauri ya take masa baya yana fad’in “Sameer are you sure you can drive...?” Yayi maganar cikeda kulawa...
K’ak’aro murmushi Sameer yai ya sakar masa kana ya jinjina kai a hankali yace “Kar ka damu abokina Insha Allah zan iya...”
Cikeda nuna damuwa Shamsu yace “Toh ko dai nai driving naka ne...?”
Nanma girgiza kai yai yana mai sakin murmushi yace “I’ll be fine Shamsu ka daina damuwa...”
Nannauyan ajiyan zuciya Shamsu ya sauk’e kana yace “Shikenan if you insist, drive safe abokina.....”
Sameer ya jinjina kai kafin suka soma sauk’owa daga benen..
Har wajen da ya aje motarsa Shamsu ya masa rakiya yana mai masa fatan sauk’a lafiya da samun nasara...
***
Idan kaga Hajiya a kwanaki biyun nan da babu Raihanah duk ta fice hayyacinta tayi wajaga wajaga, ‘ya’yanta Sahariyya da Naja’atu sam babu mai taimaka mata da aikin gida cikinsu, ga hidimar Kausar dake gabanta...
Tana zaune ta ida sanwar abincin rana ga Kausar da tun daren jiya ke kuka sabida tsananin zafin jikin da take fama dashi, da alama yarinyar batada lafiya, gaba d’aya Hajiya bata samu wadataccen barci ba ta tsaya jinyar Kausar, abin ya mata yawa kanta na neman zaucewa... Kaman wacce aka sinkaya haka ta mik’e ta sab’a Kausar a baya ta fice...
Bata zarce ko ina ba sai gidan Hafiz....
Tun bayan bikin sai yau Hajiya ta taka gidan Hafiz dukda cewa ita Sawwamar bata tab’a d’aukan k’afafu taje gaida sirakanta ba iyayen mijinta...
Hajiya bugun duniya tayi ba’a bud’e k’ofa ba ga Kausar dake sab’e a bayanta tana ci gaba da aikin kuka, sai faman jijjiga yarinyar take....
Bayan shud’ewar wasu mintoci taji ana k’ok’arin bud’e k’ofar don har ta cire rai baza’a bud’e ba ta soma neman mai adaidaita...
A yatsine Sawwama ke dubanta tana wani kanne idanu alamun tashinta kenan daga bacci....
Hajiya baki sake take duban Sawwama domin kaw babu sitirar kirki jikinta don sanye take cikin kayanta na bacci..
Ta kasa furta koda kalma guda sai duban Sawwama da take babu ko k’yafta idanu...
Banda watsa mata kallon wulak’anci Sawwama bata komai, ta lura da mamakin da ya kama Hajiya don haka ta kuma juya jikinta alamun ta kalleta da kyau kana tace “Lafiya...? Bashi ko Tara...?!” Yanda tai maganar cikeda isa da izza yasa Hajiya saurin saita kanta kana ta shiga wage baki tana yak’e tace “Baki shaidani bane...? Nice Hajiya mahaifiyar mijinki....”
Saida Sawwama ta kuma binta da wani wulak’antaccen kallon kana ta d’anyi gajeren dariya tace “Na ganeki mana, shiyasa nake tambayarki, bashi ko tara...? Idan kaw babu d’aya daga ciki uwar mai kikazo mana gida da asubahin fari.....?”
Gwiwoyin Hajiya suka sake tai k’ok’arin k’ak’aro murmushi tace “Kodai baki lura bane ai gari ya waye tuntuni azahar muke hari...”
Nanma tsuka Sawwama tai tana wani juya idanu had’ida jijjiga ita kad’ai kana tace “Toh naji gari ya waye, yanzu dai ki sanar dani mai ya kawoki....”
Hajiya da k’atutun bak’in ciki ya tokare mata mak’oshi harara ta wurgawa Sawwama sanda ta saci kallonta taga wani gefen take duba, tana maido da dubanta ga Hajiya tai saurin saita kanta tanaci gaba da murmushin yak’e wanda bahaushe ke cewa tafi kuka ciwo...
“Aidai da kin bari mun shiga daga ciki, bai kamata matar aure ta lek’o har waje haka ba....”
Dakatar da ita Sawwama tai ta hanyar d’aga hannu kana tace “A’a a’a idan wa’azi kikeso maza ki tafi bakin kasuwa ko tasha ba’a nan ba, don na tabbata wa’azinki bazai karb’u a masallaci ba balle nace kije can ki haye mumbari.... Idan kuma sa ido ne ya kawoki toh ki wanke idanunki da kyau don kinada kallo bakiga komai ba tukun.....!” Ta k’arashe cikin salo na juya idanu...
Baki sake Hajiya ke kallon ikon Allah, kalan rashin mutuncin da bata tab’a gani ba tsawon rayuwarta...
K’arasowar Hafiz wajen ne yasa Hajiya saurin sadda kanta tana mai k’ok’arin saita kanta don bataso ya gano tsantsan tashin hankalin data fad’a, gwara tai k’ok’arin shanye wulak’ancin Sawwama da dai ace ta zama loser....
Yana shafa kai yake duban Hajiyar kana ya saci kallon Sawwama...
Tsuka Sawwama tai ta shige ciki abinta tana binsa da wawan kallo...
Hafiz tamkar wanda dodonsa ya gifta Sawwama na shigewa yai saurin k’arasowa ga Hajiya yana fad’in “Hajiya sannu da zuwa, ya kika tsaya daga waje, shigo daga ciki mana....” Ya k’arashe yana bata hanya...
Kallonsa kurum Hajiya keyi tana hango kalan rama da bak’i da yayi, da ace bataima d’an nata farin sani ba tabbas da tace canzashi akai...
Hankalin Hajiya idan yayi dubu ya tashi...
Tai saurin tare Hafiz da tambaya...
“Hafiz mai ya sameka ciwo ne kayi....?” Tai maganar cikeda tsoro da fargaba...
D’an shafa kansa yai had’ida k’ak’aro murmushi kana yace “A’a Hajiya lafiyata lau mu k’arasa ciki.....” Yai maganar yana mai k’ara sauri don kar Hajiya ta kuma jefo masa wata tambayar....
Da k’yar Hajiya Haule ke iya jan k’afafunta da suka mata mugun sanyi har Hafiz ya yaye labulen parlorn suka shige....
Sawwama na hakimce saman doguwar kujera mai d’aukan mutum uku, k’afafu d’aya bisa d’aya sai faman shafa wayarta take...
Cikeda d’ari Hajiya ta soma lalumar kujera zata zauna Hafiz na fad’in “Bismillah Hajiya zauna mana...”
Kaman mai tsoron kujeran haka take k’ok’arin zama....
Aiko Sawwama kaman jira take ta tari Hajiya da fad’in “A’a a’a ina zaki zauna.... Kinga sauk’a k’asan tile ba kowani shirgi ke d’ale min kujera ba....!” Hajiya ta saki baki tana jira taga hukuncin da Hafiz zai d’auka saima kauda kai gefe dataga yayi yana sosa k’eya...
Shikenan an shanye mata d’ah...
Duban Sawwama da kyau tai wannan karon domin kaw tazo wuya...
Da ‘yar yatsa Hajiya ke nunata kana tace “Amma ke dai bakida mutunci bakida kunya... Ni zaki duba ki wulak’anta in tsuguna in haifi mijinki ki wulak’antani... Kai kuma kana tsaye kana kallo ana min cin kashi baka kikkifawa ‘yar jakar uba mari ba... Toh wllhi kunyi kad’an daga kai har ita... Bokan naki ma yayi kad’an...”
Sawwama ta katseta da fad’in “Ki sake kirata maras kunya zan nuna miki rashin kunya tsirarta don na lura har yau baki tab’a ganin rashin kunya zindir d’inta ba mai sutura kike gani...”
Hajiya ta shiga zaro idanu waje hannaye dafe da k’irji har lokacin bakinta sake yake wai donma Kausar tayi bacci a bayanta...
“Allah....! Eh lallai ikon Allah.... Kai Hafiz saketa ka rubuta saki nace banso ta k’ara ko sakan guda a gidan nan....”
Hafiz ya dubi Sawwama dake faman aika masa harara kana ya maidoda dubansaga Hajiya yace “Hajiya gaskiya kiyi hak’uri bazan iya sakin matata ba gaskiya....”
Hajiya ta dafe k’irji tana fad’in “Na shiga uku ni Haule.... Hafizu ni nake baka umarni kana cewa bazakayi ba...?” Saiga hawaye na gangarowa daga idanun Hajiya..
Jinjina mata kai Hafiz yayi yace “K’warai kuwa Hajiya idan nabi naki bazan zauna da ko wata mace a duniya ba tinda bakida aiki sai datse min igiyoyin aurena gaskiya bazan saki matata ba...” Ya k’arashe yana hura hanci...
Hajiya batasan sanda ta shiga kwance goyon Kausar ba ta dangwala masu yarinyar gabansu tana fad’in “Ga d’iyarka sai kasan gidan uwar da zaka kaita amma bani ba... Shanyayyen banza da wofi... Ke kuma mu zuba nidake, har gaban bokan naki sai kin tafi kina kuka... Haule kikeji baki santa ba...!” Daga haka saita mayafinta tai ta fice tana huci yayinda Sawwama ta saki baki tana kallon Kausar dake kuka Hafiz d’inma Hajiya yabi da kallo har ta fice ga kukan Kausar da ya gauraye gidan gaba d’aya...
“Kaga ka tsayar da ita ka bata yarinyar nan don wllhi bazan iya raino ba kaima ka sani, ba a gidan nan ba wllhi....!” Daga haka sa kai tai ta shige d’aki kaman zata tashi sama...
Jiki a sanyaye Hafiz ya duk’a ya d’auki d’iyarsa ya aza a kafad’a yana jijjigata a hankali wasu irin tunani da wani abu mai kamada tausayi na yawo a kwanyarsa amma shi kansa bazai iya cewa ga abinda yakeji ba....
Har Hajiya ta shigo gida bata daina ashariya tana dannawa Sawwama da uwarta Magajiya tsinuwa ba... Sahariyya da Najah suka kalli juna lokaci guda suka shek’e da dariya don dama sunsan hakan zata faru idan dai Sawwama ce...
Hajiya ta wurga masu harara tana jifa da mayafinta take fad’in “Ku kuma fah uban mai ya baku dariya....?”
Suka kuma tintsirewa da dariya..
Hajiya tai k’wafa tace “Aikin banza aikin wofi kuma kuji na fad’a maku wllhi dole ku shiga kitchen ku girka abinci na gaji da bautan ‘ya’yan da ba gani suke ba... Duk fad’i tashin nan kanku nake amma yau wai Hafiz na gani aka d’ibemin albarka wanda tinda uwata ta haifeni ba’a tab’a min irinta ba ya kasa tab’uka komai.. Ohni Haule na shiga uku....!” Ta k’arashe tana mai kamo bakin zaninta tana share hawayen dake zubo mata...
Sahariyya ta tab’e baki ta shige d’aki tana fad’in “Wllhi idan za’a mutu a gidan nan bazanyi girki ba...”
Najah ma tab’e bakin tai tace “Nidai Allah ya gani karatu nake bazan iya aikatau d’in gidan nan ba...” Ta k’arashe tana mai ficewa waje...
Hajiya tabi d’iyoyin nata da kallo had’ida kurma sabon kuka tana furta ta shiga uku....
***
Suna zaune a lambun dake bayan d’akin Abbah a asibitin suna tartaunawa irinta uwa da d’iya wanda suka jima basuyi ba...
Mamy ta kuma kamo hannayen Zulfa’u tace “Kar ki damu In sha Allahu zamu ceto rayuwar Kausar daga hannun wad’annan azzalumai, duk yanda zamuyi In sha Allah rik’on Kausar zai dawo hannunmu kinji koh, ki kwantar da hankalinki...”
Zulfah ta k’ak’aro murmushi tana mai jinjina kai tace “Toh Mamyna... Allah ya k’addara faruwan hakan...”
Mamy ta amsa da Ameen a daidai lokacinda Aunty Lami ta k’araso wajen tana sakin murmushin da iyakacinta fatar baki....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*44*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
KADUNA