Sashe 108
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Wayar na manne kunnenta na hagu tayi shiru alamun tana sauraren magana daga d’aya b’angaren, cikin sanyin murya irin tata tace “Mamy Abbah kuma..? Mamy cewa yai na dawo...?”
Daga d’aya b’angaren Mamy tace “Zulfa’u kinsan halin Baban naku waima yanzu abin yayi sauk’i tun bayan bayyanar Yayanku, kinfi kowa sanin halinsa ai....”
Zulfa’u da hawaye ke k’ok’arin cikowa idanunta tace “Mamy wllhi Allah nasan bayin Abbah bane, nasan haka kurum bazaice na tattara na dawo gida ba, Mamy nan fah da can duk d’aya ne, kuma ma nan d’in yafimin sauk’in tafiya Office...”
Sauk’e ajiyan zuciya Mamy tai kana tace “Zulfa’u nima na fad’a mishi hakan, amma yace lallai lallai gobe ki dawo gida, tinda naga Baba Alhaji ya fice daga parlornsa nasan wani zance ka iya biyo baya tinda gashi ya hura wuta sosai kan maganar auren Yayanku da ‘yar wajensa Sahariyya...”
Shiru Zulfah tai tana nazarin maganganun Mamyn kana tace “Baba Alhaji yazo Mamy...?”
Mamy tace “Yanda kikaji... Banason dogon bayani Zulfa’u ki tattara gobe kizo gida zan nemi Antin taku a waya nai mata bayanin komai....”
A hankali Zulfah ta jinjina kai tamkar Mamyn na dubanta kana tace “Shikenan Mamy zanyi yanda kukace in sha Allah....”
“Yauwa sai kinzo, Allah shi miki Albarka...”
“Ameen Mamy...”
Sukai sallama kana Zulfah tai jigum tana tunanin, yanda Baba Alhaji ya hura wuta kan batun auren Ya Ma’aruf da Sahariyya ko shakka babu akwai abinda yake shirin yi tsakaninta da Ya Hafiz, idan kuwa nufinsa ne maida aurensu da Ya Hafiz gaskiya ba’a kyauta mata ba... Tana tsaka da tinanin Aunty B ta shigo ta taddata...
Tsaye tai tana duban Zulfa’un da tai nisa duniyar tunani....
Aunty B ta k’arasa ta ije kayan gugan data shigo dashi saman gado, gefen Zulfa’u ta zauna had’ida d’an dafata kad’an “Daughter lafiya... meke faruwa naga kinyi nisa cikin tunani haka...?”
Sauk’e ajiyan zuciya Zulfah tai “Aunty, Mamy ce muka gama waya da ita...”
Aunty B ta jinjina kai “Umhum ina jinki....”
Gyara zama Zulfa’u ta kumayi kana tace “Cewa tayi Abbah yace lallai lallai gobe na koma gida, and daga bayananta kaman maganar bazai wuce akan aurena da Ya Hafiz ba... Aunty idan hakan ta kasance bansan ya zanyi ba, tsoro nake kar suce zasu kuma had’a aurenmu a karo na biyu tinda gashi Baba Alhaji ya hura wuta kan batun auren Ya Ma’aruf da Sahariyya...”
Shiru Aunty B tai tamkar mai nazari kana tace “Bazai yuwu ki koma gidan Hafiz ba, bazan bari ba....”
Dubanta Zulfa’u tai da idanunta da sukai raurau “Aunty idan sukace na koma fah... Bazan iya bijire masu ba...”
Girgiza kai Aunty B tai had’ida gyara zama sosai “Toh ke Zulfa’u mai zai hana ki baiwa yaron nan Akram dama iyaye su shiga maganar tinda gashi naji Atika na cewa tin satin da ya shige yaketa damunki da batun turo magabatansa amma kink’i basa k’ofa, na tabbata idan sukaga kin tsaida manemi bazasu miki dole ba, saidai idan kuma har yanzu kina son Hafiz d’in ne....”
Fuzar da iska maras k’arfi Zulfah tai had’ida muskutawa “Aunty bazan b’oye maki ba, da fari bansan mai nakeji ba, I was so confused about Ya Hafiz amma yanzu ina mai tabbatar maki bana son Ya Hafiz, shi ma Akram banjin ina sonsa Aunty... Bansan menene na hanzarin ba, dadai sun barni zuwa wani d’an lokacin to get my head cleared...”
Sauk’e ajiyan zuciya Aunty B tai kana tace “Akram yaron kirki ne Zulfa’u kuma ni nan nasa anmin bincike akanshi and his background, baida wani aibu, mai zai hana ki bashi dama Zulfa’u, idan dai iyayenki sun matsa nidai a nawa shawarin da ki bari su maida aurenki da Hafiz gwara miki wannan yaro Akram... Amma fah shawarice... Ki natsu kiyi tunani kuma ki fad’iwa Ubangijinki ki fawwala masa lamranki domin zab’insa shine maki alkhairi...”
A hankali Zulfah ta jinjina kai kana tace “Toh Aunty zanyi yanda kikace zanyi tunanin... kuma zanyi addu’a dikda cewa cikin yinta nake ko yaushe....Na gode da shawarwarinki Aunty... thank you for always being there..”
D’an rungumeta Aunty B tai kana tace “Anything for you daughter... Allah Ubangiji ya miki zab’i mafi alkhairi...”
Zulfa’u ta amsada “Ameen Aunty na...”
***
Koda Sameer ya sami sak’on Wan mahaifin nasa bai k’asa a gwiwa ba ya amsa kiran nasa, saidai bai sami Baba Alhajin gida ba saiko Haule da yaranta, musamman Haule tasa Najah ta bud’e masa parlorn Baba Alhaji, sai wani nan nan dashi ake, Sameer bai mance farkon zuwansa gidan ba sanda ya buge Raihanah ya tadda Haule da wannan maras kunyar ‘yar nata da ake yunk’urin aura masa matsayin mata sun tasa Raihanah a gaba suna aibantata... Tinda ya shigo gidan gaba d’aya a tsare yake sosai, ganinsu ya kuma tuno masa abinda ya tadda suna ma Raihanah a wancan lokacin, kansa na bisa wayarsa Haule ta shigo tamkar zata zube ta masa sijjada, sai rawa jikinta keyi tana kuma tura k’eyar Najah tana fad’in tai sauri ta ije masa kayan motsa baki dake hannunta...
Najah dai girgiza kai kurum tai kana ta k’arasa ta aje masa tray d’in tana gaidashi... A tak’aice ya amsa sannan har lokacin fuskarsa babu walwala....
Ga mamakin Haule jira take yaji yace ina amaryarsa take, shiru kakeji saima sinkayo muryarsa tai yana tambayar Najah Baba Alhaji...
Najah tace “Ai ba dawo ba Yaya...”
Jinjina kai kurum yai kana ya dubi agogon hannunsa....
Haule ta watsawa Najah harara sanda take ficewa kana ta kutso kai ta shigo parlorn, baki har kunne take sakin murmushi da sallama...
A tak’aice Sameer ya gaidata don tuntuni baisan maiyasa tasu batazo d’aya da matar ba ko bayan da ya fahimci matar yayan babansa ne, ko hakan nada alak’a da saninda ya mata a fari ne sai Allah.... Dik yanda Haule taso tajasa da hira ta kasa samun fuska, harta firan kawo kayan lefe da shirinsa na biki dataita k’ok’arin bijiro dashi babu ko kamun kai Sameer bai amsa mata ba, k’arshe dai data gama kid’inta da rawarta mik’ewa tai tana fad’in “Ka saki jikinka fah kaci komai nan gidanku bara na kira maka Sahariyyar tana can tana shiryawa...”
D’an dakatar da ita yai da fad’in “A’a da kin barta don zuwan ba nata bane...”
Haule bata bari ya dasa aya ba tace “A’a karka damu tindadai kazo dole ta fito ku gaisa...” Kallo kurum yabi Haule dashi yanda take rawar k’afa har ta fice...
A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya yana mai ayyanawa cikin zuciyarsa “What have you gotten yourself into Sameer... Baka gama da problem d’in Siyama ba ga wani na kunno maka kai....” a hankali ya fuzar da iska mai zafin gaske yana mai ayyanawa cikin zuciyarsa he’s doing this for the sake of the family, he cannot allow his family to fall apart bayan k’unci da suka fuskanta a lokacin da ya b’ace, he has to sacrifice and do what they ask him to do, for the sake of everybody’s happiness....
Yana tsaka da tunanin wayarsa ta d’auki ruri...
Sanda Sahariyya ta shigo parlorn waya yake dan haka bai amsa sallamarta ba, sai wani sanne sanne kai take ita a dole an fito zance wajen saurayi....
Duba guda ya mata ya d’auke kansa, har lokacin waya yake....
Sahariyya ta k’arasa ta zauna a kujera mai kallon nasa.... Sai faman sakin murmushi take tana k’irga ‘yan yatsunta yawa mutumiyar arzikin gaske...
Lokaci guda taga ya mik’e yana fad’i cikin wayar “I’ll be on my way...”
Zunbur Sahariyya ta mik’e tana binsa da kallon mamaki....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................ DA DABO_
*79*
Daga d’aya b’angaren Mamy tace “Zulfa’u kinsan halin Baban naku waima yanzu abin yayi sauk’i tun bayan bayyanar Yayanku, kinfi kowa sanin halinsa ai....”
Zulfa’u da hawaye ke k’ok’arin cikowa idanunta tace “Mamy wllhi Allah nasan bayin Abbah bane, nasan haka kurum bazaice na tattara na dawo gida ba, Mamy nan fah da can duk d’aya ne, kuma ma nan d’in yafimin sauk’in tafiya Office...”
Sauk’e ajiyan zuciya Mamy tai kana tace “Zulfa’u nima na fad’a mishi hakan, amma yace lallai lallai gobe ki dawo gida, tinda naga Baba Alhaji ya fice daga parlornsa nasan wani zance ka iya biyo baya tinda gashi ya hura wuta sosai kan maganar auren Yayanku da ‘yar wajensa Sahariyya...”
Shiru Zulfah tai tana nazarin maganganun Mamyn kana tace “Baba Alhaji yazo Mamy...?”
Mamy tace “Yanda kikaji... Banason dogon bayani Zulfa’u ki tattara gobe kizo gida zan nemi Antin taku a waya nai mata bayanin komai....”
A hankali Zulfah ta jinjina kai tamkar Mamyn na dubanta kana tace “Shikenan Mamy zanyi yanda kukace in sha Allah....”
“Yauwa sai kinzo, Allah shi miki Albarka...”
“Ameen Mamy...”
Sukai sallama kana Zulfah tai jigum tana tunanin, yanda Baba Alhaji ya hura wuta kan batun auren Ya Ma’aruf da Sahariyya ko shakka babu akwai abinda yake shirin yi tsakaninta da Ya Hafiz, idan kuwa nufinsa ne maida aurensu da Ya Hafiz gaskiya ba’a kyauta mata ba... Tana tsaka da tinanin Aunty B ta shigo ta taddata...
Tsaye tai tana duban Zulfa’un da tai nisa duniyar tunani....
Aunty B ta k’arasa ta ije kayan gugan data shigo dashi saman gado, gefen Zulfa’u ta zauna had’ida d’an dafata kad’an “Daughter lafiya... meke faruwa naga kinyi nisa cikin tunani haka...?”
Sauk’e ajiyan zuciya Zulfah tai “Aunty, Mamy ce muka gama waya da ita...”
Aunty B ta jinjina kai “Umhum ina jinki....”
Gyara zama Zulfa’u ta kumayi kana tace “Cewa tayi Abbah yace lallai lallai gobe na koma gida, and daga bayananta kaman maganar bazai wuce akan aurena da Ya Hafiz ba... Aunty idan hakan ta kasance bansan ya zanyi ba, tsoro nake kar suce zasu kuma had’a aurenmu a karo na biyu tinda gashi Baba Alhaji ya hura wuta kan batun auren Ya Ma’aruf da Sahariyya...”
Shiru Aunty B tai tamkar mai nazari kana tace “Bazai yuwu ki koma gidan Hafiz ba, bazan bari ba....”
Dubanta Zulfa’u tai da idanunta da sukai raurau “Aunty idan sukace na koma fah... Bazan iya bijire masu ba...”
Girgiza kai Aunty B tai had’ida gyara zama sosai “Toh ke Zulfa’u mai zai hana ki baiwa yaron nan Akram dama iyaye su shiga maganar tinda gashi naji Atika na cewa tin satin da ya shige yaketa damunki da batun turo magabatansa amma kink’i basa k’ofa, na tabbata idan sukaga kin tsaida manemi bazasu miki dole ba, saidai idan kuma har yanzu kina son Hafiz d’in ne....”
Fuzar da iska maras k’arfi Zulfah tai had’ida muskutawa “Aunty bazan b’oye maki ba, da fari bansan mai nakeji ba, I was so confused about Ya Hafiz amma yanzu ina mai tabbatar maki bana son Ya Hafiz, shi ma Akram banjin ina sonsa Aunty... Bansan menene na hanzarin ba, dadai sun barni zuwa wani d’an lokacin to get my head cleared...”
Sauk’e ajiyan zuciya Aunty B tai kana tace “Akram yaron kirki ne Zulfa’u kuma ni nan nasa anmin bincike akanshi and his background, baida wani aibu, mai zai hana ki bashi dama Zulfa’u, idan dai iyayenki sun matsa nidai a nawa shawarin da ki bari su maida aurenki da Hafiz gwara miki wannan yaro Akram... Amma fah shawarice... Ki natsu kiyi tunani kuma ki fad’iwa Ubangijinki ki fawwala masa lamranki domin zab’insa shine maki alkhairi...”
A hankali Zulfah ta jinjina kai kana tace “Toh Aunty zanyi yanda kikace zanyi tunanin... kuma zanyi addu’a dikda cewa cikin yinta nake ko yaushe....Na gode da shawarwarinki Aunty... thank you for always being there..”
D’an rungumeta Aunty B tai kana tace “Anything for you daughter... Allah Ubangiji ya miki zab’i mafi alkhairi...”
Zulfa’u ta amsada “Ameen Aunty na...”
***
Koda Sameer ya sami sak’on Wan mahaifin nasa bai k’asa a gwiwa ba ya amsa kiran nasa, saidai bai sami Baba Alhajin gida ba saiko Haule da yaranta, musamman Haule tasa Najah ta bud’e masa parlorn Baba Alhaji, sai wani nan nan dashi ake, Sameer bai mance farkon zuwansa gidan ba sanda ya buge Raihanah ya tadda Haule da wannan maras kunyar ‘yar nata da ake yunk’urin aura masa matsayin mata sun tasa Raihanah a gaba suna aibantata... Tinda ya shigo gidan gaba d’aya a tsare yake sosai, ganinsu ya kuma tuno masa abinda ya tadda suna ma Raihanah a wancan lokacin, kansa na bisa wayarsa Haule ta shigo tamkar zata zube ta masa sijjada, sai rawa jikinta keyi tana kuma tura k’eyar Najah tana fad’in tai sauri ta ije masa kayan motsa baki dake hannunta...
Najah dai girgiza kai kurum tai kana ta k’arasa ta aje masa tray d’in tana gaidashi... A tak’aice ya amsa sannan har lokacin fuskarsa babu walwala....
Ga mamakin Haule jira take yaji yace ina amaryarsa take, shiru kakeji saima sinkayo muryarsa tai yana tambayar Najah Baba Alhaji...
Najah tace “Ai ba dawo ba Yaya...”
Jinjina kai kurum yai kana ya dubi agogon hannunsa....
Haule ta watsawa Najah harara sanda take ficewa kana ta kutso kai ta shigo parlorn, baki har kunne take sakin murmushi da sallama...
A tak’aice Sameer ya gaidata don tuntuni baisan maiyasa tasu batazo d’aya da matar ba ko bayan da ya fahimci matar yayan babansa ne, ko hakan nada alak’a da saninda ya mata a fari ne sai Allah.... Dik yanda Haule taso tajasa da hira ta kasa samun fuska, harta firan kawo kayan lefe da shirinsa na biki dataita k’ok’arin bijiro dashi babu ko kamun kai Sameer bai amsa mata ba, k’arshe dai data gama kid’inta da rawarta mik’ewa tai tana fad’in “Ka saki jikinka fah kaci komai nan gidanku bara na kira maka Sahariyyar tana can tana shiryawa...”
D’an dakatar da ita yai da fad’in “A’a da kin barta don zuwan ba nata bane...”
Haule bata bari ya dasa aya ba tace “A’a karka damu tindadai kazo dole ta fito ku gaisa...” Kallo kurum yabi Haule dashi yanda take rawar k’afa har ta fice...
A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya yana mai ayyanawa cikin zuciyarsa “What have you gotten yourself into Sameer... Baka gama da problem d’in Siyama ba ga wani na kunno maka kai....” a hankali ya fuzar da iska mai zafin gaske yana mai ayyanawa cikin zuciyarsa he’s doing this for the sake of the family, he cannot allow his family to fall apart bayan k’unci da suka fuskanta a lokacin da ya b’ace, he has to sacrifice and do what they ask him to do, for the sake of everybody’s happiness....
Yana tsaka da tunanin wayarsa ta d’auki ruri...
Sanda Sahariyya ta shigo parlorn waya yake dan haka bai amsa sallamarta ba, sai wani sanne sanne kai take ita a dole an fito zance wajen saurayi....
Duba guda ya mata ya d’auke kansa, har lokacin waya yake....
Sahariyya ta k’arasa ta zauna a kujera mai kallon nasa.... Sai faman sakin murmushi take tana k’irga ‘yan yatsunta yawa mutumiyar arzikin gaske...
Lokaci guda taga ya mik’e yana fad’i cikin wayar “I’ll be on my way...”
Zunbur Sahariyya ta mik’e tana binsa da kallon mamaki....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................ DA DABO_
*79*