Sashe 63
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata Innar Hajiya ce ta rik’esa tana basa baki tana fad’in yayita karanto innalillahi.... Inaaa Hafiz sai fuzgewa yake yana tambayan ina aka b’oye masa d’iya... Fad’i yake “Hajiya nasan baki son zamanta a nan fine na maki alk’awari daga rana mai kaman ta yau kin gama rik’onta zan d’auketa na tafi da ita.... Ni zan rik’eta zan rik’e kayana... Please ki fito min da ita I know she’s in there ku bani d’iyata please....” Ya k’arashe yana nuni da uwar d’akin Hajiya....
Innar Hajiya ta kuma jaddada masa cewa d’iyarsa ta rasu ta rasu babu dawowa...., Hajiya ta cafe da masifa tana mai furta “Da kin k’yaleshi ya shigo d’akin ya duba tinda ya tab’a ganin yanda akai k’aryar mutuwa...” Ta k’arashe tana muzurai...
Hafiz durk’ushe k’asa rungume da kayan wasan yarinyarsa yake hawaye, lokaci guda yake furta “I only want to be with my daughter....” Wajen yayi shiru banda sautin fitar kukan Hafiz da kake iya jiyowa.... Ya d’ago idanunsa masu zuban hawaye yana duban mahaifiyarsa kana yace “Hajiya maiyasa akai mata sutura ba tareda an sanar dani ba.. Mai yasa aka kaita makwancinta ba tareda na mata addu’a ba... Mai yasa ba’a bari nayi bankwana da d’iyata ba...?” Ya k’arashe hawaye na kuma gangaro masa....
Fuska a tab’e Hajiya tace “Cikin abinda ka lissafa babu wanda ba’ayi ba, wayarka an kira yafi sau babu adadi kai har d’an aike an tura gidanka akaji gidan a rufe toh so kake a barta haka nan ayita jiranka sai sanda kaga dama ko mai...?” Bai kuma furta komai ba sai rintse idanunsa da yayi da k’arfin gaske...
Sahariyya dake lab’e jikin labule tana lek’ensa sai faman yatsina baki take d’igon tausayi ko nadama babu a tattareda ita
Fuskarsa jazir ya kuma d’agowa ya dubi mahaifiyarsa yana mai sakin huci a hankali, cikin dakakkiyar murya yace “Hajiya mai ya sameta... Mai yayi sanadin rayuwarta...?”
Sahariyya da Hajiya suka had’a ido Sahariyyan na aikawa Hajiya wani irin duba... Take Hajiya ta shiga inda inda tana fad’in “Yo mai kuwa ya kasheta banda ajali ko kashe maka d’iyarka zamuyi... inyi, ko rashin yardar naka takai haka ne...?”
Bai kuma cewa komai ba sai mik’ewa da yayi tamkar wanda ruwa ya shanye ya fice ba tareda ya kuma furta koda kalma ba... Naja’atu tabi bayansa cikeda tausayawa har ya fice kana ta maido da dubanta ga Hajiya da Sahariyya tanai masu muguwar kallo cikin sauri ta fice tana mai girgiza kai... Sahariyya ta rakata da muguwar kallo kana ta tab’e baki ta koma cikin d’aki tana mai danna earpiece a kunnenta ta saki sauti cikin kunnuwanta....
***
Zaune suke saman dakali k’ofar gida sai zuba zance suke irinta matasa, akasarin firan ya danganci siyasa ne da kuma wasanni k’wallon k’afa.... Daidai sanda mai amalanken rake yazo shigewa d’aya daga cikin matasan mai suna Auwalu ya tsaida mai amalanken, tuni mai rake ya gangaro yanda matasan ke zaune...
Auwalu ya dubi Akram da hankakinsa kega wayar salulansa yace “Yauwa ga mai raken na kira a saya mana muji dadin yin zance ko ya kukace...?”
Gaba d’aya sauran matasan sukace haka ne...
Akram ya d’an dube abokan nasa a kaikaice kana yace “Amma dai bani na tsaida mai rake ba...?”
“Koma bakai bane dole ka saya mana tinda mai gidanka na nema muk’ami idan ba haka ba mu hanaku k’uriunmu ko ya kuka ce..?” Nan ma suka amsa da wannan haka take, basu jira cewar Akram ba suka shiga zab’en rake mai rake na fere masu radio na kunnensa yana faman saurare...
Akram fad’i yake “Kaga Malam ko wanne cikinsu sai ya biyaka kud’inka....”
Mai rake na murmushi yake fad’in “Ai idan zasu zab’i MUTALLAB zab’in talakwa ko amalanken raken sukeso gaba d’aya sai na basu....”
Suka kekate da dariya gaba d’aya harda shi Akram d’in, tabbas ya sani Mai gidansa yanada magoya baya da dama wanda idan za’ayi zab’en gaskiya tsakani da Allah zai iyaci...
Akaci gaba da firan siyasa harda mai rake radio na bisa aiki, nan kuwa aka soma program d’in Muryar ‘yanci, Akram ya bud’e kunnuwa sosai yana jira yaji muryarta, baiji muryar tata ba sai na abokan aikinta daga bisani yaji d’aukacin ma’aikatan gidan radio d’in na mik’a mata sak’on ta’aziya na rashin d’iyarta da tayi... Tsananin mamaki ya cika Akram... Wai dama tanada aure harda yara...? Shi kad’ai yake tambayar kansa cikin zuciyarsa.... Bai kuma bi takan firan tasu ba har ya sallami mai rake ya basa kud’insa ya kuma ce ya rik’e canjin domin gudan dubu ne a aljihunsa... Matasan suka kuma ihu suna wasa shi suna fad’in sai Uban gidansa ko garin bakowa...
Akram dai gaba d’aya zuciyarsa ta tafi wata duniyar...
Abokinsa da suka taso tare a unguwar mai suna Yusuf shi ya fahimci nisan zango da Akram d’in yayi....
D’an dafasa kad’an yayi kana yace “Abokina akwai matsala ne...?”
Akram ya d’ago ya dubi Yusuf kana yace “Muje daga gefe...”
Babu musu Yusuf ya mik’e yabi bayan abokin nasa....
Daga can tsallake suka tsaya k’ofan gidansu Yusuf....
Yusuf yace “Akram lafiya dai ko...?”
Akram yace “Yusuf dama tanada aure...?”
Cikin rashin gane inda ya dosa yace “Aure... wace kenan...?”
Akram ya d’an shafi goshinsa yace “Zulfa’u Mailafiya ta gidan radion Muryar ‘yanci....”
Yusuf ya d’an murmusa a hankali kana yace “Aw dama baka sani ba...? Eh toh tanada aure batada aure...”
Akram ya dubesa da alaman tambaya kana yace “Ban gane ba what do you mean tanada aure batada aure...?”
Yusuf yace “From what I know sun rabu da mijin nata kwanakin baya can, kasan Atika abokiyar aikinta k’awar Saliha k’anwatace....”
Akram ya jinjina kai kana yace “I want to know more about her,...”
Yusuf ya d’an murmusa kana yace “Kar ka damu abokina zanyi k’ok’arina, zansa Saliha ta sanar da k’awarta zamu kaiwa Zulfa’u ta’aziya da sunan jamk’iyarku ko ya ka gani...?”
Akram ya d’anyi shiru kana yace “Amma kanaga bazatayi tunani siyasa ya kawo mu ba....?”
Yusuf yace “Haba Akram kasan MUTALLAB yanada magoya baya da dama yau ko siyasarce takaimu na tabbata bazamuji kunya ba duk yanda mukaje da sunansa....”
Akram ya d’anyi shiru na wasu dak’ik’ai kana yace “Shikenan Allah shi wuce mana gaba..”
Yusuf ya amsa da Ameen kana suka nufi cikin gidan gaba d’aya....
***
Tinda suka iso Kaduna suka had’a k’arya da gaskiya suka fad’iwa Ammi, Siyama harda cewa Khalid harda ita ya had’e ya daka...
Ammi ta dafe k’irji tana salallami...
“Khalid ne ya d’aga hannu ya dakeki...?” Ta kuma tambayar Siyamar...
Cikeda makirci Siyama tace “Aw mamaki kike sha Ammi, Toh wllhi Khalid ya shige duk yanda kike tunani, baiga darajan girme masa da nayi a haife ba yasa hannu ya dakeni nima don kawai nace ya rabu da wancan dangin mayun....”
Yesmin dake gefe da kumburarren bakinta tace “Wllhi Ammi ko shakka babu an juye masa kwanya bakiga yanda ya fice a hayyacinsa ba gaba d’aya....”
Ammi tai k’wafa tace “Dad na hanya ai shine kawai maganinsa don wllhi bazai janyo mana kayan kunya ba....” Ta k’arashe tana mai kuma dialing layin Khalid d’in
Kubura dake lab’e jikin staircase sai faman k’unshe dariyarta take tana kwaikwayan maganan Yesmin da yanda bakinta ya kumbura ya koma gefe guda, sai murna take tana tsallen Allah shi k’ara....
A daren Khalid ya dawo garin Kaduna saidai ko sashen Amminsa bai shiga ba, washe gari ma bai fito ba har saida ya tabbata mahaifinsa ya dawo don yana ganin sanda driver ya tafi airport d’aukosa, baiji mamakin ganin Khalid d’in baizo d’aukansa ba don tun a waya Ammi ta zayyane masa komai duk halinda ake ciki, shi kad’ai yake sakin huci har sai yafi Ammi fushi da lamarin musamman da shike an tab’o sanyin idaniyarsa Siyama wacce a duniya yak’i jinin yaga fushinta sabida tsananin sonta da yake....
Suna zaune gaba d’aya a parlorn ya sako kai, ko ba’ace ba yasan fitowarsa ake jira....
Kallo d’aya ya watsawa Siyama ya d’auke kai daga barin duban nata.... Can k’asa gefen k’afafun mahaifinsa ya k’arasa ya zauna...
A hankali ya furta “Daddy sannu da zuwa... Ammi ina kwana...?”
Baikai aya ba Ammi ta katsesa da fad’in “Da ban kwana ba zaka ganni...? Nace da ban kwana ba zaka ganni...? Ince kai ka zama sallamemme.... Ace tun jiya ka dawo gidan nan ka kasa lek’owa mu gaisa sabida ta zuba maka a ruwa kasha koh.... Harda wulak’anta ‘yan uwanka don kawai sun fad’i gaskiya...? Idan ka zab’eta sama da ‘yan uwanka ne sai ka tattara ka koma can ka zama cikakken sallamemme...” Siyama ta k’arada “Ahtoh fad’a masa dai Ammi..”
Daddy ya cafi zancen da ambato sunan Khalid...
“Khalid...!”
Khalid ya d’ago a hankali yana dubansa kana yace “Na’am Daddy...”
“Dad yaci gaba da fad’in “Khalid meke faruwa da rayuwar ka....?”
A hankali ya furta “I’ll explain everything Dad....”
Dakatar dashi yayi ta hanyar d’aga masa hannu kana yace “Ba sai ka min bayanin komai ba, mahaifiyarka ta sanar dani, ba kuma zan bari ka kawo mana abin fad’i a dangi ba, bazaka kawo mana yarinya maras cikakken asali ba da sunan mata, ga mata da yawa a duniya, kaje duk yanda kakeso ka kawo mace idan har family background d’inta nada kyau ni zan aura maka amma banda yarinyar da aka tabbatar batada cikakken asali balle tarbiya...”
Khalid ya dubi Ammi da Siyama da tsananin mamakin jin yanda suka had’awa Dad zance ya hau kai ya zauna... Ammi ta katse hanzarin nasa da fad’in “Ga k’awarsa Yesmin babu abinda ya rasa mai zai kaisa wani duniya neman mace...”
Daddy yace “Kaji koh... Inaso kamin rantsuwa babu kai babu wancan yarinyar sannan zaka auri ‘yar uwarka Yesmin....”
Khalid ya d’ago da mamaki yana duban mahaifinsa kana yace “Daddy rantsuwa fah kace....? Daddy it doesn’t have to reach this point...”
Ammi tace “K’warai kuwa it does ta hakane kawai zamu amince ka rabu da wancan tsinanniyar yarinyar.... Zaka rantse ne kokuwa...”
Khalid ya dubi mahaifiyarsa kurum ba tareda ya iya furta koda kalma ba...
Dad yace “K’yalesa tinda bazaiyi abinda mu muke so ba a matsayinmu na iyayensa muma bazamuyi abinda yakeso ba...”
Innar Hajiya ta kuma jaddada masa cewa d’iyarsa ta rasu ta rasu babu dawowa...., Hajiya ta cafe da masifa tana mai furta “Da kin k’yaleshi ya shigo d’akin ya duba tinda ya tab’a ganin yanda akai k’aryar mutuwa...” Ta k’arashe tana muzurai...
Hafiz durk’ushe k’asa rungume da kayan wasan yarinyarsa yake hawaye, lokaci guda yake furta “I only want to be with my daughter....” Wajen yayi shiru banda sautin fitar kukan Hafiz da kake iya jiyowa.... Ya d’ago idanunsa masu zuban hawaye yana duban mahaifiyarsa kana yace “Hajiya maiyasa akai mata sutura ba tareda an sanar dani ba.. Mai yasa aka kaita makwancinta ba tareda na mata addu’a ba... Mai yasa ba’a bari nayi bankwana da d’iyata ba...?” Ya k’arashe hawaye na kuma gangaro masa....
Fuska a tab’e Hajiya tace “Cikin abinda ka lissafa babu wanda ba’ayi ba, wayarka an kira yafi sau babu adadi kai har d’an aike an tura gidanka akaji gidan a rufe toh so kake a barta haka nan ayita jiranka sai sanda kaga dama ko mai...?” Bai kuma furta komai ba sai rintse idanunsa da yayi da k’arfin gaske...
Sahariyya dake lab’e jikin labule tana lek’ensa sai faman yatsina baki take d’igon tausayi ko nadama babu a tattareda ita
Fuskarsa jazir ya kuma d’agowa ya dubi mahaifiyarsa yana mai sakin huci a hankali, cikin dakakkiyar murya yace “Hajiya mai ya sameta... Mai yayi sanadin rayuwarta...?”
Sahariyya da Hajiya suka had’a ido Sahariyyan na aikawa Hajiya wani irin duba... Take Hajiya ta shiga inda inda tana fad’in “Yo mai kuwa ya kasheta banda ajali ko kashe maka d’iyarka zamuyi... inyi, ko rashin yardar naka takai haka ne...?”
Bai kuma cewa komai ba sai mik’ewa da yayi tamkar wanda ruwa ya shanye ya fice ba tareda ya kuma furta koda kalma ba... Naja’atu tabi bayansa cikeda tausayawa har ya fice kana ta maido da dubanta ga Hajiya da Sahariyya tanai masu muguwar kallo cikin sauri ta fice tana mai girgiza kai... Sahariyya ta rakata da muguwar kallo kana ta tab’e baki ta koma cikin d’aki tana mai danna earpiece a kunnenta ta saki sauti cikin kunnuwanta....
***
Zaune suke saman dakali k’ofar gida sai zuba zance suke irinta matasa, akasarin firan ya danganci siyasa ne da kuma wasanni k’wallon k’afa.... Daidai sanda mai amalanken rake yazo shigewa d’aya daga cikin matasan mai suna Auwalu ya tsaida mai amalanken, tuni mai rake ya gangaro yanda matasan ke zaune...
Auwalu ya dubi Akram da hankakinsa kega wayar salulansa yace “Yauwa ga mai raken na kira a saya mana muji dadin yin zance ko ya kukace...?”
Gaba d’aya sauran matasan sukace haka ne...
Akram ya d’an dube abokan nasa a kaikaice kana yace “Amma dai bani na tsaida mai rake ba...?”
“Koma bakai bane dole ka saya mana tinda mai gidanka na nema muk’ami idan ba haka ba mu hanaku k’uriunmu ko ya kuka ce..?” Nan ma suka amsa da wannan haka take, basu jira cewar Akram ba suka shiga zab’en rake mai rake na fere masu radio na kunnensa yana faman saurare...
Akram fad’i yake “Kaga Malam ko wanne cikinsu sai ya biyaka kud’inka....”
Mai rake na murmushi yake fad’in “Ai idan zasu zab’i MUTALLAB zab’in talakwa ko amalanken raken sukeso gaba d’aya sai na basu....”
Suka kekate da dariya gaba d’aya harda shi Akram d’in, tabbas ya sani Mai gidansa yanada magoya baya da dama wanda idan za’ayi zab’en gaskiya tsakani da Allah zai iyaci...
Akaci gaba da firan siyasa harda mai rake radio na bisa aiki, nan kuwa aka soma program d’in Muryar ‘yanci, Akram ya bud’e kunnuwa sosai yana jira yaji muryarta, baiji muryar tata ba sai na abokan aikinta daga bisani yaji d’aukacin ma’aikatan gidan radio d’in na mik’a mata sak’on ta’aziya na rashin d’iyarta da tayi... Tsananin mamaki ya cika Akram... Wai dama tanada aure harda yara...? Shi kad’ai yake tambayar kansa cikin zuciyarsa.... Bai kuma bi takan firan tasu ba har ya sallami mai rake ya basa kud’insa ya kuma ce ya rik’e canjin domin gudan dubu ne a aljihunsa... Matasan suka kuma ihu suna wasa shi suna fad’in sai Uban gidansa ko garin bakowa...
Akram dai gaba d’aya zuciyarsa ta tafi wata duniyar...
Abokinsa da suka taso tare a unguwar mai suna Yusuf shi ya fahimci nisan zango da Akram d’in yayi....
D’an dafasa kad’an yayi kana yace “Abokina akwai matsala ne...?”
Akram ya d’ago ya dubi Yusuf kana yace “Muje daga gefe...”
Babu musu Yusuf ya mik’e yabi bayan abokin nasa....
Daga can tsallake suka tsaya k’ofan gidansu Yusuf....
Yusuf yace “Akram lafiya dai ko...?”
Akram yace “Yusuf dama tanada aure...?”
Cikin rashin gane inda ya dosa yace “Aure... wace kenan...?”
Akram ya d’an shafi goshinsa yace “Zulfa’u Mailafiya ta gidan radion Muryar ‘yanci....”
Yusuf ya d’an murmusa a hankali kana yace “Aw dama baka sani ba...? Eh toh tanada aure batada aure...”
Akram ya dubesa da alaman tambaya kana yace “Ban gane ba what do you mean tanada aure batada aure...?”
Yusuf yace “From what I know sun rabu da mijin nata kwanakin baya can, kasan Atika abokiyar aikinta k’awar Saliha k’anwatace....”
Akram ya jinjina kai kana yace “I want to know more about her,...”
Yusuf ya d’an murmusa kana yace “Kar ka damu abokina zanyi k’ok’arina, zansa Saliha ta sanar da k’awarta zamu kaiwa Zulfa’u ta’aziya da sunan jamk’iyarku ko ya ka gani...?”
Akram ya d’anyi shiru kana yace “Amma kanaga bazatayi tunani siyasa ya kawo mu ba....?”
Yusuf yace “Haba Akram kasan MUTALLAB yanada magoya baya da dama yau ko siyasarce takaimu na tabbata bazamuji kunya ba duk yanda mukaje da sunansa....”
Akram ya d’anyi shiru na wasu dak’ik’ai kana yace “Shikenan Allah shi wuce mana gaba..”
Yusuf ya amsa da Ameen kana suka nufi cikin gidan gaba d’aya....
***
Tinda suka iso Kaduna suka had’a k’arya da gaskiya suka fad’iwa Ammi, Siyama harda cewa Khalid harda ita ya had’e ya daka...
Ammi ta dafe k’irji tana salallami...
“Khalid ne ya d’aga hannu ya dakeki...?” Ta kuma tambayar Siyamar...
Cikeda makirci Siyama tace “Aw mamaki kike sha Ammi, Toh wllhi Khalid ya shige duk yanda kike tunani, baiga darajan girme masa da nayi a haife ba yasa hannu ya dakeni nima don kawai nace ya rabu da wancan dangin mayun....”
Yesmin dake gefe da kumburarren bakinta tace “Wllhi Ammi ko shakka babu an juye masa kwanya bakiga yanda ya fice a hayyacinsa ba gaba d’aya....”
Ammi tai k’wafa tace “Dad na hanya ai shine kawai maganinsa don wllhi bazai janyo mana kayan kunya ba....” Ta k’arashe tana mai kuma dialing layin Khalid d’in
Kubura dake lab’e jikin staircase sai faman k’unshe dariyarta take tana kwaikwayan maganan Yesmin da yanda bakinta ya kumbura ya koma gefe guda, sai murna take tana tsallen Allah shi k’ara....
A daren Khalid ya dawo garin Kaduna saidai ko sashen Amminsa bai shiga ba, washe gari ma bai fito ba har saida ya tabbata mahaifinsa ya dawo don yana ganin sanda driver ya tafi airport d’aukosa, baiji mamakin ganin Khalid d’in baizo d’aukansa ba don tun a waya Ammi ta zayyane masa komai duk halinda ake ciki, shi kad’ai yake sakin huci har sai yafi Ammi fushi da lamarin musamman da shike an tab’o sanyin idaniyarsa Siyama wacce a duniya yak’i jinin yaga fushinta sabida tsananin sonta da yake....
Suna zaune gaba d’aya a parlorn ya sako kai, ko ba’ace ba yasan fitowarsa ake jira....
Kallo d’aya ya watsawa Siyama ya d’auke kai daga barin duban nata.... Can k’asa gefen k’afafun mahaifinsa ya k’arasa ya zauna...
A hankali ya furta “Daddy sannu da zuwa... Ammi ina kwana...?”
Baikai aya ba Ammi ta katsesa da fad’in “Da ban kwana ba zaka ganni...? Nace da ban kwana ba zaka ganni...? Ince kai ka zama sallamemme.... Ace tun jiya ka dawo gidan nan ka kasa lek’owa mu gaisa sabida ta zuba maka a ruwa kasha koh.... Harda wulak’anta ‘yan uwanka don kawai sun fad’i gaskiya...? Idan ka zab’eta sama da ‘yan uwanka ne sai ka tattara ka koma can ka zama cikakken sallamemme...” Siyama ta k’arada “Ahtoh fad’a masa dai Ammi..”
Daddy ya cafi zancen da ambato sunan Khalid...
“Khalid...!”
Khalid ya d’ago a hankali yana dubansa kana yace “Na’am Daddy...”
“Dad yaci gaba da fad’in “Khalid meke faruwa da rayuwar ka....?”
A hankali ya furta “I’ll explain everything Dad....”
Dakatar dashi yayi ta hanyar d’aga masa hannu kana yace “Ba sai ka min bayanin komai ba, mahaifiyarka ta sanar dani, ba kuma zan bari ka kawo mana abin fad’i a dangi ba, bazaka kawo mana yarinya maras cikakken asali ba da sunan mata, ga mata da yawa a duniya, kaje duk yanda kakeso ka kawo mace idan har family background d’inta nada kyau ni zan aura maka amma banda yarinyar da aka tabbatar batada cikakken asali balle tarbiya...”
Khalid ya dubi Ammi da Siyama da tsananin mamakin jin yanda suka had’awa Dad zance ya hau kai ya zauna... Ammi ta katse hanzarin nasa da fad’in “Ga k’awarsa Yesmin babu abinda ya rasa mai zai kaisa wani duniya neman mace...”
Daddy yace “Kaji koh... Inaso kamin rantsuwa babu kai babu wancan yarinyar sannan zaka auri ‘yar uwarka Yesmin....”
Khalid ya d’ago da mamaki yana duban mahaifinsa kana yace “Daddy rantsuwa fah kace....? Daddy it doesn’t have to reach this point...”
Ammi tace “K’warai kuwa it does ta hakane kawai zamu amince ka rabu da wancan tsinanniyar yarinyar.... Zaka rantse ne kokuwa...”
Khalid ya dubi mahaifiyarsa kurum ba tareda ya iya furta koda kalma ba...
Dad yace “K’yalesa tinda bazaiyi abinda mu muke so ba a matsayinmu na iyayensa muma bazamuyi abinda yakeso ba...”