Sashe 141
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Kasa furta komai tai sai takowa izuwa gabansa da take, fusakar k’aramin yaron shi yake gizo a idanunta... Rayuwarsu yana k’arami shi take hangowa... Shin ta yaya zata mance wannan fuska, fuskar da kullum take kwana ta tashi da ita cikin idon zuci... Ma’aruf, Ma’aruf take gani gabanta... Tabbas shi d’in ne... Gashi nan da gaske a gabanta, tanaso ta tab’a fuskarsa ta tabbatar hakan ba d’aya bane daga cikin mafarkan da take... Allahu Akbar, Mai Rai baya cire tsammani daga rahamar Ubangijinsa... A haka ta k’araso har gabanshi su duka biyun duban juna suke cikin wane irin shauk’i mai ban tausai, hannayenta suna matuk’ar rawa take k’ok’arin d’agowa kana ta shiga shafa fuskarsa har lokacin bata iya furta koda kalma ba sai kallonsa da take da idaniyanta da suka matuk’ar raunana.... Shid’inma dubanta yake idaniyansa basu daina zuban ruwa ba... Da gaske dai itace a k’wayar idanunsa... Tabbas what he went through as a child wasn’t easy... The traumatic experience da yai going through yana k’arami shi ya tafiyar da tinaninsa yasa ya mance komai, amma wannan fuska jigo na rayuwarsa da kaman yanda sunansa bai b’ace masa ba bai tinanin wannan fuskar ta b’ace masa na har abada... Mamy da Aunty Bara’atu na hawaye suka dubi juna cikin wane irin shauk’i suna mai kuma duban wannan buwayar Ubangiji da suke kallo na aukuwa a gabansu, Allah sarki tabbas INDA RAI toh fah akwai RABO, bayan duka wad’annan shekarun yau ga Ma’aruf ya dawo garesu, ga Ma’aruf Babba ga kuma Ma’aruf k’arami, kai lallai Allah mai lullub’e bawansa da tulin Rahamoninsa ne, bayan cire tsammani sama da wad’annan tulin shekaru yau saiga Ma’aruf Allah ya dawo masu dashi garesu, family d’insu sun kuma had’ewa waje guda, bayan tilin iftila’in da suka fuskanta, bayan sab’ani da rashin fahimta da yai tasiri cikin rayuwarsu yau gashi komai ya bayyana masu, komai ya fito sarari....Which of the favors of your Lord will you deny...!
Cikin rawar murya take k’ok’arin ambato sunansa har lokaci bata daina shafa fuskarsa zuwa k’irjinsa da hannayensa ba, dik yanda hannunta ya sauk’a ajikinsa bin hannun nata kurum take da kallo tana mai tabbatarda cewa Eh shid’in ne dai gashi nan gabanta, ba gizo bane yake mata... A haka hannayenta suka iso izuwa yatsun hannunsa lokaci guda ta d’ago yatsun hannayen nasa tana dubawa, idanunta suka sauk’a kan d’an wani mark k’arami dake a cikin hannunsa wanda yake exactly irin na mahaifinsa ne, kuma tin yana k’arami shima yanada wannan tabo...Take taji wani irin kuka yazo mata mai k’arfin gaske, zuciyarta ta gama raunana, k’arfin jikinta yai rauni, k’afafunta suka gaza d’aukanta lokaci guda ta fad’a jikinsa tana wani irin kuka mai ban tausai.... Take Engr ya rungumeta sosai shima yana cazgan kukan da tinda yazo duniya bai tab’a irinsa ba... Allahu Akbar gaba d’aya illahirin jama’an dake wajen sai suka zamto masu tamkar tv, kowa hawaye ne kurum Ke gangaro masa mai gauraye da murmushin Farin ciki had’ida tarin al’ajabi... Harta su Haule saida jikkunansu ya sanyaya... Tabbas yau d’in sun yarda da K’udurar Ubabgiji ta wuce gaban wasa, buwayarsa ya wuce gaban tinanin d’an Adam... Akwai darussa mai tarin yawa a rayuwar wad’annan bayin Allah... Abida tayi sadaukarwa ga ‘yar uwarta Mariya, ta kuma fidda d’anta daga cikin ramin da azzalumai suka hak’a dashike da zuya d’aya tai hakan sai gashi Allah yaji k’anta ya dawo mata da nata d’an gareta.... Tabbas wannan ya isa ya zamto izna da ishara ga masu hali irin tasu, mu kasance masu yad’a soyayya sama da k’iyayya, mu kasance masu sadaukarwa a duk lokacinda mukeda ikon yin hakan, Allhairanmu Sufi sharrinmu yawa, tabbas idan muka rik’e wad’anann bazamu tab’e ba da izinin Ubangiji....
Cikin rawar murya take k’ok’arin ambato sunansa har lokaci bata daina shafa fuskarsa zuwa k’irjinsa da hannayensa ba, dik yanda hannunta ya sauk’a ajikinsa bin hannun nata kurum take da kallo tana mai tabbatarda cewa Eh shid’in ne dai gashi nan gabanta, ba gizo bane yake mata... A haka hannayenta suka iso izuwa yatsun hannunsa lokaci guda ta d’ago yatsun hannayen nasa tana dubawa, idanunta suka sauk’a kan d’an wani mark k’arami dake a cikin hannunsa wanda yake exactly irin na mahaifinsa ne, kuma tin yana k’arami shima yanada wannan tabo...Take taji wani irin kuka yazo mata mai k’arfin gaske, zuciyarta ta gama raunana, k’arfin jikinta yai rauni, k’afafunta suka gaza d’aukanta lokaci guda ta fad’a jikinsa tana wani irin kuka mai ban tausai.... Take Engr ya rungumeta sosai shima yana cazgan kukan da tinda yazo duniya bai tab’a irinsa ba... Allahu Akbar gaba d’aya illahirin jama’an dake wajen sai suka zamto masu tamkar tv, kowa hawaye ne kurum Ke gangaro masa mai gauraye da murmushin Farin ciki had’ida tarin al’ajabi... Harta su Haule saida jikkunansu ya sanyaya... Tabbas yau d’in sun yarda da K’udurar Ubabgiji ta wuce gaban wasa, buwayarsa ya wuce gaban tinanin d’an Adam... Akwai darussa mai tarin yawa a rayuwar wad’annan bayin Allah... Abida tayi sadaukarwa ga ‘yar uwarta Mariya, ta kuma fidda d’anta daga cikin ramin da azzalumai suka hak’a dashike da zuya d’aya tai hakan sai gashi Allah yaji k’anta ya dawo mata da nata d’an gareta.... Tabbas wannan ya isa ya zamto izna da ishara ga masu hali irin tasu, mu kasance masu yad’a soyayya sama da k’iyayya, mu kasance masu sadaukarwa a duk lokacinda mukeda ikon yin hakan, Allhairanmu Sufi sharrinmu yawa, tabbas idan muka rik’e wad’anann bazamu tab’e ba da izinin Ubangiji....