Sashe 33
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Khalid na kallon yanda Ammi ke serving d’insa yana murmushi yana tuna a lokutan baya idan yana fushi haka Amminsa ke masa abinci kala kala tana lallashin shi, a nashi zaton sabida maganar da sukayi jiya akan Yesmin ne takeson lallashin shi...
Siyama tace “Ammi da kin bari wacce ta dafa abincin tai serving d’inshi ai...” Ta k’arashe tana kai spoon baki... Cak Siyama ta tsayada zancen nata sakamakon sugar had’ida yaji da taji sun mata sallama saman harshe a dai dai lokacin da Khalid yakai spoon d’in abinci baki ba tareda ya kula Siyama ba Ammi na ci gaba da fad’in “Your Sister cooked specially for.....”Aya Ammi taiwa kalaman nata jin Khalid ya mik’e a zabure yana tsananin tari had’ida watsar da abincin dake bakinsa...
Yesmin ta mik’e a razane tana dubanshi..
Ammi ta mik’e tana masa sannu had’ida rik’e shi...”
Yesmin tai saurin tsiyaya drink a cup ta mik’awa Ammi jikinta har rawa yake...
Ammi ta mik’a masa bakinsa tana fad’in “Sannu son sha ruwa....”
Aiko yana kafa kai yaji barkwanon ya k’aru, ya fuzar yana ci gaba da tari had’ida duk’awa...
Ammi ta dubi Yesmin tace “Yesmin mai kika saka a abincin..?”
Yesmin da gaba d’aya ta daburce tace “Ammi wllhi ban saka komai ba, Siyama even tasted...” Aya tai wa kalaman nata ganin Siyama ma na tari had’ida fito da harcenta waje tana hurawa...
Saurin d’aukan spoon Yesmin tai ta d’ibi abincin takai bakinta, bata iya had’iyewa ba itama ta wuce kitchen a guje ta zubda abincin bakinta tana neman abin shashe baki sabida tsananin barkwano had’ida tsami da zak’i...
Kubura dake lab’e sai buga tsalle take tana cin dariya a b’angare guda kuma tausayin Khalid d’inta ya kama ta amma ko babu komai Yesmin tasha disgi kwalliya ta biya kud’in sabulu...
Khalid ya d’ago a galabaice yana duban Ammi kana yace “Ammi yaushe Siyama ta iya girkin da za’a bar mata girkin gidan nan tayi...?”
Siyama ta d’ago tana dubanshi magana k’unshe a bakinta saidai itama har yanzu barkwanon bai saketa ba, kafin ta samu zarafin magana Kubura tai karaf ta nuna Yesmin da fitowarta kenan daga kitchen taje ta watsar da abincin bakinta kana taci gaba da fad’in “Gata nan... Ga wacce tai girkin gidan yau gaba d’aya kuma musamman sabida kai tayi...”
Wani irin kallo kurum Khalid ke aika mata, bai kuma cewa komai ba sai tattara car keys d’insa da folder had’ida wayar salulansa ya fice ya nufi b’angarensa..
Yesmin dake tsaye tamkar ruwa ya shanye take ta fashe da wani irin kuka tana fad’in wllhi wani ne ya b’ata mata abincinta kuma bata zargin kowa sai Kubura...
Haba nan fah Kubura ma ta dinga rantse rantse ita ba itabace sharri Yesmin take mata don ta tsaneta...
Ammi ta daka masu tsawa sukai shiru kana tace “Yesmin wuce sama, ke kuma Kubura ki wuce ki tattara dining d’in nan idan kin gama ki sameni d’aki...” Daga haka Ammi ficewa tai ta nufi b’angaren Khalid...
Yana ganinta ya d’an rausayar da idanunsa had’ida fuzar da iska yasan bazai wuce maganan Yesmin tazo mashi dashi ba...
“Ammi not now please...” Ya fad’i cikin kasaltecciyar murya
Harara ta wurga mashi tana mai fad’in
“Khalid kana jina ka saurareni da kyau, abinda ya faru ba laifin Yesmin bane sannan idanma laifinta ne ya kamata kai appreciating effort d’inta, all she’s doing tanayi ne sabida tana sonka Khalid, babban abin takaicin kai baka ma fahimtar hakan... Khalid wai mai ya shige kanka ne... Haka kakeso mu zuba maka idanu babu aure, mai amfanin zaman naka tinda ka kammala karatu ga aiki da yanzu ka kama ba dama what else bayan aure...Inyi...?”
Sauk’e deep breath yayi had’ida zama cikin sofa kana yace “Ammi kin sani fah I don’t like being pressured... Please mana Ammi, how many time do we have to talk about this.... Ammi sau nawa zance banason yarinyar nan... Idanma auren kuke so nayi then ku barni na zab’i wacce nakeso kaman yanda kuka bar Siyama ta zab’a... But please Ammi don’t force me into an arranged marriage.... I don’t like that girl period...”
Zama tayi gefenshi kana ta kamo hannayensa tana dubanshi, cikin kwantar da murya tace “Khalid... I only want what is best for you, meye laifin Yesmin, she’s beautiful, intelligent... family d’inta sanannu a garin Abuja gata ‘yar uwarka ce kuma tanada hankali and above all she’s deeply in love with you, Khalid mai kake nema sama da wannan...”
Tinda ta fara magana take dubanta kana ya girgiza kai yace “Ammi duk abinda kika lissafo doesn’t matters idan dai har bana sonta... Do not pressure me please Ammi....” Ya k’arashe yana mai lumshe idanu had’ida kishingida cikin kujeran...
A kufule ta mik’e tana fad’in “Rayuwarka ce ai sai kayi yanda kaso da ita, amma ka sani bazaka d’aukomin ko wacce irin shirgi kace zaka kawo min ita matsayin sirkaba kaji na fad’a maka....” Daga haka ficewa tayi fuu kaman zata tashi sama...
A hankali yake ambaton sunan Allah wani haushin Yesmin da tsanarta na kuma taso masa....
Siyama kam bata kuma bi takan kowa ba saima tattara kayanta da ta shigayi ta had’esu waje guda don tanaso ta maidasu gida ta canzo wasu sets d’in..
Kubura ta ganta na tattara kaya tace “Aunty badai tafiya zakiyi ba...?”
Harara Siyama ta galla mata kana tace “Kubura nafah sanki sarai akan Khalid, nasan babu abinda bazakiyi ba, nasan kece kika b’awatawa Yesmin abinci, wllhi ki shiga hankalinki idan ba so kike na sami Khalid na sanar dashi sonshi kike ba...”
Kubura tai saurin k’arasowa cikin d’akin had’ida tura k’ofar kana ta risina gaban Siyama tace “Aunty Siyama kimin rai ki barni a haka nake kallon shi inajin dad’i yanzu kika fad’i masa ai saidai ya koreni gidan nan na daina ganinshi gaba d’aya, kofah magana bai tab’a min ba ni har tsoron gaisheshi nake... Ita wancan dai bata dace ba billahillazi Aunty...” Ta k’arashe tana wani gyara rigar jikinta irin itace daidan shi..
Girgiza kai kurum Siyama tai had’ida jan gajeren tsuka tace”Au bata dace dashi ba... Toh wace ta dace dashi ke...?”
Kubura ta murmusa had’ida sinne kai tace “Wllhi kuwa Aunty”
Dariya Siyama tai don abin dariya ya bata kana tace “Ni dalla banson sakarci zoki fitar min da jakkan nan....”
Kubura ta d’auko jakan tana rok’on Siyama kada ta koma gidanta suyi zamansu a nan tinda Dr bai dawo ba...
Siyama bata tsaya biye shiriritan Kubura ba ta tada mota ta wuce abinta...
Tin daga gate d’in compound d’in nasu taji kaman k’irjinta na bugu bata gama aminta da bugun da k’irjinta keyiba saida ta hangi motarsa a parking space d’insu...
Mamaki ya kamata shin yaushe Sameer yazo kuma ko waya bai mata ba, wata zuciya tace k’ilan yayi niyyan surprising d’inki ne.. Murmushi ta d’an saki kana ta janyo trolley d’in ta shige cikin gidan...
Hangoshi da tai zaune saman kujera yasa gabanta kuma fad’uwa, gashi dai zaune kurum sannan TV na kashe kuma bawai aiki yake bisa computer ba ko danna wayarsa, a’a zaune kawai yake shi kad’ai, cikin zuciyarta tace this is not like him, koma surprise zai bata da ba’a parlor zata ganshi ba sannan da ace ma yana parlor d’in da yanzu ya taso ya bata hugs, tamkar mai sand’a haka take tafiyar har ta isa ta taddashi yanda ta hangi fatar fuskarsa tayi jajazir haka nan idanunsa da ya k’urasu ma waje guda...
This isn’t the Sameer she used to know, yanayi ne da tinda take a rayuwarta bata tab’a ganinsa cikin makamancinta ba...
Tai k’arfin halin k’ak’aro murmushi kana ta rungumeshi tana fad’in “Partner wane irin surprise ne wannan, oh I missed you....” Ta k’arashe tana kuma k’ank’ameshi saidai abinda ya bata mamaki shine bai maida mata martanin rungumarta ba saima b’anb’are hannayenta da ya soma daga cikin jikinsa cikin wane irin zafin nama....
Da tsananin mamaki Siyama ta d’ago tana dubansa ga wani irin huci da yakeyi...
Murya na rawa tace “Partner what’s all this about... Wai meke faruwa ne...?”
Da wasu irin idanu yake dubanta kana yace “Don’t touch me again...!”
Kallonsa ta kumayi cikin rashin yarda da abinda take gani hawaye na neman ciko idanunta don duk wani sab’ani da zasu samu bai tab’a mata irin hakan ba, cikin muryar kuka take furta “Sameer wai meke faruwa don Allah...?”
Cikin dakakkiyar murya ya kuma ceda ita “How long have you been lying to me...?”
Duban idanunsa tai tana iya hango tsananin b’acin rai cikinsu had’ida tashin hankali, take jikinta ya d’auki rawa ta shiga girgiza masa kai tana hawaye, cikin murya irinta mai kuka take furta “I don’t get you Sameer, please what’s happening...?”
Cikin karaji ya matso kusa da ita, fuskarsu dab na juna tana iya jiyo tsananin hucin da yake...
Da iyaka k’arfinsa ya finciko hannunta ya d’aura mata gidan magani saman tafin hannun nata kana yaci gaba da fad’in “I know you’ve been taking contraceptions Siyama....And you know, I don’t need your damn explanation... The only thing I need to know shine meyasa kika min k’arya, why did you make me believe that you love me.... Why Siyama...?”
Kuka take tana girgiza masa kai had’ida furta “Sameer please let me explain...”
Cikin tsananin d’aga murya jijiyoyin jikinsa suna tashi yake furta “I told you I don’t need your explanations... Just tell me your reason for making a fool out of me... Tell me Siyama....!!” Ya k’arashe hawaye na gangarowa daga idanunsa guda wanda da gani na tsananin b’acin rai ne...
A hankali ta furta “Partner...”
Katseta yayi da fad’in “Don’t you dare call me Partner again, just answer the damn question...!!”
Kasa furta komai tayi sai kuka da take harda shesshek’a bata tab’a zaton haka abin zai kasance ba....
Siyama tace “Ammi da kin bari wacce ta dafa abincin tai serving d’inshi ai...” Ta k’arashe tana kai spoon baki... Cak Siyama ta tsayada zancen nata sakamakon sugar had’ida yaji da taji sun mata sallama saman harshe a dai dai lokacin da Khalid yakai spoon d’in abinci baki ba tareda ya kula Siyama ba Ammi na ci gaba da fad’in “Your Sister cooked specially for.....”Aya Ammi taiwa kalaman nata jin Khalid ya mik’e a zabure yana tsananin tari had’ida watsar da abincin dake bakinsa...
Yesmin ta mik’e a razane tana dubanshi..
Ammi ta mik’e tana masa sannu had’ida rik’e shi...”
Yesmin tai saurin tsiyaya drink a cup ta mik’awa Ammi jikinta har rawa yake...
Ammi ta mik’a masa bakinsa tana fad’in “Sannu son sha ruwa....”
Aiko yana kafa kai yaji barkwanon ya k’aru, ya fuzar yana ci gaba da tari had’ida duk’awa...
Ammi ta dubi Yesmin tace “Yesmin mai kika saka a abincin..?”
Yesmin da gaba d’aya ta daburce tace “Ammi wllhi ban saka komai ba, Siyama even tasted...” Aya tai wa kalaman nata ganin Siyama ma na tari had’ida fito da harcenta waje tana hurawa...
Saurin d’aukan spoon Yesmin tai ta d’ibi abincin takai bakinta, bata iya had’iyewa ba itama ta wuce kitchen a guje ta zubda abincin bakinta tana neman abin shashe baki sabida tsananin barkwano had’ida tsami da zak’i...
Kubura dake lab’e sai buga tsalle take tana cin dariya a b’angare guda kuma tausayin Khalid d’inta ya kama ta amma ko babu komai Yesmin tasha disgi kwalliya ta biya kud’in sabulu...
Khalid ya d’ago a galabaice yana duban Ammi kana yace “Ammi yaushe Siyama ta iya girkin da za’a bar mata girkin gidan nan tayi...?”
Siyama ta d’ago tana dubanshi magana k’unshe a bakinta saidai itama har yanzu barkwanon bai saketa ba, kafin ta samu zarafin magana Kubura tai karaf ta nuna Yesmin da fitowarta kenan daga kitchen taje ta watsar da abincin bakinta kana taci gaba da fad’in “Gata nan... Ga wacce tai girkin gidan yau gaba d’aya kuma musamman sabida kai tayi...”
Wani irin kallo kurum Khalid ke aika mata, bai kuma cewa komai ba sai tattara car keys d’insa da folder had’ida wayar salulansa ya fice ya nufi b’angarensa..
Yesmin dake tsaye tamkar ruwa ya shanye take ta fashe da wani irin kuka tana fad’in wllhi wani ne ya b’ata mata abincinta kuma bata zargin kowa sai Kubura...
Haba nan fah Kubura ma ta dinga rantse rantse ita ba itabace sharri Yesmin take mata don ta tsaneta...
Ammi ta daka masu tsawa sukai shiru kana tace “Yesmin wuce sama, ke kuma Kubura ki wuce ki tattara dining d’in nan idan kin gama ki sameni d’aki...” Daga haka Ammi ficewa tai ta nufi b’angaren Khalid...
Yana ganinta ya d’an rausayar da idanunsa had’ida fuzar da iska yasan bazai wuce maganan Yesmin tazo mashi dashi ba...
“Ammi not now please...” Ya fad’i cikin kasaltecciyar murya
Harara ta wurga mashi tana mai fad’in
“Khalid kana jina ka saurareni da kyau, abinda ya faru ba laifin Yesmin bane sannan idanma laifinta ne ya kamata kai appreciating effort d’inta, all she’s doing tanayi ne sabida tana sonka Khalid, babban abin takaicin kai baka ma fahimtar hakan... Khalid wai mai ya shige kanka ne... Haka kakeso mu zuba maka idanu babu aure, mai amfanin zaman naka tinda ka kammala karatu ga aiki da yanzu ka kama ba dama what else bayan aure...Inyi...?”
Sauk’e deep breath yayi had’ida zama cikin sofa kana yace “Ammi kin sani fah I don’t like being pressured... Please mana Ammi, how many time do we have to talk about this.... Ammi sau nawa zance banason yarinyar nan... Idanma auren kuke so nayi then ku barni na zab’i wacce nakeso kaman yanda kuka bar Siyama ta zab’a... But please Ammi don’t force me into an arranged marriage.... I don’t like that girl period...”
Zama tayi gefenshi kana ta kamo hannayensa tana dubanshi, cikin kwantar da murya tace “Khalid... I only want what is best for you, meye laifin Yesmin, she’s beautiful, intelligent... family d’inta sanannu a garin Abuja gata ‘yar uwarka ce kuma tanada hankali and above all she’s deeply in love with you, Khalid mai kake nema sama da wannan...”
Tinda ta fara magana take dubanta kana ya girgiza kai yace “Ammi duk abinda kika lissafo doesn’t matters idan dai har bana sonta... Do not pressure me please Ammi....” Ya k’arashe yana mai lumshe idanu had’ida kishingida cikin kujeran...
A kufule ta mik’e tana fad’in “Rayuwarka ce ai sai kayi yanda kaso da ita, amma ka sani bazaka d’aukomin ko wacce irin shirgi kace zaka kawo min ita matsayin sirkaba kaji na fad’a maka....” Daga haka ficewa tayi fuu kaman zata tashi sama...
A hankali yake ambaton sunan Allah wani haushin Yesmin da tsanarta na kuma taso masa....
Siyama kam bata kuma bi takan kowa ba saima tattara kayanta da ta shigayi ta had’esu waje guda don tanaso ta maidasu gida ta canzo wasu sets d’in..
Kubura ta ganta na tattara kaya tace “Aunty badai tafiya zakiyi ba...?”
Harara Siyama ta galla mata kana tace “Kubura nafah sanki sarai akan Khalid, nasan babu abinda bazakiyi ba, nasan kece kika b’awatawa Yesmin abinci, wllhi ki shiga hankalinki idan ba so kike na sami Khalid na sanar dashi sonshi kike ba...”
Kubura tai saurin k’arasowa cikin d’akin had’ida tura k’ofar kana ta risina gaban Siyama tace “Aunty Siyama kimin rai ki barni a haka nake kallon shi inajin dad’i yanzu kika fad’i masa ai saidai ya koreni gidan nan na daina ganinshi gaba d’aya, kofah magana bai tab’a min ba ni har tsoron gaisheshi nake... Ita wancan dai bata dace ba billahillazi Aunty...” Ta k’arashe tana wani gyara rigar jikinta irin itace daidan shi..
Girgiza kai kurum Siyama tai had’ida jan gajeren tsuka tace”Au bata dace dashi ba... Toh wace ta dace dashi ke...?”
Kubura ta murmusa had’ida sinne kai tace “Wllhi kuwa Aunty”
Dariya Siyama tai don abin dariya ya bata kana tace “Ni dalla banson sakarci zoki fitar min da jakkan nan....”
Kubura ta d’auko jakan tana rok’on Siyama kada ta koma gidanta suyi zamansu a nan tinda Dr bai dawo ba...
Siyama bata tsaya biye shiriritan Kubura ba ta tada mota ta wuce abinta...
Tin daga gate d’in compound d’in nasu taji kaman k’irjinta na bugu bata gama aminta da bugun da k’irjinta keyiba saida ta hangi motarsa a parking space d’insu...
Mamaki ya kamata shin yaushe Sameer yazo kuma ko waya bai mata ba, wata zuciya tace k’ilan yayi niyyan surprising d’inki ne.. Murmushi ta d’an saki kana ta janyo trolley d’in ta shige cikin gidan...
Hangoshi da tai zaune saman kujera yasa gabanta kuma fad’uwa, gashi dai zaune kurum sannan TV na kashe kuma bawai aiki yake bisa computer ba ko danna wayarsa, a’a zaune kawai yake shi kad’ai, cikin zuciyarta tace this is not like him, koma surprise zai bata da ba’a parlor zata ganshi ba sannan da ace ma yana parlor d’in da yanzu ya taso ya bata hugs, tamkar mai sand’a haka take tafiyar har ta isa ta taddashi yanda ta hangi fatar fuskarsa tayi jajazir haka nan idanunsa da ya k’urasu ma waje guda...
This isn’t the Sameer she used to know, yanayi ne da tinda take a rayuwarta bata tab’a ganinsa cikin makamancinta ba...
Tai k’arfin halin k’ak’aro murmushi kana ta rungumeshi tana fad’in “Partner wane irin surprise ne wannan, oh I missed you....” Ta k’arashe tana kuma k’ank’ameshi saidai abinda ya bata mamaki shine bai maida mata martanin rungumarta ba saima b’anb’are hannayenta da ya soma daga cikin jikinsa cikin wane irin zafin nama....
Da tsananin mamaki Siyama ta d’ago tana dubansa ga wani irin huci da yakeyi...
Murya na rawa tace “Partner what’s all this about... Wai meke faruwa ne...?”
Da wasu irin idanu yake dubanta kana yace “Don’t touch me again...!”
Kallonsa ta kumayi cikin rashin yarda da abinda take gani hawaye na neman ciko idanunta don duk wani sab’ani da zasu samu bai tab’a mata irin hakan ba, cikin muryar kuka take furta “Sameer wai meke faruwa don Allah...?”
Cikin dakakkiyar murya ya kuma ceda ita “How long have you been lying to me...?”
Duban idanunsa tai tana iya hango tsananin b’acin rai cikinsu had’ida tashin hankali, take jikinta ya d’auki rawa ta shiga girgiza masa kai tana hawaye, cikin murya irinta mai kuka take furta “I don’t get you Sameer, please what’s happening...?”
Cikin karaji ya matso kusa da ita, fuskarsu dab na juna tana iya jiyo tsananin hucin da yake...
Da iyaka k’arfinsa ya finciko hannunta ya d’aura mata gidan magani saman tafin hannun nata kana yaci gaba da fad’in “I know you’ve been taking contraceptions Siyama....And you know, I don’t need your damn explanation... The only thing I need to know shine meyasa kika min k’arya, why did you make me believe that you love me.... Why Siyama...?”
Kuka take tana girgiza masa kai had’ida furta “Sameer please let me explain...”
Cikin tsananin d’aga murya jijiyoyin jikinsa suna tashi yake furta “I told you I don’t need your explanations... Just tell me your reason for making a fool out of me... Tell me Siyama....!!” Ya k’arashe hawaye na gangarowa daga idanunsa guda wanda da gani na tsananin b’acin rai ne...
A hankali ta furta “Partner...”
Katseta yayi da fad’in “Don’t you dare call me Partner again, just answer the damn question...!!”
Kasa furta komai tayi sai kuka da take harda shesshek’a bata tab’a zaton haka abin zai kasance ba....