Sashe 56
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ya d’ago ya dubi Mummy dake d’igan hawaye wani irin tausayinta da k’aunarta ya lullub’esa.... Jiki a sanyaye ya mik’e ya isa ga Mummy ya durk’usa had’ida d’ora kansa saman cinyarta yana kuka sosai, itama d’in kukan take sosai...
Cikin muryar kuka yake fad’in “I’m sorry Mummy, Mummy I’m sorry... Dan Allah ki yafemin, hak’ika banida gatan data wuceki a fad’in duniyar nan, da ace baki amsheni ba k’ila da yanzu an kasheni kokuma an turani wani k’asar almajiranci kaman yanda wancar matar tace... Mummy banida abinda zan biyaku keda Daddy.... Allah shi kad’ai zai iya maku sakayya.....”
Rik’o fuskar Sameer mai zuban hawaye tai itama tana hawayen take fad’in “Sameer ka daina mana godiya, har gobe kai d’ah ne a garemu koda ka sami asalin iyayenka ka sani har abada zakaci gaba da kasancewa d’ah a gareni... Sameer ka kawo haske da farin ciki ma rayuwata wanda na rasa a baya... Har abada kai d’anah ne koda ace ban haifeka ba amma a zuciyata you’re my only son.....!” Gaba d’aya suka kuma fashewa da kuka had’ida rungume juna...
Idan ka gansu sai sun baka tausayi, cikin zuciyarsa yake maimaita AMINAI UKU, Ya sha alwashin INDA RAI sai ya binciko su waye Aminai uku su waye suka rabashi da iyayensa da danginsa, su waye sukai farautar rayuwarsa shekaru talatin baya........!”
***
K’arfe biyu daidai ya sauk’a a garin Kano ko sallama baiyiwa Ammi ba ya fice abinsa, bai zarce ko ina ba sai gidan Mamani, aiko taji dad’in ziyarar tasa sai haba haba dashi take tana fad’in “Lale Haladu d’an gayu....” Tuni ta umarci Raihana data kawo masa abinci da abin sha... Tana ida kawo masa taceda Mamani zata sashen su Marliya lokacin kai abinci asibiti yayi zasu kai abincin Abbah...
Mamani ta jinjina mata kai kana tace su kula da hanya itama tana nan tafe idan rana yayi sanyi.....
Raiha ta amsa mata cikeda ladabi kana ta fice...
Duban Mamani yai kana yace “Mamani waye babu lafiya...?”
Mamani tace “Abbansu ne ke asibiti yau kwana biyu kenan...”
Khalid ya d’anyi shiru kaman mai nazari har Raiha ta kusan k’ofar fita daga sashen Mamani yaceda Mamani su tsaya zai kaisu asibitin...
Mamani tace “Kai Haladu da d’awainiya haka...”
Khalid ya kurb’i ruwan gabanshi yace “A’a haba dai ai babu komai Mamani....”
“Ayya Haladu yaron arziki....” Ta d’an bud’e murya ta kira Raiha tace “Maza kicewa ‘yan uwan naki za’a kaiku koh, ku jirashi yana nan fitowa...”
Raiha ta amsa had’ida jinjina kai kana ta nufi sashensu Nabila...
Mamani ta dubi Khalid dake k’ok’arin mik’ewa nan ta hangi rama da ya d’anyi shima..
Turus tai tana dubansa kana tace “Haladu lafiya kake kuwa... Jibi yanda ka rame ba kaman wancan lokacin da na ganka ba sannan d’an walwalan da kake yanzu du babu lafiya dai koh...?”
K’ak’aro murmushi yai yana ciro car keys d’insa daga aljihu yace “Babu komai Mamani kawai dai gajjiyan hanyace, barinje mu duba Abban...”
Mamani ta jinjina kai ba wai don ta yarda dashi ba tace “Toh abincin fah....?”
Nan ma cewa yayi sai sun dawo yaci, Mamani dai dubansa take gaba d’aya kaman wani abin na damunsa, fatan alheri da adawo lafiya tai masu kana ya fice...
Nabila ta dubi Raiha kana tace “Bak’on Mamanin ne yace zai kaimu....?”
Raiha ta jinjina kai tace “Eh Addah Naby inagama ya fice tuntuni mu yake jira....”
Daidai nan Marliya ta fito da basket na abinci tace “Mujenku koh...”
Itadai Nabilah dubansu kurum take kafin ta zira takalmanta ta biyo bayansu don tuni Marliya da Raiha sun fice...
Suka gaidashi ya amsa masu da sakin fuska kana ya bud’e masu backseat suka shige...
Yaja ya tsaya yana jiran fitowarta...
Tana tafe tana gyara zaman wuyan hijab d’inta kaman wacce akace ta d’ago idanu nan sukai ido hud’u yana tsaye ya hard’e hannaye fuskar nan tamau babu alamun walwala yana jifanta da firgitaccen kallo... Take ta d’aure fuska itama sai sakin huci tana tuna cin zarafin dasu Yesmin suka mata akanshi.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*45*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Kaman zata sa kai ta juya sai ta jiyo muryar Marliya tana fad’i mata ta k’araso su tafi....
Ta d’an d’auki wasu dak’ik’ai tana tsaye kaman bazata motsa ba sai kuma ta dawo da baya, Khalid yana ganin haka ya bud’e mota ya shige...
Itako Nabila tana k’arasowa ta nufi back seat saidai taji marfin motar a kulle, da shike glass d’an a zuge yake hakan ya bata daman danna masa harara daga cikin mirror shid’inma ita yake duba fuska babu walwala, bai tankata ba sai bud’e mata front seat da yai....
Marliya na dubansu tana karantarsu tabbas ko ba’ace ba wannan shine saurayin da Nabila ke ambatonsa, ikon Allah ashe ba Abbah kawai ba harta Mamani ya sani, Marliya tace cikin zuciyarta...
Idanunsa a kanne yake dubanta, bataso ‘yan uwan nata su fahimci wani abu, hakan yasa ta nufi frontseat tana tab’awa kuwa ta jita a bud’e, fuska a tamke babu walwala ta shige....
Kaman wanda yake jira tana shigewa yaja motar ya soma tafiya... Bakajin komai sai sautin music dake tashi a hankali cikin motar.... Marliya ce kurum da Raihana ke magana jifa jifa a b’angaren Khalid da Nabilah kuwa kowa da abinda yake sak’awa cikin zuciyarsa...
Tafiyar da bata wuce ta mintoci ashirin zuwa ashirin da ashirin da biyar ba ta kaisu asibitin....
Marliya da Raiha suka masa godiya suka sauk’a suka nufi cikin asibitin da kwandon abincin... Kafin Nabilah tai wani katab’us da niyyan fita saiji tai ya saka motar lock...
Ta kuma jan handle d’in taji tabbas a kulle ne.... Tsananin takaici ya kuma cikata...
Fuska a tamke ta juyo tanai masa wani irin duba.... Cikin tsantsan kufula take dubansa... Ba tareda ya dubeta ba yace “Tell me is it true....?”
Da tsananin mamaki ta kuma dubansa zuciyarta na kuma tafasa...
Cikin tsananin fushi take fad’in “Kaga malam ka bud’e mun k’ofa na fi....” Batakai aya ba ya katseta cikin tsananin fushi da d’aga murya lokaci guda ya juyo da fuskarsa yana dubanta...
“I’m asking you to tell me the meaning of this...!!” Ya k’arashe yana nuna mata hoton video d’in dasu Siyama suka mata yara na mata wak’an karuwace....
Zuciyarta taci gaba da sosuwa tamkar zata fito waje, take taji k’walla na neman ciko idanunta...
Banda watsa mata muguwar kallo Khalid baya komai, jin tayi shiru ya sanyashi jinjina kai had’i da sakin gajeren murmushi kana yace “So it is true.... Da gaske ne kenan... Why Teddy Bear....? Meyasa... Meyasa...? Why did you choose to break my heart.... Tell me why..!!!?” Ya k’arashe tamkar wanda zai shak’o wuyanta...
Cikin tsananin tafasan zuciya idanunta na zubar da k’walla take fad’in “This is all your fault, da ace baka shigo cikin rayuwata ba da babu wanda zaimin wannan cin zarafin, meyasa baka tambayai wad’anda suka tura maka ba idan gaskiyace ko akasinta... Why do you even care...? Meye had’ina dakai meyasa bazaka k’yaleni ba ka fice a rayuwata ba... Ni Nabilah ban tab’a giving up ma fad’a ba sai akanka.... Why just can’t you stay away, why is it so hard for you...!?” Batakai aya ba ya katseta da fad’in “Because I Love you.... I love you so much, abinda kike tambaya ba mai yuwa bane... Ina Sonki Nabeelah....” Ya k’arashe cikin tsananin huci yana mai kallon k’wayan idanunta mai zuban hawaye....
A hankali tasa bayan hannunta tana goge hawayen kana tace “Please ka bud’e min na fice...” Tai maganar cikin tsananin sanyin murya...
Ya d’auki wasu dak’ikai yana duban yanda jikinta yai sanyi sosai kafin yasa hannunsa akan security lock d’in ya bud’e...
Har ta shige cikin asibitin tana matsan k’walla kalaman ina sonki da Khalid ya fad’i mata basu daina yawo a kwanyarta ba....
Da k’yar ta iya saita kanta kana ta nufi ward d’in da Abbah yake don sam bataso iyayen nata su gano wani abu....
Da sallama saman bakinta ta shigo d’akin, saidai tsananin sanyi jikinta yai ganin gaba d’ayansu idanunsu akanta ne... Nabilah tasha jinin jikinta domin kuwa tasan dole Mamy ta tambayi ina ta tsaya ga ‘yan uwanta tuni sun shigo, duba d’aya zakaiwa Mamy ka fahimci magana ne sosai a bakinta, su Marliya ma duk sunsha jinin jikinsu don har tunanin shigowar Nabilar suke....
Fitowar Abbah daga bayi ne ya ceceta Mamy ta had’iye tambayar da tai niyyan jefo mata ta k’arasa domin taimakawa mijinta....
Gaba d’aya suka rusuna suna gaida Abban sai amsa masu yake da sakin fuska yana fad’in su k’araso kusansa sosai su gaisa don ya shirya gina wata shak’uwa ta musamman da yaransa....
Abbah yace Mamy ta huta yaransa suyi serving nasa, jiki har rawa yake Nabilah ta mik’e tana k’ok’arin serving Abbah cikedajin dad’in yanda Babansu ya canza, tanayi tana satan kallon Mamy da har lokacin muguwar kallo kurum take aika mata....
Abbah sai jan yaran nasa da fira yake yana tambayansu abubuwa sosai gameda rayuwarsu musamman gameda karatunsu, gwanin ban sha’awa....
Knocking da akai a k’ofa ya d’an katse masu firan nasu, Mamy ta bada izinin shigowa, ya shigo sallama saman bakinsa wasu samari guda biyu suka biyo bayanshi da carton d’in ruwa da nau’in lemu har kashi uku....
Suka gaidasu suka fice...
Khalid ya k’arasa shigowa Mamy tanai masa nuni da farar kujeran dake gefe, k’irjin Nabila sai faman lugude yake, Abbah yaso ganesa bayan sun gaisa nan Khalid d’in ke sanar dashi abokin Sameer ne da suka tab’a kai masa ziyara tare a gida... Nan fah aka soma sabon gaisuwa musamma da Abbah yaji cewa abokin Sameer ne....
Marliya ta k’arada fad’in shinema ya kawosu... Nabilah ta jefa mata kallo aiko itama kallon tuhumar Mamy ke mata.... Gaba d’aya ta kasa sakewa alla alla take ya tashi ya tafi, batasan uwar gulmar daya shigo dashi gaida Abbah ba da alama saida ya tsallaka kanti tsallake yayo sayayyan sannan ya shigo, wani irin muguwar haushinsa ke d’awainya da ita.....
Mamy dai bata wani sake da Khalid d’in ba kaman yanda Abbah ya sake dashi, bai wani jima sosai ba ya masu sallama had’ida fatan samun sauk’iwa Abbah...
Har suka k’araci zamansu Mamy bata sakewa Nabilah ba ita kanta tasan had’uwarsu da Mamy bazasu wanye lafiya ba she had a lot to explain to her...
Cikin muryar kuka yake fad’in “I’m sorry Mummy, Mummy I’m sorry... Dan Allah ki yafemin, hak’ika banida gatan data wuceki a fad’in duniyar nan, da ace baki amsheni ba k’ila da yanzu an kasheni kokuma an turani wani k’asar almajiranci kaman yanda wancar matar tace... Mummy banida abinda zan biyaku keda Daddy.... Allah shi kad’ai zai iya maku sakayya.....”
Rik’o fuskar Sameer mai zuban hawaye tai itama tana hawayen take fad’in “Sameer ka daina mana godiya, har gobe kai d’ah ne a garemu koda ka sami asalin iyayenka ka sani har abada zakaci gaba da kasancewa d’ah a gareni... Sameer ka kawo haske da farin ciki ma rayuwata wanda na rasa a baya... Har abada kai d’anah ne koda ace ban haifeka ba amma a zuciyata you’re my only son.....!” Gaba d’aya suka kuma fashewa da kuka had’ida rungume juna...
Idan ka gansu sai sun baka tausayi, cikin zuciyarsa yake maimaita AMINAI UKU, Ya sha alwashin INDA RAI sai ya binciko su waye Aminai uku su waye suka rabashi da iyayensa da danginsa, su waye sukai farautar rayuwarsa shekaru talatin baya........!”
***
K’arfe biyu daidai ya sauk’a a garin Kano ko sallama baiyiwa Ammi ba ya fice abinsa, bai zarce ko ina ba sai gidan Mamani, aiko taji dad’in ziyarar tasa sai haba haba dashi take tana fad’in “Lale Haladu d’an gayu....” Tuni ta umarci Raihana data kawo masa abinci da abin sha... Tana ida kawo masa taceda Mamani zata sashen su Marliya lokacin kai abinci asibiti yayi zasu kai abincin Abbah...
Mamani ta jinjina mata kai kana tace su kula da hanya itama tana nan tafe idan rana yayi sanyi.....
Raiha ta amsa mata cikeda ladabi kana ta fice...
Duban Mamani yai kana yace “Mamani waye babu lafiya...?”
Mamani tace “Abbansu ne ke asibiti yau kwana biyu kenan...”
Khalid ya d’anyi shiru kaman mai nazari har Raiha ta kusan k’ofar fita daga sashen Mamani yaceda Mamani su tsaya zai kaisu asibitin...
Mamani tace “Kai Haladu da d’awainiya haka...”
Khalid ya kurb’i ruwan gabanshi yace “A’a haba dai ai babu komai Mamani....”
“Ayya Haladu yaron arziki....” Ta d’an bud’e murya ta kira Raiha tace “Maza kicewa ‘yan uwan naki za’a kaiku koh, ku jirashi yana nan fitowa...”
Raiha ta amsa had’ida jinjina kai kana ta nufi sashensu Nabila...
Mamani ta dubi Khalid dake k’ok’arin mik’ewa nan ta hangi rama da ya d’anyi shima..
Turus tai tana dubansa kana tace “Haladu lafiya kake kuwa... Jibi yanda ka rame ba kaman wancan lokacin da na ganka ba sannan d’an walwalan da kake yanzu du babu lafiya dai koh...?”
K’ak’aro murmushi yai yana ciro car keys d’insa daga aljihu yace “Babu komai Mamani kawai dai gajjiyan hanyace, barinje mu duba Abban...”
Mamani ta jinjina kai ba wai don ta yarda dashi ba tace “Toh abincin fah....?”
Nan ma cewa yayi sai sun dawo yaci, Mamani dai dubansa take gaba d’aya kaman wani abin na damunsa, fatan alheri da adawo lafiya tai masu kana ya fice...
Nabila ta dubi Raiha kana tace “Bak’on Mamanin ne yace zai kaimu....?”
Raiha ta jinjina kai tace “Eh Addah Naby inagama ya fice tuntuni mu yake jira....”
Daidai nan Marliya ta fito da basket na abinci tace “Mujenku koh...”
Itadai Nabilah dubansu kurum take kafin ta zira takalmanta ta biyo bayansu don tuni Marliya da Raiha sun fice...
Suka gaidashi ya amsa masu da sakin fuska kana ya bud’e masu backseat suka shige...
Yaja ya tsaya yana jiran fitowarta...
Tana tafe tana gyara zaman wuyan hijab d’inta kaman wacce akace ta d’ago idanu nan sukai ido hud’u yana tsaye ya hard’e hannaye fuskar nan tamau babu alamun walwala yana jifanta da firgitaccen kallo... Take ta d’aure fuska itama sai sakin huci tana tuna cin zarafin dasu Yesmin suka mata akanshi.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*45*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Kaman zata sa kai ta juya sai ta jiyo muryar Marliya tana fad’i mata ta k’araso su tafi....
Ta d’an d’auki wasu dak’ik’ai tana tsaye kaman bazata motsa ba sai kuma ta dawo da baya, Khalid yana ganin haka ya bud’e mota ya shige...
Itako Nabila tana k’arasowa ta nufi back seat saidai taji marfin motar a kulle, da shike glass d’an a zuge yake hakan ya bata daman danna masa harara daga cikin mirror shid’inma ita yake duba fuska babu walwala, bai tankata ba sai bud’e mata front seat da yai....
Marliya na dubansu tana karantarsu tabbas ko ba’ace ba wannan shine saurayin da Nabila ke ambatonsa, ikon Allah ashe ba Abbah kawai ba harta Mamani ya sani, Marliya tace cikin zuciyarta...
Idanunsa a kanne yake dubanta, bataso ‘yan uwan nata su fahimci wani abu, hakan yasa ta nufi frontseat tana tab’awa kuwa ta jita a bud’e, fuska a tamke babu walwala ta shige....
Kaman wanda yake jira tana shigewa yaja motar ya soma tafiya... Bakajin komai sai sautin music dake tashi a hankali cikin motar.... Marliya ce kurum da Raihana ke magana jifa jifa a b’angaren Khalid da Nabilah kuwa kowa da abinda yake sak’awa cikin zuciyarsa...
Tafiyar da bata wuce ta mintoci ashirin zuwa ashirin da ashirin da biyar ba ta kaisu asibitin....
Marliya da Raiha suka masa godiya suka sauk’a suka nufi cikin asibitin da kwandon abincin... Kafin Nabilah tai wani katab’us da niyyan fita saiji tai ya saka motar lock...
Ta kuma jan handle d’in taji tabbas a kulle ne.... Tsananin takaici ya kuma cikata...
Fuska a tamke ta juyo tanai masa wani irin duba.... Cikin tsantsan kufula take dubansa... Ba tareda ya dubeta ba yace “Tell me is it true....?”
Da tsananin mamaki ta kuma dubansa zuciyarta na kuma tafasa...
Cikin tsananin fushi take fad’in “Kaga malam ka bud’e mun k’ofa na fi....” Batakai aya ba ya katseta cikin tsananin fushi da d’aga murya lokaci guda ya juyo da fuskarsa yana dubanta...
“I’m asking you to tell me the meaning of this...!!” Ya k’arashe yana nuna mata hoton video d’in dasu Siyama suka mata yara na mata wak’an karuwace....
Zuciyarta taci gaba da sosuwa tamkar zata fito waje, take taji k’walla na neman ciko idanunta...
Banda watsa mata muguwar kallo Khalid baya komai, jin tayi shiru ya sanyashi jinjina kai had’i da sakin gajeren murmushi kana yace “So it is true.... Da gaske ne kenan... Why Teddy Bear....? Meyasa... Meyasa...? Why did you choose to break my heart.... Tell me why..!!!?” Ya k’arashe tamkar wanda zai shak’o wuyanta...
Cikin tsananin tafasan zuciya idanunta na zubar da k’walla take fad’in “This is all your fault, da ace baka shigo cikin rayuwata ba da babu wanda zaimin wannan cin zarafin, meyasa baka tambayai wad’anda suka tura maka ba idan gaskiyace ko akasinta... Why do you even care...? Meye had’ina dakai meyasa bazaka k’yaleni ba ka fice a rayuwata ba... Ni Nabilah ban tab’a giving up ma fad’a ba sai akanka.... Why just can’t you stay away, why is it so hard for you...!?” Batakai aya ba ya katseta da fad’in “Because I Love you.... I love you so much, abinda kike tambaya ba mai yuwa bane... Ina Sonki Nabeelah....” Ya k’arashe cikin tsananin huci yana mai kallon k’wayan idanunta mai zuban hawaye....
A hankali tasa bayan hannunta tana goge hawayen kana tace “Please ka bud’e min na fice...” Tai maganar cikin tsananin sanyin murya...
Ya d’auki wasu dak’ikai yana duban yanda jikinta yai sanyi sosai kafin yasa hannunsa akan security lock d’in ya bud’e...
Har ta shige cikin asibitin tana matsan k’walla kalaman ina sonki da Khalid ya fad’i mata basu daina yawo a kwanyarta ba....
Da k’yar ta iya saita kanta kana ta nufi ward d’in da Abbah yake don sam bataso iyayen nata su gano wani abu....
Da sallama saman bakinta ta shigo d’akin, saidai tsananin sanyi jikinta yai ganin gaba d’ayansu idanunsu akanta ne... Nabilah tasha jinin jikinta domin kuwa tasan dole Mamy ta tambayi ina ta tsaya ga ‘yan uwanta tuni sun shigo, duba d’aya zakaiwa Mamy ka fahimci magana ne sosai a bakinta, su Marliya ma duk sunsha jinin jikinsu don har tunanin shigowar Nabilar suke....
Fitowar Abbah daga bayi ne ya ceceta Mamy ta had’iye tambayar da tai niyyan jefo mata ta k’arasa domin taimakawa mijinta....
Gaba d’aya suka rusuna suna gaida Abban sai amsa masu yake da sakin fuska yana fad’in su k’araso kusansa sosai su gaisa don ya shirya gina wata shak’uwa ta musamman da yaransa....
Abbah yace Mamy ta huta yaransa suyi serving nasa, jiki har rawa yake Nabilah ta mik’e tana k’ok’arin serving Abbah cikedajin dad’in yanda Babansu ya canza, tanayi tana satan kallon Mamy da har lokacin muguwar kallo kurum take aika mata....
Abbah sai jan yaran nasa da fira yake yana tambayansu abubuwa sosai gameda rayuwarsu musamman gameda karatunsu, gwanin ban sha’awa....
Knocking da akai a k’ofa ya d’an katse masu firan nasu, Mamy ta bada izinin shigowa, ya shigo sallama saman bakinsa wasu samari guda biyu suka biyo bayanshi da carton d’in ruwa da nau’in lemu har kashi uku....
Suka gaidasu suka fice...
Khalid ya k’arasa shigowa Mamy tanai masa nuni da farar kujeran dake gefe, k’irjin Nabila sai faman lugude yake, Abbah yaso ganesa bayan sun gaisa nan Khalid d’in ke sanar dashi abokin Sameer ne da suka tab’a kai masa ziyara tare a gida... Nan fah aka soma sabon gaisuwa musamma da Abbah yaji cewa abokin Sameer ne....
Marliya ta k’arada fad’in shinema ya kawosu... Nabilah ta jefa mata kallo aiko itama kallon tuhumar Mamy ke mata.... Gaba d’aya ta kasa sakewa alla alla take ya tashi ya tafi, batasan uwar gulmar daya shigo dashi gaida Abbah ba da alama saida ya tsallaka kanti tsallake yayo sayayyan sannan ya shigo, wani irin muguwar haushinsa ke d’awainya da ita.....
Mamy dai bata wani sake da Khalid d’in ba kaman yanda Abbah ya sake dashi, bai wani jima sosai ba ya masu sallama had’ida fatan samun sauk’iwa Abbah...
Har suka k’araci zamansu Mamy bata sakewa Nabilah ba ita kanta tasan had’uwarsu da Mamy bazasu wanye lafiya ba she had a lot to explain to her...