Sashe 155
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haule ta saki tukunya tana gyara d’aurin zani had’ida murje idanunta alamun tabbatarwa... Eh da gaske dai Raihanah take gani tarda Ma’aruf ba mafarki bane...
Sameer ya d’anyi gyaran murya kad’an kana yace “Kina mamaki ne...?”
Haule ta kuma matsowa kad’an tana nunasu da yatsa dan tama kasa furta koda kalma.... Lokaci guda labb’anta dake tsananin b’ari taji suna furta “Al... Alhaji... Alhaji fito kaga kayan al’ajabi... Ashe ga makirar da k’aninka ya aurawa d’ansa....!” Ta k’arashe tana kuma kururwa had’ida dannawa Baba Alhaji kira... A fusace ya fito Magajiya na biyedashi tana sanye cikin kayan bacci ‘yar kanti mai tsantsi ta d’aura zani sama sai wane yamutse fuska take alamun bata jima da tashuwa ba, Sai narkewa cikin jikinsa ake tana fad’in “Dalin Dalin dan Allah kaiwa matarka magana wllhi fitinarta Ke tadamu a gidan nan, sai taita biyewa yaran nan suna kokawa da farar safiya, kuma fad’ar bai wuce kan abinci, gaskiya Nidai Dalin Dalin ka taka mata birki kasan banson hayaniya..” Ta k’arashe tana narkewa cikin jikinsa ... Shiko Baba Alhaji tuni ya soma hura hanci yana fad’in “Wai ke Haule shikenan garin Allah na wayewa kinyi da kowa ken....!” Aya ya sakawa kalaman nasa sakamakon hangosu da yai tsaye tsakar gidan....
Haule kaw k’ek’ashe da idanu take duban Magajiya sai faman huci take, alla alla take dare tai Baba Alhaji ya bar d’akin Magajiya kaman yanda Shari’a ya tanada, ko banza wani k’uncin zai ragu mata... Lokaci guda Haule Ke fad’in “Ka nad’e a d’aki ana d’irka maka tsiddabaru kai a dole ga mai Amarya.... Toh sai ka fito ka ganema idanunka, an nad’e d’iyarka ma da sunan Amarya... Ka ganta nan... Ko kunya tana mak’ale jikinsa ta nuna mana ita cikakkiya ce.....!” Ta k’arashe tana hura hanci....
Raihanah da tuni k’walla sun ciko idanunta cikin sauri ta fuzge hannunta cikin na Sameer ta duk’a da saurin gaske tana k’ok’arin gaidasu saidai gaba d’aya ma kasa furta komai tai sabida kuka da yazo bakinta gadan gadan.... Sameer kaw da tsananin mamaki yake duban Haule, ko kunyar idanunsa bayan dik abubuwan da tai masu shida mahaifansa da ‘yar uwarsa Zulfa’u bataji ba.... Bai ida mamaki ba saida ya sinkayo muryan Baba Alhaji yana huci yake fad’in “K’yale ja’ira munafuka... Kina jina sai ya sakeki dan wannan aure bai d’auru ba dan dama Usman mutunci na yai niyyan ci....” Ya maido da dubansaga Sameer dake faman binsa da kallon mamaki kana yace “Kai kuma sai ka sakar min d’iya dan ba ita nayi niyyan baka ba, idan baka sakar min d’iya yanzu cikin salama a cikin gidan nan ba zaka amsa sammaci a kotu... Daga kai har Manu Billahillazi k’ararku zanyi....”
Sahariyya ta shiga doka tsalle tana murna Sameer zai saki Raihanah dan ko bata sameshi ba ta gwammaci dukansu su rasa da dai ace harma Wai Raihanah ce matar tasa....
Haule ta jinjjna kai tace “Ahtoh sai muji Uban da ya basu dama su aurar da yarinyar da ba tasu ba... Munafuka jibi yanda take mannewa cikin jikinsa kaman wata mage tana san san da kai na minafinci....”
A kufule Baba Alhaji yayo kanta yana furta “Zaki tashi Ki wuce ciki ne ko sai na jibgeki... Ja’irar banza.....!”
A d’imauce ta yunk’ura ta tashi tana k’ok’arin nufa d’akinsu saiji tai gam Sameer ya rik’o hannunta cikin nasa, idanunta masu zuban hawaye ta d’ago tana dubansa, ga tsananin mamakinta wane irin yanayi taga fuskan nasa ciki wanda zatai rantsuwa bata tab’a ganinsa cikin irin yanayin ba....
Haule ta wani zabura ita kad’ai tana duban yanda Sameer ya hana Raihana shigewa zuwa garesu... Shi kanshi Baba Alhaji da tsananin mamaki yake duban Sameer d’in... Lokaci guda yake furta “Eh lallai na yarda bakada mutunci baka gada ba... Sakar min d’iya dan ba kai ka haifa min ita ba, ba kuma ubanda ya aura maka bane ya haifa min ita... Sakarta nace....!”
Ga tsananin mamakinsa muryar Sameer ya sinkayo cikin wane irin dakewa yana furta “Babu yanda zata shige..!!!!” Yai maganar cikin tsananin tsimewa, had’ida rik’o hannunta...
Gaba d’aya suka zuba masa ta mujiya... Saida ya tabbata dik shi suke duba fuskokinsu cikeda tsoro kana Sameer yaci gaba da magana cikin tsimewa “Dama sallama mukazo muyi maku.... And to make sure bamu tafi da hakkokinmu akanku ba, amma ga dikkan alamu bakuda buk’atan hakan... Mun barku lafiya... Shige muje...!” Ya k’arashe yana mai janyo hannun Raihanah da har lokacin jikinta bai daina rawa ba...
Haule ta soma sallalami tana fad’in “Eh lallai kin cika Raihanah da har zaki zab’i namiji samada mahaifinki... Kin rik’a kin cika tabbataciya.....”
Maganganun Haule ya kuma sanya Raihanah fashewa da sabon kuka ta shiga k’ok’arin k’watan hannunta daga cikin nasa, amma saidai sam Sameer d’in yak’i sakinta saima damk’e hannun da yai sosai yana aikama Haule wani irin mugun kallon tsana da k’yama ya tina dik kalan abubuwa da Haule dasu Baba Alhaji suka masa shida Mamynsa harmada Abbah... Sai faman tururi kurum yake yana duban Haule da idanuniyansa da suka kad’a sukai jazir, ko sauraron Raihanah dake matuk’ar kuka tana fad’in “Ya Ma’aruf kai hak’uri ka barni naima Abbah biyayya na rok’i arzikinka... Shid’in magaifina ne...!!” Sam bai iya sauraronta saima ci gaba da duban Haule da yake cikin matuk’ar b’acin rai, kai kace sai taking out dik wani b’acin ran da ya shiga da k’unci a baya akan Haule.... Su Sahariyya sai murna ake Haule ma sai jijjiga take tana ayyanawa cikin zuciyarta cewa ko babu komai bazata tashi a 2 zero ba idan bataci wani yak’in ba taci wani, ko Babu komai idan ta murk’ushe auren Raihanah da Sameer yanzu a nan wani buri nata ya cika... Bata ankara ba sai ganin Magajiya tai ta tako gaban Baba Alhaji, lokaci guda Magajiya Ke dubansa, murmushi ta saki had’ida langab’e kai kad’an “Haba Alhajina... ‘Ya’ya dai duka naka ne, kuma ko shakka babu abun kunya ne dai kun riga kun tapkashi, mai sunan duk wannan borin da kake na cewa sai ya sakar maka d’iya...? Kokuwa rik’on saikainan kashin da kayiwa d’iyarka kakewa borin kunya kake cewa a saketa....?”
Baba Alhaji ya kasa furta komai sai muzurai... Haule tai karaf tace “Toh ke kuma uban wa ya kasa dake da zaki d’auka...?”
Murmusawa Magajiya tai kad’an kana ta dubi Baba Alhaji tace “Da kai nake Alhaji na...?”
Cikeda borin kunya ya soma fad’in “Toh ai toh ai fin k’arfi aka nuna min kan d’iyata.....”
Daidai nan Sameer ya k’araso gaban Baba Alhaji murya a shak’e wanda dagaji kasan maganar fita masa kurum yake, lokaci guda yake furta “Bayan dik abubuwan saka min, bayan duk abubuwan da kaima iyayena... And especially my father... Na yafe maka, kuma ina rok’on Allah ya yafe maka.... Amma kar kace na saki matata dan bani na zab’awa kaina ita ba sannan itama ba ita ta zab’eni ba, Allah shi yai hukuncinsa akanmu... Ina kuma fata hakan ya zama wa’azi a gareku akida matarka Hajiya Haule...!”Ya k’arashe siririyar hawaye wanda da gani na tafasan zuciya ne tana gangaro masa.... Gaba d’aya k’uri suka masa jikkuna a sanyaye...
Raihanah ta duk’a tana hawaye, lokaci guda take furta “Baba...! Baba..!!” Kuka yaci k’arfinta... Wajen yai shiru bakajin komai sai sautin kukan Raihanah, ga tsananin mamakin Haule sai gani tai Baba Alhaji ya dafa kan Raihanah, cikin murya mai tsananin rawa yake furta “Ki tafi tareda mijinki.... Ki tafi tareda mijinki.... Tashi kije..!!” Abubuwan da yake iya furtawa kenan...
Raihanah ta d’ago tanai masa duban mamaki... Baba Alhaji yaci gaba da jinjina kai yana furta “Ki tafi tareda mijinki...!!!” Yana ida fad’in haka ya juya ya nufi d’aki cikin sauri tamkar mai shirin kuka...
Tuni Sameer yasa hannayensa duka biyu ya d’agota... Cikin b’angaren jikinsa yai mata masauk’i yana mai share mata hawayen fuskarta... Sahariyya ta d’aura Duka hannayenta biyu aka tana furta “Na shiga uku Hajiya kina gani kuwa....? Shegiya k’onenniyar nan ce fah Wai matar tasa... Hajiya karki barta tabisa... Mutuwa zanyi...!!” Ta k’arashe tana kururwa...
Ko takansu Sameer bai kuma bi ba ya janyo hannun matarsa suka nufi k’ofa...
‘Yandaudu suka saki tafi suna yaba dacewa dasu Raihanah da Sameer sukaida juna... Yayinda Magajiya ta saki gud’a tana taya ‘yandaudunta kod’a Raihanah da Sameer....
Haule kam mutuwar tsaye tai a wajen tamkar wata gunki ta kasa yarda Baba Alhaji ya gwaleta irin haka... Ta bud’e murya yana fad’in “Alhaji barin Raihan kai ta tafi... Shikenan ka yarda ka sallamarta ma abokan gabanka.....? Na shiga uku ni Haule....!!!”
Sahariyya kaw tukunyar dake faman tafasa da ruwan zafi ta nufa ta d’auko a guje tabi bayan su Raihanah tana furta “Wllhi yau sai na k’arasa k’onaki mai gaba d’aya kowa ya huta... Saidai a daidai hanyar fita suka kusan yin karo da Hafiz da baisan tana zuwa ba aiko nan ruwan ya dawo kanta ya kware mata... Ta shiga talewa tana ihu tana tsalle had’ida birgima a wajen... Hafiz kaw ko d’auki bai k’ok’arin kawo mata ba sai matsawa gefe da yai yana kallon yanda take birgima a k’asa tana ihu sabida zafin k’unan dake ratsata... Murmushi ya saki kana yace “Alhamdulillah yau kinji azaban irin abinda kikawa d’iyata Khausar.... Allah shi k’ara...!” Daga haka yasa kai ya kutsa cikin gidan yanda ya tadda ‘yandaudu sunyi chaa wa mahaifiyarsa sun d’aura mata tukunyar tuwo aka suna rawa suna zagayeta Haule kaw sai cazgan kuka take har abin tausai.... Hafiz yai kansu a haukace tamkar sabon kamu.... Nan suke sanar dashi uwarsu Magajiya taima rashin arziki shisa suke ladabta ta dan dama Magajiya bata koda sa’insa da Haule saidai ta saka sojojinta ‘yandaudu su handling mata Haule... A d’ari Hafiz ya nufi d’akin Mahaifinsa yana fad’in ko ya saki Magajiya ko shi yaje ya saki Sawwama... Magajiya ta mik’e tana wuraga masa harara... “K’aramin maras kunya, ai bari kaji na fad’a maka zuri’armu sun zama d’aya billahillazi mutuwa ce zata rabamu... Uwarka kuma idan tana son zama lafiya toh tabi umarni na....”
Hafiz yakai dubansa ga mahaifinsa da ya kasa furta komai sai duba daga gefe.... Girgiza kai kurum Hafiz yai cikeda takaici kana ya fice a gidan tamkar zai kifa k’asa....
Sameer ya d’anyi gyaran murya kad’an kana yace “Kina mamaki ne...?”
Haule ta kuma matsowa kad’an tana nunasu da yatsa dan tama kasa furta koda kalma.... Lokaci guda labb’anta dake tsananin b’ari taji suna furta “Al... Alhaji... Alhaji fito kaga kayan al’ajabi... Ashe ga makirar da k’aninka ya aurawa d’ansa....!” Ta k’arashe tana kuma kururwa had’ida dannawa Baba Alhaji kira... A fusace ya fito Magajiya na biyedashi tana sanye cikin kayan bacci ‘yar kanti mai tsantsi ta d’aura zani sama sai wane yamutse fuska take alamun bata jima da tashuwa ba, Sai narkewa cikin jikinsa ake tana fad’in “Dalin Dalin dan Allah kaiwa matarka magana wllhi fitinarta Ke tadamu a gidan nan, sai taita biyewa yaran nan suna kokawa da farar safiya, kuma fad’ar bai wuce kan abinci, gaskiya Nidai Dalin Dalin ka taka mata birki kasan banson hayaniya..” Ta k’arashe tana narkewa cikin jikinsa ... Shiko Baba Alhaji tuni ya soma hura hanci yana fad’in “Wai ke Haule shikenan garin Allah na wayewa kinyi da kowa ken....!” Aya ya sakawa kalaman nasa sakamakon hangosu da yai tsaye tsakar gidan....
Haule kaw k’ek’ashe da idanu take duban Magajiya sai faman huci take, alla alla take dare tai Baba Alhaji ya bar d’akin Magajiya kaman yanda Shari’a ya tanada, ko banza wani k’uncin zai ragu mata... Lokaci guda Haule Ke fad’in “Ka nad’e a d’aki ana d’irka maka tsiddabaru kai a dole ga mai Amarya.... Toh sai ka fito ka ganema idanunka, an nad’e d’iyarka ma da sunan Amarya... Ka ganta nan... Ko kunya tana mak’ale jikinsa ta nuna mana ita cikakkiya ce.....!” Ta k’arashe tana hura hanci....
Raihanah da tuni k’walla sun ciko idanunta cikin sauri ta fuzge hannunta cikin na Sameer ta duk’a da saurin gaske tana k’ok’arin gaidasu saidai gaba d’aya ma kasa furta komai tai sabida kuka da yazo bakinta gadan gadan.... Sameer kaw da tsananin mamaki yake duban Haule, ko kunyar idanunsa bayan dik abubuwan da tai masu shida mahaifansa da ‘yar uwarsa Zulfa’u bataji ba.... Bai ida mamaki ba saida ya sinkayo muryan Baba Alhaji yana huci yake fad’in “K’yale ja’ira munafuka... Kina jina sai ya sakeki dan wannan aure bai d’auru ba dan dama Usman mutunci na yai niyyan ci....” Ya maido da dubansaga Sameer dake faman binsa da kallon mamaki kana yace “Kai kuma sai ka sakar min d’iya dan ba ita nayi niyyan baka ba, idan baka sakar min d’iya yanzu cikin salama a cikin gidan nan ba zaka amsa sammaci a kotu... Daga kai har Manu Billahillazi k’ararku zanyi....”
Sahariyya ta shiga doka tsalle tana murna Sameer zai saki Raihanah dan ko bata sameshi ba ta gwammaci dukansu su rasa da dai ace harma Wai Raihanah ce matar tasa....
Haule ta jinjjna kai tace “Ahtoh sai muji Uban da ya basu dama su aurar da yarinyar da ba tasu ba... Munafuka jibi yanda take mannewa cikin jikinsa kaman wata mage tana san san da kai na minafinci....”
A kufule Baba Alhaji yayo kanta yana furta “Zaki tashi Ki wuce ciki ne ko sai na jibgeki... Ja’irar banza.....!”
A d’imauce ta yunk’ura ta tashi tana k’ok’arin nufa d’akinsu saiji tai gam Sameer ya rik’o hannunta cikin nasa, idanunta masu zuban hawaye ta d’ago tana dubansa, ga tsananin mamakinta wane irin yanayi taga fuskan nasa ciki wanda zatai rantsuwa bata tab’a ganinsa cikin irin yanayin ba....
Haule ta wani zabura ita kad’ai tana duban yanda Sameer ya hana Raihana shigewa zuwa garesu... Shi kanshi Baba Alhaji da tsananin mamaki yake duban Sameer d’in... Lokaci guda yake furta “Eh lallai na yarda bakada mutunci baka gada ba... Sakar min d’iya dan ba kai ka haifa min ita ba, ba kuma ubanda ya aura maka bane ya haifa min ita... Sakarta nace....!”
Ga tsananin mamakinsa muryar Sameer ya sinkayo cikin wane irin dakewa yana furta “Babu yanda zata shige..!!!!” Yai maganar cikin tsananin tsimewa, had’ida rik’o hannunta...
Gaba d’aya suka zuba masa ta mujiya... Saida ya tabbata dik shi suke duba fuskokinsu cikeda tsoro kana Sameer yaci gaba da magana cikin tsimewa “Dama sallama mukazo muyi maku.... And to make sure bamu tafi da hakkokinmu akanku ba, amma ga dikkan alamu bakuda buk’atan hakan... Mun barku lafiya... Shige muje...!” Ya k’arashe yana mai janyo hannun Raihanah da har lokacin jikinta bai daina rawa ba...
Haule ta soma sallalami tana fad’in “Eh lallai kin cika Raihanah da har zaki zab’i namiji samada mahaifinki... Kin rik’a kin cika tabbataciya.....”
Maganganun Haule ya kuma sanya Raihanah fashewa da sabon kuka ta shiga k’ok’arin k’watan hannunta daga cikin nasa, amma saidai sam Sameer d’in yak’i sakinta saima damk’e hannun da yai sosai yana aikama Haule wani irin mugun kallon tsana da k’yama ya tina dik kalan abubuwa da Haule dasu Baba Alhaji suka masa shida Mamynsa harmada Abbah... Sai faman tururi kurum yake yana duban Haule da idanuniyansa da suka kad’a sukai jazir, ko sauraron Raihanah dake matuk’ar kuka tana fad’in “Ya Ma’aruf kai hak’uri ka barni naima Abbah biyayya na rok’i arzikinka... Shid’in magaifina ne...!!” Sam bai iya sauraronta saima ci gaba da duban Haule da yake cikin matuk’ar b’acin rai, kai kace sai taking out dik wani b’acin ran da ya shiga da k’unci a baya akan Haule.... Su Sahariyya sai murna ake Haule ma sai jijjiga take tana ayyanawa cikin zuciyarta cewa ko babu komai bazata tashi a 2 zero ba idan bataci wani yak’in ba taci wani, ko Babu komai idan ta murk’ushe auren Raihanah da Sameer yanzu a nan wani buri nata ya cika... Bata ankara ba sai ganin Magajiya tai ta tako gaban Baba Alhaji, lokaci guda Magajiya Ke dubansa, murmushi ta saki had’ida langab’e kai kad’an “Haba Alhajina... ‘Ya’ya dai duka naka ne, kuma ko shakka babu abun kunya ne dai kun riga kun tapkashi, mai sunan duk wannan borin da kake na cewa sai ya sakar maka d’iya...? Kokuwa rik’on saikainan kashin da kayiwa d’iyarka kakewa borin kunya kake cewa a saketa....?”
Baba Alhaji ya kasa furta komai sai muzurai... Haule tai karaf tace “Toh ke kuma uban wa ya kasa dake da zaki d’auka...?”
Murmusawa Magajiya tai kad’an kana ta dubi Baba Alhaji tace “Da kai nake Alhaji na...?”
Cikeda borin kunya ya soma fad’in “Toh ai toh ai fin k’arfi aka nuna min kan d’iyata.....”
Daidai nan Sameer ya k’araso gaban Baba Alhaji murya a shak’e wanda dagaji kasan maganar fita masa kurum yake, lokaci guda yake furta “Bayan dik abubuwan saka min, bayan duk abubuwan da kaima iyayena... And especially my father... Na yafe maka, kuma ina rok’on Allah ya yafe maka.... Amma kar kace na saki matata dan bani na zab’awa kaina ita ba sannan itama ba ita ta zab’eni ba, Allah shi yai hukuncinsa akanmu... Ina kuma fata hakan ya zama wa’azi a gareku akida matarka Hajiya Haule...!”Ya k’arashe siririyar hawaye wanda da gani na tafasan zuciya ne tana gangaro masa.... Gaba d’aya k’uri suka masa jikkuna a sanyaye...
Raihanah ta duk’a tana hawaye, lokaci guda take furta “Baba...! Baba..!!” Kuka yaci k’arfinta... Wajen yai shiru bakajin komai sai sautin kukan Raihanah, ga tsananin mamakin Haule sai gani tai Baba Alhaji ya dafa kan Raihanah, cikin murya mai tsananin rawa yake furta “Ki tafi tareda mijinki.... Ki tafi tareda mijinki.... Tashi kije..!!” Abubuwan da yake iya furtawa kenan...
Raihanah ta d’ago tanai masa duban mamaki... Baba Alhaji yaci gaba da jinjina kai yana furta “Ki tafi tareda mijinki...!!!” Yana ida fad’in haka ya juya ya nufi d’aki cikin sauri tamkar mai shirin kuka...
Tuni Sameer yasa hannayensa duka biyu ya d’agota... Cikin b’angaren jikinsa yai mata masauk’i yana mai share mata hawayen fuskarta... Sahariyya ta d’aura Duka hannayenta biyu aka tana furta “Na shiga uku Hajiya kina gani kuwa....? Shegiya k’onenniyar nan ce fah Wai matar tasa... Hajiya karki barta tabisa... Mutuwa zanyi...!!” Ta k’arashe tana kururwa...
Ko takansu Sameer bai kuma bi ba ya janyo hannun matarsa suka nufi k’ofa...
‘Yandaudu suka saki tafi suna yaba dacewa dasu Raihanah da Sameer sukaida juna... Yayinda Magajiya ta saki gud’a tana taya ‘yandaudunta kod’a Raihanah da Sameer....
Haule kam mutuwar tsaye tai a wajen tamkar wata gunki ta kasa yarda Baba Alhaji ya gwaleta irin haka... Ta bud’e murya yana fad’in “Alhaji barin Raihan kai ta tafi... Shikenan ka yarda ka sallamarta ma abokan gabanka.....? Na shiga uku ni Haule....!!!”
Sahariyya kaw tukunyar dake faman tafasa da ruwan zafi ta nufa ta d’auko a guje tabi bayan su Raihanah tana furta “Wllhi yau sai na k’arasa k’onaki mai gaba d’aya kowa ya huta... Saidai a daidai hanyar fita suka kusan yin karo da Hafiz da baisan tana zuwa ba aiko nan ruwan ya dawo kanta ya kware mata... Ta shiga talewa tana ihu tana tsalle had’ida birgima a wajen... Hafiz kaw ko d’auki bai k’ok’arin kawo mata ba sai matsawa gefe da yai yana kallon yanda take birgima a k’asa tana ihu sabida zafin k’unan dake ratsata... Murmushi ya saki kana yace “Alhamdulillah yau kinji azaban irin abinda kikawa d’iyata Khausar.... Allah shi k’ara...!” Daga haka yasa kai ya kutsa cikin gidan yanda ya tadda ‘yandaudu sunyi chaa wa mahaifiyarsa sun d’aura mata tukunyar tuwo aka suna rawa suna zagayeta Haule kaw sai cazgan kuka take har abin tausai.... Hafiz yai kansu a haukace tamkar sabon kamu.... Nan suke sanar dashi uwarsu Magajiya taima rashin arziki shisa suke ladabta ta dan dama Magajiya bata koda sa’insa da Haule saidai ta saka sojojinta ‘yandaudu su handling mata Haule... A d’ari Hafiz ya nufi d’akin Mahaifinsa yana fad’in ko ya saki Magajiya ko shi yaje ya saki Sawwama... Magajiya ta mik’e tana wuraga masa harara... “K’aramin maras kunya, ai bari kaji na fad’a maka zuri’armu sun zama d’aya billahillazi mutuwa ce zata rabamu... Uwarka kuma idan tana son zama lafiya toh tabi umarni na....”
Hafiz yakai dubansa ga mahaifinsa da ya kasa furta komai sai duba daga gefe.... Girgiza kai kurum Hafiz yai cikeda takaici kana ya fice a gidan tamkar zai kifa k’asa....