Sashe 67
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jinjina kai Lami tai cikeda tsoro kana tace “Haule shine shine dai Ma’aruf ya dawo garemu... Wayyo Allah na Haule, idan Usman ya koreni ina zanje ni ba d’a ba balle jika ba iyaye a raye ba, ina zan dafa Haule...?”
Muzurai Hajiya keyi tana faman sak’e sak’e cikin zuciyarta....
Cikin sauri ta kuma kamo hannayen Aunty Lami kana tace cikin k’asa k’asa da murya “Ki kwantar da hankalinki Lami asirinmu bazai tab’a tonuwa ba... Ni nasan abinda zanyi amma a halin yanzu ki koma kuma kiyi k’ok’ari ki daina bari wannan tsoron naki yana rinjayarki, ki watsar da komai ki nuna tamkar bakisan komai ba....”
Aunty Lami da har lokacin a firgice take ta dubi Hajiya Haule tace “Haule ina zan iya rayuwa gida guda da Ma’aruf..? Gani nake kaman zai tuno fuskokinmu....”
Hajiya tai wata shed’aniyar murmushi tace “Lami bazaki canza ba wannan tsoron naki har yanzu yana nan... Shekarun da yawa Lami na tabbata Ma’aruf bazai fahimci komai ba sannan da ace zai gane wani abu da ya fahimta tinda ya had’u damu tin ba yanzu ba don haka ki kwantar da hankalinki kici gaba da al’amranki kaman da kar ki janyo wani abinda zaisa asirinmu ya tonu... Jeki jeki kawai sai mun had’u mu duka UKUN na tabbata Aminiyar Sirri zatafi kowa gudun tonuwar wannan dadd’en sirrin.... Jeki Lami mijinki zai iya zargin wani abu....” Tana ida fad’in haka ta janyo hannun Aunty Lami suka nufo waje yayinda Naja’atu ta b’ace daga wajen cikin sauri tana mamakin tattaunawan dataji Hajiya da Aunty Lami keyi... Shin waye Ma’aruf shin kodai Yaya Ma’aruf d’an gidan Abbah suke nufi da ya b’ace shekaru da jimawa... Shin kodai akwai sa hannun Hajiyarta a b’acewarsa ne...?” Tambayoyin da suka cika zuciyar Naja’atu.. Dole tabi a sannu don gano wannan sirri da Hajiya ke k’ok’arin bisnewa bayan yana neman tona kansa, ta d’au alwashin bazata kuma bari Hajiya ta cuci wani ba koda kuwa Mahaifinta ne da Hajiyar ta riga ta shanyesa... Da wannan tunani Naja’atu ta koma mawanki jiki a sanyaye.....
***
Koda Aunty Lami ta koma asibitin bata tadda Abbah ba, tayi tunanin hakan ka iya kasancewa don haka kai tsaye gida ta wuce yanda ta tadda gaba d’aya illahirin ahalin gidan suna hallare a parlor, Alhaji Usman Mailafiya na daga center yayinda sauran ahalin ke kewaye dashi, can ta hangi Sameer na zaune k’asa shima kusada k’afafun Abbah...
Gaban Aunty Lami ya kuma tsinkewa musamman data hango kwantacciyar murmushi dake a fuskar Mamy...
Abbah yayi gyaran murya kana yace gaba da fad’in “Kaman yanda kuka sani a gidan nan ko nace a ahalin nan mun kwashe sama da shekaru talatin muna neman d’an uwanku wanda ya b’ace mana a ranar da kikazo duniya Zulfa’u.....”
Zulfah ta d’ago idanunta mai zuban hawaye cikin sauri tana duban Abbah yayinda muryar Abbah ta soma rawa sosai.....
Sameer ya d’ago yana duban wacce aka kirada Zulfa’u... Tsananin tausayinta ya rufesa sanda take fad’in “Abbah Ka samu Yayana ne... Abbah ka sami Yaya Ma’aruf ne....?”
Abbah na murmushi hawaye na gangaro mashi yace “Zulfa’u Allah ya bayyana mana Yayanku ya yaye mana bak’in ciki da muka jima a cikinta....” Idanun Abbah suka sauk’a kan Sameer dake faman bin ‘yan uwansa da kallo d’aya bayan d’aya...
Gaba d’aya suka maida dubansuga likitan wanda azatonsu yana wajen ne kurum a matsayinsa na likitan Abbah...
Murya na rawa Marliya tace “Abbah wannan shine Ya Ma’aruf... Shine Yaya na da ban sanshi ba sai labarinshi....”
Sameer da siririyar hawaye ta gangaro masa a hankali yake furta “Nine Yayanki Ni ne Yayanki da baki sani ba little Sis....” A guje ta tafi gareshi sai kuma taja ta tsaya hawaye sun wanke mata fuska... Murmushi saman fuskokinsu tace “Can I please hug you...?”
Ya jinjina mata kai a hankali murmushi saman fuskarsa yake furta “Of course.... Come here...” Ya bud’e mata hannaye ta tafi a guje ta rungumesa....
Su Nabila da Zulfa’u hawayene kurum suma ke kwaranyowa daga idanunsu...
Sameer ya d’ago ya dubesu kana yace su taho suma...
Gaba d’aya su duka hud’un suka rungume juna suna hawaye
Cikin muryar kuka Sameer ke furta “I have beautiful sisters in the world....” Yana fad’i murmushi mai bayyana hak’wara na fita daga fuskarsa...
Yanda suka rungume juna su duka hud’u suna hawaye yasa Mamy da Abbah zuban hawaye
A hankali Mamy ta isa ta rungume yaranta gaba d’aya tana hawaye take hamdala ga Ubangijinta da ya nuna mata rana irin wannan, ga yaranta gaba d’aya a tareda ita...
Harta Aunty Lami dake tsaye jikin k’ofa saida taji k’walla na neman ciko idanunta, ji tai bazata iya shiga parlorn ba cikin sauri ta juyoda baya tana mai goge hawayen da ya mak’ale mata a idanu... Ido hud’u sukai da Aunty Bara’atu... Sukai tsaye suna duban juna....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
55
*©️Sameena Aleeyou ...✍🏽*
NOT EDITED
Cikin sauri Aunty Lami tasa kai zata shige Aunty Bara’atu ta janyota.... Kallon kallo suke aikawa juna lokaci guda Aunty Bara’atu ta saki murmushi kana tace “Kina mamaki ya dawo ne...?”
Aunty Lami ta waiga gefe da gefe kana tace “Mai kike nufi.....?”
Janyota Aunty B ta kumayi kana tace “Muje, ban yarda dake ba, you must be hiding something....” Lokaci guda ta tura k’eyarta suka b’ace daga wajen Aunty Lami na faman muzurai......
Parlorn yai shiru sanda Sameer ke labarta masu rayuwarsa da mutanen da ya tashi ya gansu a matsayin iyayensa, Mamy da Abbah saida suka zubda k’walla jin yanda iyayen goyon Sameer suka rik’eshi bisa gaskiya da amana ba tareda sunsan cewa ko su waye iyayenshi ba, sun d’au alwashin kaima iyayen rik’on Sameer ziyara ta musamman da kuma mik’a godiyarsu a garesu baki d’aya....
Yanda Mummy ta bashi labarin k’anda akai ya fad’a hannunsu haka ya sanar dasu Mamy, sosai abin ya d’aure masu kai, al’ajabi ya cikasu baki d’aya...
Abbah yace “Wannan yana nuni da cewa tabbas Ma’aruf ba b’acewa kayi haka kurum ba, tabbas akwai mugu a tsakani wanda yaso rabaka damu koma yaso rabaka da rayuwarka baki d’aya....”
Sameer ya jinjina kai kana yace “K’warai Abbah wannan shine abinda nake tunani bayan mahaifiyata ta bani labarin yanda akayi na b’ace daga gareta....”
Zulfa’u datai jigum tana saurarensu sai cewa tayi “Toh Abbah shin wanene zai nemi ganin bayan k’aramin yaro irin haka a wancan lokacin....? Lallai wannan mutumi yakai k’ololuwa wajen rashin imani....”
Abbah ya sauk’e ajiyan zuciya kana yace “Zulfa’u Duniyarmu cike take da mutane iri daban daban, kana tare da mutum wasu lokutan amma bakasan wanene mugu ba, masu iya magana sunce mugu baida kama...”
Nabilah dake zaune gefensa so take ta tambayesa mecece alak’arsa da Khalid amma bata san ta yanda zata soma tambayar nasa ba...
“Ya Ma’aruf ....”
Ta kirawo sunansa a hankali....
D’agowa yayi yana dubanta jin sabon sunan da aka ambace sa dashi...
Itama d’in taji wani iri don ba sabawa sukai ba...
A hankali ta d’an sadda kai kana tace “Sorry... Can we please call you Ya Ma’aruf....?”
Murmushi Sameer yai kana yace “You can call me Ya Ma’aruf or Ya Sameer duka sunana ne zan amsa kinji koh....”
A hankali ta saki murmushi ita da sauran ‘yan uwan nata...
Shigowar Aunty Lami ya hana Nabilah ci gaba da magana..
Murmushi har kunne Aunty Lami ta shigo tana fad’in “Masha Allah.. Masha Allah .... Finally Ma’aruf d’inmu ya dawo.... Alhamdulillahi Allah shine abin godiya....” Ta k’arashe tana mai zama gaban Sameer da yai mutuwar zaune yana duban matar, wacce duba guda ya mata yaji k’irjinsa ya buga dum kaman an aje guduma lokaci guda....
Aunty Lami ta kuma fad’ad’a murmushinta tana fad’in “Ma’aruf...! Ma’aruf ashe zamu sake sakaka a idanuwan mu....!!!?” Lokaci guda kuma ta shiga tattaro bakin zani tana goge hawayen dake zubo mata wanda zakai zaton tsan tsan farin ciki ne....
Sameer duk sau yaji wani iri ganin matar tana sharan kuka gabansa...
Nabilah tab’e baki kurum tai tana kallon salon makircin matar Baban nata
Abbah na murmushi yake fad’in “Lami d’anki Ma’aruf ya dawo garemu... Allah ya dawo mana dashi....” Ya dubi Sameer yace “Ma’aruf wannan itace mamarka Lami abokiyar zama ce ga mahaifiyarka....”
Sameer ya sakar mata murmushi zai bud’a baki tai saurin cewa “Call me Aunty Lami..... Haka k’annenka suke kirana....”
Ya kuma sakin murmushi kana yace “Aunty Lami......”
Ta jinjina kai tana kuma sakin murmushi....
Murmushin yak’e kurum Sameer yake amma har ransa baijin ya sake da matar, sannan yana tuna kaman wani muhimmin abu ya tab’a had’asa da ita a wasu lokuta can masu tsawo....
Sameer bai sami zarafin sanar dasu cewa nada iyali ba har akai masa waya ana neman sa acan asibiti, shi kansa ya mance da sabgan wata Siyama, Farin cikin had’uwa da dangin sa da iyayensa ya sakashi mancewa da duk wani k’unci da Siyama ta jefa sa ciki.....
Yana isa asibiti ward d’in Raihanah ya nufa duk da cewa director na asibitin ne da kansa yake nemansa...
A hankali Sameer ya murd’a handle d’in k’ofar.... Kwance ya hangeta idanunta a rufe alamun bacci take... Ya jima yana dubanta kafin yaji motsin tab’a k’ofan toilet
Cikin sauri ya janyo k’ofar a hankali ya shige don dama kiran nasa director na asibitin ne mai nemansa..
***
Duk saurin da yake gudun kada ya makara ya bar ogan nashi zaman jira saida ya makara sabida holdup mai tsawo data kuma tsareshi, cikin ransa yake ayyana tabbas yasan Boss ya gama shiryawa shi kawai ake jira tinda yasan African time ba tsarinsa bane.... Yana tsaka da tunanin ne wayar d’aya daga cikin tawagan nasu ya shigo masa.... Bai d’aga ba sai k’ara malejin motar da yai, Don ko ya d’aga yasan maganar guda ce His excellency ya shirya shi ake jira....
Muzurai Hajiya keyi tana faman sak’e sak’e cikin zuciyarta....
Cikin sauri ta kuma kamo hannayen Aunty Lami kana tace cikin k’asa k’asa da murya “Ki kwantar da hankalinki Lami asirinmu bazai tab’a tonuwa ba... Ni nasan abinda zanyi amma a halin yanzu ki koma kuma kiyi k’ok’ari ki daina bari wannan tsoron naki yana rinjayarki, ki watsar da komai ki nuna tamkar bakisan komai ba....”
Aunty Lami da har lokacin a firgice take ta dubi Hajiya Haule tace “Haule ina zan iya rayuwa gida guda da Ma’aruf..? Gani nake kaman zai tuno fuskokinmu....”
Hajiya tai wata shed’aniyar murmushi tace “Lami bazaki canza ba wannan tsoron naki har yanzu yana nan... Shekarun da yawa Lami na tabbata Ma’aruf bazai fahimci komai ba sannan da ace zai gane wani abu da ya fahimta tinda ya had’u damu tin ba yanzu ba don haka ki kwantar da hankalinki kici gaba da al’amranki kaman da kar ki janyo wani abinda zaisa asirinmu ya tonu... Jeki jeki kawai sai mun had’u mu duka UKUN na tabbata Aminiyar Sirri zatafi kowa gudun tonuwar wannan dadd’en sirrin.... Jeki Lami mijinki zai iya zargin wani abu....” Tana ida fad’in haka ta janyo hannun Aunty Lami suka nufo waje yayinda Naja’atu ta b’ace daga wajen cikin sauri tana mamakin tattaunawan dataji Hajiya da Aunty Lami keyi... Shin waye Ma’aruf shin kodai Yaya Ma’aruf d’an gidan Abbah suke nufi da ya b’ace shekaru da jimawa... Shin kodai akwai sa hannun Hajiyarta a b’acewarsa ne...?” Tambayoyin da suka cika zuciyar Naja’atu.. Dole tabi a sannu don gano wannan sirri da Hajiya ke k’ok’arin bisnewa bayan yana neman tona kansa, ta d’au alwashin bazata kuma bari Hajiya ta cuci wani ba koda kuwa Mahaifinta ne da Hajiyar ta riga ta shanyesa... Da wannan tunani Naja’atu ta koma mawanki jiki a sanyaye.....
***
Koda Aunty Lami ta koma asibitin bata tadda Abbah ba, tayi tunanin hakan ka iya kasancewa don haka kai tsaye gida ta wuce yanda ta tadda gaba d’aya illahirin ahalin gidan suna hallare a parlor, Alhaji Usman Mailafiya na daga center yayinda sauran ahalin ke kewaye dashi, can ta hangi Sameer na zaune k’asa shima kusada k’afafun Abbah...
Gaban Aunty Lami ya kuma tsinkewa musamman data hango kwantacciyar murmushi dake a fuskar Mamy...
Abbah yayi gyaran murya kana yace gaba da fad’in “Kaman yanda kuka sani a gidan nan ko nace a ahalin nan mun kwashe sama da shekaru talatin muna neman d’an uwanku wanda ya b’ace mana a ranar da kikazo duniya Zulfa’u.....”
Zulfah ta d’ago idanunta mai zuban hawaye cikin sauri tana duban Abbah yayinda muryar Abbah ta soma rawa sosai.....
Sameer ya d’ago yana duban wacce aka kirada Zulfa’u... Tsananin tausayinta ya rufesa sanda take fad’in “Abbah Ka samu Yayana ne... Abbah ka sami Yaya Ma’aruf ne....?”
Abbah na murmushi hawaye na gangaro mashi yace “Zulfa’u Allah ya bayyana mana Yayanku ya yaye mana bak’in ciki da muka jima a cikinta....” Idanun Abbah suka sauk’a kan Sameer dake faman bin ‘yan uwansa da kallo d’aya bayan d’aya...
Gaba d’aya suka maida dubansuga likitan wanda azatonsu yana wajen ne kurum a matsayinsa na likitan Abbah...
Murya na rawa Marliya tace “Abbah wannan shine Ya Ma’aruf... Shine Yaya na da ban sanshi ba sai labarinshi....”
Sameer da siririyar hawaye ta gangaro masa a hankali yake furta “Nine Yayanki Ni ne Yayanki da baki sani ba little Sis....” A guje ta tafi gareshi sai kuma taja ta tsaya hawaye sun wanke mata fuska... Murmushi saman fuskokinsu tace “Can I please hug you...?”
Ya jinjina mata kai a hankali murmushi saman fuskarsa yake furta “Of course.... Come here...” Ya bud’e mata hannaye ta tafi a guje ta rungumesa....
Su Nabila da Zulfa’u hawayene kurum suma ke kwaranyowa daga idanunsu...
Sameer ya d’ago ya dubesu kana yace su taho suma...
Gaba d’aya su duka hud’un suka rungume juna suna hawaye
Cikin muryar kuka Sameer ke furta “I have beautiful sisters in the world....” Yana fad’i murmushi mai bayyana hak’wara na fita daga fuskarsa...
Yanda suka rungume juna su duka hud’u suna hawaye yasa Mamy da Abbah zuban hawaye
A hankali Mamy ta isa ta rungume yaranta gaba d’aya tana hawaye take hamdala ga Ubangijinta da ya nuna mata rana irin wannan, ga yaranta gaba d’aya a tareda ita...
Harta Aunty Lami dake tsaye jikin k’ofa saida taji k’walla na neman ciko idanunta, ji tai bazata iya shiga parlorn ba cikin sauri ta juyoda baya tana mai goge hawayen da ya mak’ale mata a idanu... Ido hud’u sukai da Aunty Bara’atu... Sukai tsaye suna duban juna....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
55
*©️Sameena Aleeyou ...✍🏽*
NOT EDITED
Cikin sauri Aunty Lami tasa kai zata shige Aunty Bara’atu ta janyota.... Kallon kallo suke aikawa juna lokaci guda Aunty Bara’atu ta saki murmushi kana tace “Kina mamaki ya dawo ne...?”
Aunty Lami ta waiga gefe da gefe kana tace “Mai kike nufi.....?”
Janyota Aunty B ta kumayi kana tace “Muje, ban yarda dake ba, you must be hiding something....” Lokaci guda ta tura k’eyarta suka b’ace daga wajen Aunty Lami na faman muzurai......
Parlorn yai shiru sanda Sameer ke labarta masu rayuwarsa da mutanen da ya tashi ya gansu a matsayin iyayensa, Mamy da Abbah saida suka zubda k’walla jin yanda iyayen goyon Sameer suka rik’eshi bisa gaskiya da amana ba tareda sunsan cewa ko su waye iyayenshi ba, sun d’au alwashin kaima iyayen rik’on Sameer ziyara ta musamman da kuma mik’a godiyarsu a garesu baki d’aya....
Yanda Mummy ta bashi labarin k’anda akai ya fad’a hannunsu haka ya sanar dasu Mamy, sosai abin ya d’aure masu kai, al’ajabi ya cikasu baki d’aya...
Abbah yace “Wannan yana nuni da cewa tabbas Ma’aruf ba b’acewa kayi haka kurum ba, tabbas akwai mugu a tsakani wanda yaso rabaka damu koma yaso rabaka da rayuwarka baki d’aya....”
Sameer ya jinjina kai kana yace “K’warai Abbah wannan shine abinda nake tunani bayan mahaifiyata ta bani labarin yanda akayi na b’ace daga gareta....”
Zulfa’u datai jigum tana saurarensu sai cewa tayi “Toh Abbah shin wanene zai nemi ganin bayan k’aramin yaro irin haka a wancan lokacin....? Lallai wannan mutumi yakai k’ololuwa wajen rashin imani....”
Abbah ya sauk’e ajiyan zuciya kana yace “Zulfa’u Duniyarmu cike take da mutane iri daban daban, kana tare da mutum wasu lokutan amma bakasan wanene mugu ba, masu iya magana sunce mugu baida kama...”
Nabilah dake zaune gefensa so take ta tambayesa mecece alak’arsa da Khalid amma bata san ta yanda zata soma tambayar nasa ba...
“Ya Ma’aruf ....”
Ta kirawo sunansa a hankali....
D’agowa yayi yana dubanta jin sabon sunan da aka ambace sa dashi...
Itama d’in taji wani iri don ba sabawa sukai ba...
A hankali ta d’an sadda kai kana tace “Sorry... Can we please call you Ya Ma’aruf....?”
Murmushi Sameer yai kana yace “You can call me Ya Ma’aruf or Ya Sameer duka sunana ne zan amsa kinji koh....”
A hankali ta saki murmushi ita da sauran ‘yan uwan nata...
Shigowar Aunty Lami ya hana Nabilah ci gaba da magana..
Murmushi har kunne Aunty Lami ta shigo tana fad’in “Masha Allah.. Masha Allah .... Finally Ma’aruf d’inmu ya dawo.... Alhamdulillahi Allah shine abin godiya....” Ta k’arashe tana mai zama gaban Sameer da yai mutuwar zaune yana duban matar, wacce duba guda ya mata yaji k’irjinsa ya buga dum kaman an aje guduma lokaci guda....
Aunty Lami ta kuma fad’ad’a murmushinta tana fad’in “Ma’aruf...! Ma’aruf ashe zamu sake sakaka a idanuwan mu....!!!?” Lokaci guda kuma ta shiga tattaro bakin zani tana goge hawayen dake zubo mata wanda zakai zaton tsan tsan farin ciki ne....
Sameer duk sau yaji wani iri ganin matar tana sharan kuka gabansa...
Nabilah tab’e baki kurum tai tana kallon salon makircin matar Baban nata
Abbah na murmushi yake fad’in “Lami d’anki Ma’aruf ya dawo garemu... Allah ya dawo mana dashi....” Ya dubi Sameer yace “Ma’aruf wannan itace mamarka Lami abokiyar zama ce ga mahaifiyarka....”
Sameer ya sakar mata murmushi zai bud’a baki tai saurin cewa “Call me Aunty Lami..... Haka k’annenka suke kirana....”
Ya kuma sakin murmushi kana yace “Aunty Lami......”
Ta jinjina kai tana kuma sakin murmushi....
Murmushin yak’e kurum Sameer yake amma har ransa baijin ya sake da matar, sannan yana tuna kaman wani muhimmin abu ya tab’a had’asa da ita a wasu lokuta can masu tsawo....
Sameer bai sami zarafin sanar dasu cewa nada iyali ba har akai masa waya ana neman sa acan asibiti, shi kansa ya mance da sabgan wata Siyama, Farin cikin had’uwa da dangin sa da iyayensa ya sakashi mancewa da duk wani k’unci da Siyama ta jefa sa ciki.....
Yana isa asibiti ward d’in Raihanah ya nufa duk da cewa director na asibitin ne da kansa yake nemansa...
A hankali Sameer ya murd’a handle d’in k’ofar.... Kwance ya hangeta idanunta a rufe alamun bacci take... Ya jima yana dubanta kafin yaji motsin tab’a k’ofan toilet
Cikin sauri ya janyo k’ofar a hankali ya shige don dama kiran nasa director na asibitin ne mai nemansa..
***
Duk saurin da yake gudun kada ya makara ya bar ogan nashi zaman jira saida ya makara sabida holdup mai tsawo data kuma tsareshi, cikin ransa yake ayyana tabbas yasan Boss ya gama shiryawa shi kawai ake jira tinda yasan African time ba tsarinsa bane.... Yana tsaka da tunanin ne wayar d’aya daga cikin tawagan nasu ya shigo masa.... Bai d’aga ba sai k’ara malejin motar da yai, Don ko ya d’aga yasan maganar guda ce His excellency ya shirya shi ake jira....