Sashe 34
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jin ta kasa furta komai sai aikin kuka yasa Sameer dake watsa mata mummunar kallo ci gaba da fad’in “I’ve shown you nothing but love.... Wannan shine abinda zaki sakamin dashi, ki hanani ganin gudan jinina, claiming you love me... Idan haka ake soyayya Siyama bana k’aunar irin soyayyar da kike mun, bansan reasons d’inki ba kuma banaso na sani...Amma ki sani ko ba dad’e ko ba jima zanga gudan jinina da yardar Allah...” Daga haka bai kuma cewa komai ba sai mik’ewa da yayi ya fice daga gidan gaba d’aya...
Siyama kaw kwanciya tayi a wajen tana kuka sosai, ganin kuka bazai ficceta ba ya sanyata mik’ewa ta nufi gida a fujajan..
Ammi saida ta razana da ganinta haka..
Cikin tsananin kuka da tashin hankali ta rungume Ammi tana fad’in “Ammi I cant lose him, I love him so much.... Please do something Ammi...”
Ammi ta rungumeta sosai cikeda tashin hankali take fad’in “Mai ya sami Sameer d’in... Talk to me Siyama, ina Sameer d’in...”
Siyama ta kasa furta komai sai shesshek’an kuka da take, da k’yar ta iya fad’iwa Ammi duk abinda ya faru kana ta k’arada “Ammi ban tab’a ganinshi cikin yanayin fushi irin wannan ba, Ammi ki ceceni kada ya rabu dani...” Ta k’arashe tana jijjiga Ammin...
Rungumeta Ammi ta kumayi tana lallashi “Siyama irin abinda nake jiye maki kenan amma shegen taurin kunne irin naki kikak’i ki saurareni, kin gani koh maganin hana d’aukan ciki kawai ya gani yayi fushi dake irin haka, inaga yasan cewa kin cire mashi cikinshi.. Mai kike tunanin zaiyi...?”
Cikin kuka Siyama ke fad’in “I don’t wanna think about that Ammi, nidai kawai save my marriage please...”
Jinjina kai Ammi tai kana tace “Ki kwantar da hankalinki ki daina kukan haka, karma ki bari Daddynki yaji wannan batu, ni nasan mai zanyi...”
Da wad’annan kalamai Ammi ta kwantar da hankalin Siyama har ta d’an samu tayi shiru amma kam ta k’ule a d’aki can k’asar zuciyarta bata daina fargaba da zullumin hukuncin da Sameer ka iya yankewa akanta ba dukda tasan cewa duk tsananin fushi dole ya yafe mata tinda yana sonta...
Bayan sallan Magrib Ammi tayi gidansu Sameer da k’orafin cewa Sameer na wulak’anta mata d’iya ko Hajiya Fatahiyyah ta d’au mataki ko ta fasa k’wai ta sanar da Sameer komai...
Hajiya Fatahiyya Momyn Sameer ta d’ago idanu a firgice tana duban mahaifiyar Siyama kana tace “Farida kar kimin haka bamuyi haka dake ba......”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*29*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ammi ta murmusa kana tace “Idan kaw haka ne ki kirawo d’anki kija masa kunne akan Siyama, bai isa ya wulak’anta min d’iya ba...”
Momy ta murmusa kana ta zauna saman kujera tace “Shin ke maiyasa bazakiyi fad’awa d’iyarki ba wacce ko girki batasan tayiwa mijinta, shin Farida bazaki tambayi naki d’iyar ba mai takeyiwa mijinta.... Sanin kanki ne Siyama is a spoilt brat bacin soyayya babu abinda Sameer zaiyi da ita...”
Murmushi Ammi tayi kana ta mik’e tsaye tana gyara mayafi tace “Hajiya Fatahiyya this conversation won’t take us anywhere, inaga lokaci yayi da Sameer ya kamata yasan komai, koshi wanene... Sirrin da ya kamata ya sani 30 years back...”
Momy ta mik’e a fusace tana fad’in “Ke Farida ki iya bakinki, kijida taki d’iyar amma karki kuskura ki gusarwa d’ana farin cikin dana gina rayuwarsa bisa...”
Hajiya Frida ta kuma murmusawa kana tace “Let’s see mai Sameer zaice idan ya fahimci matar da ya d’auketa da tsananin daraja da mahimmacin has been lying to him his whole life.....”
Momy na tsananin huci take fad’in “Don’t even try that Farida, wllhi karki kuskura... Sameer is my son...”
Daidai lokacin da sukaji an bud’e k’ofa an shigo....
Gaba d’aya suka juya a tare suna dubanshi, idanunsa suna kuma zuban wasu irin ruwa mai tsananin zafi....
Momy da tuni hawaye sun soma k’ok’arin ciko idanunta saurin kauda fuskarta tai daga barin dubansa....
A hankali Sameer yaci gaba da takowa cikin parlorn tamkar wanda ruwa ya shanye haka yake tafiyar....
“Mummy...” Ya kirawo sunanta a hankali cikin wani irin raunanniyar murya...
Kasa juyowa ta dubesa tai saima dad’a rintse idanunta da tayi tana mai k’ok’arin saita kanta...
Sameer yasa hannu ya share hawayen da suka zubo masa kana ya kuma cewa “Mummy is that true, Mummy please talk to me.... Da gaske ne baku kuka haifeni ba....?”
K’ok’arin saita kanta tayi kana ta k’araso ta rik’o hannayensa guda biyu, a hankali take furta “Sameer kada ka yarda da abinda take cewa, we are your real parents, I’m your mother... Bansan meyasa take fad’in haka ba... Shin sab’ani kuka samu da Siyama...?”
K’uri ya mata idanunsa babu alamun wasa ya kuma furta “Momy tell me the truth... Ki fad’a mun gaskiya, who my real parents are....”
Kamo hannayensa tai suka zauna bisa sofa don already lokacin Ammin Siyama ta fice...
“Son look into my eyes, I’m telling you the truth....Sameer kai d’ana ne... Please believe me Son...” Ta k’arashe tana shafa fuskarsa hawaye na k’ok’arin ciko idanunta...
A hankali ya rungumeta badon ya yarda da abinda take fad’i masa ba sai don bazai juri ganinta cikin hawaye ba sannan baiso zuciyarsa ta k’aryata masa ita macen da yake tsananin k’auna sama da kowa a duniya, wacce ya girma ya santa a matsayin mahaifiya a gareshi...
Jin hawayenta saman kafad’unsa ya kuma karyar masa da zuciya...
A hankali yake furta “I believe you Momy please ki daina hawayen nan....”
Momy ta d’ago tana dubansa kana tace “Bansan maiyasa Farida tace haka ba Son, kodai sab’ani ka samu da Siyama...?”
Shiru yayi tamkar mai tunani kana ya k’ak’aro murmushi ya sakar mata yace “Momy idan wani baison had’a jini dakai maybe kanada wani bak’in tabo ne... Ki kwanta ki huta you this isn’t good for your blood pressure...” Daga haka mik’ewa yayi jikinsa a sanyaye ya fice yayinda Momy ta bishi da kallo har ya fice daga parlorn tana tunanin mai Sameer yake son fad’i....
Yana ficewa sashensa dake cikin gidan ya nufa yai zaune a parlor yana tunanin rayuwa, a hankali ya lumshe idanunshi had’ida d’aura hab’ar shi saman hannayenshi guda biyu....
Zancen zuci ya shigayi shi kad’ai yana nazari.... What if da gaske su Momy basune iyayenshi ba, what if Ammin Siyama ta sanar da Siyama cewa shid’in maras asaline kar ta bari rabo ya ratsa tsakaninsu sabida bak’in fenti da rayuwarsa ke shafe da ita....? Wasu irin hawaye masu d’umi yaji suna gangaro mashi, shi kad’ai sai tauyin kanshi ne ke taso mashi, ya rasa tunanin meye zaiyi, shin abubuwa da suke kan faruwa dashi a garin Kano zaiyi tunanin warwarewa ko kuwa na nan gida Kaduna...?
Baisan da wanne zai fara ba sabida kwanyarsa gaba d’aya ji yayi ta cushe, wani tunani ne ya fad’o masa ya mik’e jiki babu laka ya fad’a bathroom ya d’an watsa ruwa ko zai d’an wartsake, yana fitowa sashen Momy ya nufa yanda ya tadda bata a parlorn da alama ta haura sama hakan sai yafi masa sauk’i, cikin sauri ya k’arasa ma’ajiyan keys na gidan ya zari key d’in sashen Daddy ya fice....
Sauri sauri yake gudanar da al’maran nasa tamkar mai tsoron kada wani ya tadda shi, kai tsaye master bedroom d’in Daddy ya nufa kana ya shige bathroom, ma’ajiyan kayan wanke baki na Daddy ya nufa ya d’auki toothbrush d’in Daddy...
Ya jima yana juya toothbrush d’in kafin ya bud’e ‘yar k’aramar jaka ta leda transparent mai d’an zip ya saka toothbrush d’in ciki, sauri sauri ya fito ya kulle sashen ya maida mabud’in ma’ajiyansa...
Ko sashen nasa bai koma ba ya nufi motarsa da ‘yar jakar da toothbrush d’in ke ciki ya fice....
Bai zarce ko ina ba sai asibitinsu da a baya yake aiki....
Sameer ya jima zaune cikin mota yana tunanin abinda yake niyyan yi, tuhumar kansa ya shigayi anya yayi dai dai, shin idan yaga abinda zai karyar masa da zuciya fah....?
Ya kuma lumshe idanu yana tuna abinda Siyama ta mishi, his heart’s already broken gwara kawai ya k’arasa abinda ya fara, da alama ya jima cikin duhu lokaci yayi da haske zai bayyana cikin rayuwarsa.....
Ajiyan zuciya ya sauk’e kana yasa hannu ya tsinko sumar kansa guda ya nad’eta cikin leda kafin ya nufi cikin asibitin....
Kasancewar biyar na yamma ta gauta shiyasa ya tadda ma’aikatan wanda suka gama morning duty nakan tafiya, gaba d’aya sai murnar ganinsa suke, wani matashi ma’aikacin laboratory ne ya tsaya suna gaisawa da Sameer don tuntuni sosai suka saba ya d’auki Dr Sameer tamkar Yaya....
Auwal yace “Dr banjin lab d’in na bud’e wani abu ne kake so...?”
Sameer ya mik’o masa ‘yar jakan hannunsa kana yace “Auwal I need a DNA result of this ASAP....”
Auwal ya d’anyi shiru kana ya jinjina kai yace “Ok Dr first thing tomorrow morning, the result will be ready in sha Allah....”
Sameer ya jinjina kai kana yace “Good... Idan ya zama ready kawai ka kirani zanzo na karb’a...”
Auwal ya d’an shafi sumarsa yace “Haba Dr ai location kawai zaka fad’i min na kawo maka...”
Sameer ya d’an murmusa kad’an kana yace “Kar ka damu kawai ka kirani zanzo na karb’a... Na gode koh...” Ya k’arashe yana d’an bubbbuga kafad’unsa...
Auwal ya jinjina kai kana yace “Alright Dr yanda kace, sai kaji daga gareni....”
Daga haka sallama sukai Sameer ya nufi motarsa kira na shigo mashi, ganin Siyama ce mai kiran ya sanyashi saka wayan a silent....Har Auwal ya soma tafiya ya kuma kiran sunansa yace “This is confidential, ko Sultan banso ya sani....”
Auwal ya jinjina kai yace “In sha Allah Dr...”
Sameer ya kuma jinjina kai kana yayi key wa motarsa....
Bai zarce ko ina ba sai gidansu Sultan don Auwal ya sanar dashi Dr Sultan yau trough out bai shiga asibitin ba....
Wayan Sultan d’in ya shiga kira sanda yayi zaune saman bayan motarsa....
***
“Ammi ya kukai, ina Sameer....?” Siyama ta tambaya tana duban Ammin da gaba d’aya ta zamto wata iri....
“Ammi talk to me dan Allah...”
Ta d’an k’ara fad’i tana kamo hannayen Ammin cikeda damuwa...
Kallo Ammi ta bita dashi kana tace “Siyama na goyi bayanki d’ari bisa d’ari kada ki tab’a yarda ki d’auki cikin Sameer, ki ci gaba da shan magani kada ki fasa....”
Siyama kaw kwanciya tayi a wajen tana kuka sosai, ganin kuka bazai ficceta ba ya sanyata mik’ewa ta nufi gida a fujajan..
Ammi saida ta razana da ganinta haka..
Cikin tsananin kuka da tashin hankali ta rungume Ammi tana fad’in “Ammi I cant lose him, I love him so much.... Please do something Ammi...”
Ammi ta rungumeta sosai cikeda tashin hankali take fad’in “Mai ya sami Sameer d’in... Talk to me Siyama, ina Sameer d’in...”
Siyama ta kasa furta komai sai shesshek’an kuka da take, da k’yar ta iya fad’iwa Ammi duk abinda ya faru kana ta k’arada “Ammi ban tab’a ganinshi cikin yanayin fushi irin wannan ba, Ammi ki ceceni kada ya rabu dani...” Ta k’arashe tana jijjiga Ammin...
Rungumeta Ammi ta kumayi tana lallashi “Siyama irin abinda nake jiye maki kenan amma shegen taurin kunne irin naki kikak’i ki saurareni, kin gani koh maganin hana d’aukan ciki kawai ya gani yayi fushi dake irin haka, inaga yasan cewa kin cire mashi cikinshi.. Mai kike tunanin zaiyi...?”
Cikin kuka Siyama ke fad’in “I don’t wanna think about that Ammi, nidai kawai save my marriage please...”
Jinjina kai Ammi tai kana tace “Ki kwantar da hankalinki ki daina kukan haka, karma ki bari Daddynki yaji wannan batu, ni nasan mai zanyi...”
Da wad’annan kalamai Ammi ta kwantar da hankalin Siyama har ta d’an samu tayi shiru amma kam ta k’ule a d’aki can k’asar zuciyarta bata daina fargaba da zullumin hukuncin da Sameer ka iya yankewa akanta ba dukda tasan cewa duk tsananin fushi dole ya yafe mata tinda yana sonta...
Bayan sallan Magrib Ammi tayi gidansu Sameer da k’orafin cewa Sameer na wulak’anta mata d’iya ko Hajiya Fatahiyyah ta d’au mataki ko ta fasa k’wai ta sanar da Sameer komai...
Hajiya Fatahiyya Momyn Sameer ta d’ago idanu a firgice tana duban mahaifiyar Siyama kana tace “Farida kar kimin haka bamuyi haka dake ba......”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*29*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ammi ta murmusa kana tace “Idan kaw haka ne ki kirawo d’anki kija masa kunne akan Siyama, bai isa ya wulak’anta min d’iya ba...”
Momy ta murmusa kana ta zauna saman kujera tace “Shin ke maiyasa bazakiyi fad’awa d’iyarki ba wacce ko girki batasan tayiwa mijinta, shin Farida bazaki tambayi naki d’iyar ba mai takeyiwa mijinta.... Sanin kanki ne Siyama is a spoilt brat bacin soyayya babu abinda Sameer zaiyi da ita...”
Murmushi Ammi tayi kana ta mik’e tsaye tana gyara mayafi tace “Hajiya Fatahiyya this conversation won’t take us anywhere, inaga lokaci yayi da Sameer ya kamata yasan komai, koshi wanene... Sirrin da ya kamata ya sani 30 years back...”
Momy ta mik’e a fusace tana fad’in “Ke Farida ki iya bakinki, kijida taki d’iyar amma karki kuskura ki gusarwa d’ana farin cikin dana gina rayuwarsa bisa...”
Hajiya Frida ta kuma murmusawa kana tace “Let’s see mai Sameer zaice idan ya fahimci matar da ya d’auketa da tsananin daraja da mahimmacin has been lying to him his whole life.....”
Momy na tsananin huci take fad’in “Don’t even try that Farida, wllhi karki kuskura... Sameer is my son...”
Daidai lokacin da sukaji an bud’e k’ofa an shigo....
Gaba d’aya suka juya a tare suna dubanshi, idanunsa suna kuma zuban wasu irin ruwa mai tsananin zafi....
Momy da tuni hawaye sun soma k’ok’arin ciko idanunta saurin kauda fuskarta tai daga barin dubansa....
A hankali Sameer yaci gaba da takowa cikin parlorn tamkar wanda ruwa ya shanye haka yake tafiyar....
“Mummy...” Ya kirawo sunanta a hankali cikin wani irin raunanniyar murya...
Kasa juyowa ta dubesa tai saima dad’a rintse idanunta da tayi tana mai k’ok’arin saita kanta...
Sameer yasa hannu ya share hawayen da suka zubo masa kana ya kuma cewa “Mummy is that true, Mummy please talk to me.... Da gaske ne baku kuka haifeni ba....?”
K’ok’arin saita kanta tayi kana ta k’araso ta rik’o hannayensa guda biyu, a hankali take furta “Sameer kada ka yarda da abinda take cewa, we are your real parents, I’m your mother... Bansan meyasa take fad’in haka ba... Shin sab’ani kuka samu da Siyama...?”
K’uri ya mata idanunsa babu alamun wasa ya kuma furta “Momy tell me the truth... Ki fad’a mun gaskiya, who my real parents are....”
Kamo hannayensa tai suka zauna bisa sofa don already lokacin Ammin Siyama ta fice...
“Son look into my eyes, I’m telling you the truth....Sameer kai d’ana ne... Please believe me Son...” Ta k’arashe tana shafa fuskarsa hawaye na k’ok’arin ciko idanunta...
A hankali ya rungumeta badon ya yarda da abinda take fad’i masa ba sai don bazai juri ganinta cikin hawaye ba sannan baiso zuciyarsa ta k’aryata masa ita macen da yake tsananin k’auna sama da kowa a duniya, wacce ya girma ya santa a matsayin mahaifiya a gareshi...
Jin hawayenta saman kafad’unsa ya kuma karyar masa da zuciya...
A hankali yake furta “I believe you Momy please ki daina hawayen nan....”
Momy ta d’ago tana dubansa kana tace “Bansan maiyasa Farida tace haka ba Son, kodai sab’ani ka samu da Siyama...?”
Shiru yayi tamkar mai tunani kana ya k’ak’aro murmushi ya sakar mata yace “Momy idan wani baison had’a jini dakai maybe kanada wani bak’in tabo ne... Ki kwanta ki huta you this isn’t good for your blood pressure...” Daga haka mik’ewa yayi jikinsa a sanyaye ya fice yayinda Momy ta bishi da kallo har ya fice daga parlorn tana tunanin mai Sameer yake son fad’i....
Yana ficewa sashensa dake cikin gidan ya nufa yai zaune a parlor yana tunanin rayuwa, a hankali ya lumshe idanunshi had’ida d’aura hab’ar shi saman hannayenshi guda biyu....
Zancen zuci ya shigayi shi kad’ai yana nazari.... What if da gaske su Momy basune iyayenshi ba, what if Ammin Siyama ta sanar da Siyama cewa shid’in maras asaline kar ta bari rabo ya ratsa tsakaninsu sabida bak’in fenti da rayuwarsa ke shafe da ita....? Wasu irin hawaye masu d’umi yaji suna gangaro mashi, shi kad’ai sai tauyin kanshi ne ke taso mashi, ya rasa tunanin meye zaiyi, shin abubuwa da suke kan faruwa dashi a garin Kano zaiyi tunanin warwarewa ko kuwa na nan gida Kaduna...?
Baisan da wanne zai fara ba sabida kwanyarsa gaba d’aya ji yayi ta cushe, wani tunani ne ya fad’o masa ya mik’e jiki babu laka ya fad’a bathroom ya d’an watsa ruwa ko zai d’an wartsake, yana fitowa sashen Momy ya nufa yanda ya tadda bata a parlorn da alama ta haura sama hakan sai yafi masa sauk’i, cikin sauri ya k’arasa ma’ajiyan keys na gidan ya zari key d’in sashen Daddy ya fice....
Sauri sauri yake gudanar da al’maran nasa tamkar mai tsoron kada wani ya tadda shi, kai tsaye master bedroom d’in Daddy ya nufa kana ya shige bathroom, ma’ajiyan kayan wanke baki na Daddy ya nufa ya d’auki toothbrush d’in Daddy...
Ya jima yana juya toothbrush d’in kafin ya bud’e ‘yar k’aramar jaka ta leda transparent mai d’an zip ya saka toothbrush d’in ciki, sauri sauri ya fito ya kulle sashen ya maida mabud’in ma’ajiyansa...
Ko sashen nasa bai koma ba ya nufi motarsa da ‘yar jakar da toothbrush d’in ke ciki ya fice....
Bai zarce ko ina ba sai asibitinsu da a baya yake aiki....
Sameer ya jima zaune cikin mota yana tunanin abinda yake niyyan yi, tuhumar kansa ya shigayi anya yayi dai dai, shin idan yaga abinda zai karyar masa da zuciya fah....?
Ya kuma lumshe idanu yana tuna abinda Siyama ta mishi, his heart’s already broken gwara kawai ya k’arasa abinda ya fara, da alama ya jima cikin duhu lokaci yayi da haske zai bayyana cikin rayuwarsa.....
Ajiyan zuciya ya sauk’e kana yasa hannu ya tsinko sumar kansa guda ya nad’eta cikin leda kafin ya nufi cikin asibitin....
Kasancewar biyar na yamma ta gauta shiyasa ya tadda ma’aikatan wanda suka gama morning duty nakan tafiya, gaba d’aya sai murnar ganinsa suke, wani matashi ma’aikacin laboratory ne ya tsaya suna gaisawa da Sameer don tuntuni sosai suka saba ya d’auki Dr Sameer tamkar Yaya....
Auwal yace “Dr banjin lab d’in na bud’e wani abu ne kake so...?”
Sameer ya mik’o masa ‘yar jakan hannunsa kana yace “Auwal I need a DNA result of this ASAP....”
Auwal ya d’anyi shiru kana ya jinjina kai yace “Ok Dr first thing tomorrow morning, the result will be ready in sha Allah....”
Sameer ya jinjina kai kana yace “Good... Idan ya zama ready kawai ka kirani zanzo na karb’a...”
Auwal ya d’an shafi sumarsa yace “Haba Dr ai location kawai zaka fad’i min na kawo maka...”
Sameer ya d’an murmusa kad’an kana yace “Kar ka damu kawai ka kirani zanzo na karb’a... Na gode koh...” Ya k’arashe yana d’an bubbbuga kafad’unsa...
Auwal ya jinjina kai kana yace “Alright Dr yanda kace, sai kaji daga gareni....”
Daga haka sallama sukai Sameer ya nufi motarsa kira na shigo mashi, ganin Siyama ce mai kiran ya sanyashi saka wayan a silent....Har Auwal ya soma tafiya ya kuma kiran sunansa yace “This is confidential, ko Sultan banso ya sani....”
Auwal ya jinjina kai yace “In sha Allah Dr...”
Sameer ya kuma jinjina kai kana yayi key wa motarsa....
Bai zarce ko ina ba sai gidansu Sultan don Auwal ya sanar dashi Dr Sultan yau trough out bai shiga asibitin ba....
Wayan Sultan d’in ya shiga kira sanda yayi zaune saman bayan motarsa....
***
“Ammi ya kukai, ina Sameer....?” Siyama ta tambaya tana duban Ammin da gaba d’aya ta zamto wata iri....
“Ammi talk to me dan Allah...”
Ta d’an k’ara fad’i tana kamo hannayen Ammin cikeda damuwa...
Kallo Ammi ta bita dashi kana tace “Siyama na goyi bayanki d’ari bisa d’ari kada ki tab’a yarda ki d’auki cikin Sameer, ki ci gaba da shan magani kada ki fasa....”