Sashe 9
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abbah baice komai ba dama sunsan bazaice d’inba, gaba d’aya tinda d’ansa Ma’aruf ya b’ace ya dawo hakan, sai ya zamana tamkar bai damuwa da damuwar sauran yaransa sam basa gabansa, hakan sosai yakewa Mamy zafi, takanyi tunanin ko don su d’in ‘ya’ya matane kaman yanda Mamani ke yab’a masu maganganu ita sauran matan ‘ya’yan nata su Karima dasu Hajiya a cewarta duk sunzo sai aifan ‘ya’ya mata suke bacin ita kuwa uwar ‘yan maza ne domin kuwa duka ‘ya’yanta biyar maza ne... Hakan nan Mamani k’iriri take nuna masu tafison jikokinta maza wanda basu wuce uku ba, daga Hafiz wanda shine babba bayan b’acewan Ma’aruf(Alk’ali) haka nan take kiransa kafin ya b’ace saiko sauran biyun wanda duka ‘ya’yan Baffah Wada ne autansu Abbah.....
Zubawa Abbah abinci Mamy take ta kasa k’arasawa, Aunty Lami da zuciyarta tuni tayi haske, murmusawa tayi tana duban Abbah da tuni d’an sauran walwalar fuskar ta d’auke dukda kasancewarsa mutum maras yalwan fari’a...
K’arasowa Aunty Lami tayi ta amshi serving spoon d’in cikeda k’issa tana fad’in “A’a Mamy tashi kije kiji da ita zanjida Abbah....”. Ta k’arashe tana duban Abban da wutsiyar idanunta.... Aiko tamau ta hango fuskar nasa, ta saki murmushi a hankali....
Jiki babu k’wari Mamy ta mik’e ta kamo Nabilah suka fice....
Aunty ta gyara zama tana ci gaba da serving Abbah wanda yabi bada hankalinsa ga kallon tv...
D’an gyaran murya tayi kana tace “Na zuba romon kifin.....?” Kafin yakaiga bata amsa sukaji sallaman Mamani Hafiz na biyeda ita... Tindaga k’ofa take surfa ruwan bala’i....
“Inyi haka kawai, a d’auki alak’ak’ai a lanjab’awa jikana toh wllhi bazai sab’u ba, yo bacin zaman hak’uri da yakeda ita mai zaiyi da ita.... Idan baza’a hukunta ta ba toh wllhi ni da kaina zan guntule wannan aure jikana ya huta... Kan me yaro sai wahala da jarababbiyar yarinya yake wacce sam babu alkhairi tattareda ita....!”
Aunty ta mik’e cikeda nuna damuwa tana fad’in “Yi hak’uri Mamani kada jininki ya hau..... Allah baya son mutuwar aure ki daina fad’in haka, Zauna....” Ta k’arashe tana zaunar da ita bisa sofa tana mai ci gaba da tausarta...
Shiko Hafiz hula gaban goshi sai wani hure huren hanci yake yanajin ya isa.....
Abbah ya dubi Hafiz kana yace “Mai ta maka wannan karon.....?”
Babu kunya balle tsoron Allah Hafiz ya soma fad’in......
“Abbah jiya Zulfah har gida taje taci mutuncin Hajiyana itada k’anwar Mhaifiyarta Bara’atu, sosai ran Hajiya ya b’aci sanda take sanar dani amma ban d’auki wani hukunci kan abinba, yau nace taje ta baiwa Hajiya hak’uri toh shine ta d’ibi k’afa ta tafi taron ‘yan siyasa ashe dama wai itama har siyasan ta shiga tana tara min matan unguwa a gida idan bana nan.... Gaskiya Abbah ni na gaji da zama da Zulfa’u dama dai darajarka takeci....” Ya k’arashe yana mai d’aga kai sama...
Mamani ta kuma gyara zama daga saman sofa tana fad’in “Kaji koh ka daiji da kunnuwanka kuma idan har Hafizu ya saketa ina mai tabbatar maka babu mai kwasanta tinda shima jininta ya kasa da ita....”
Abbah da zuciyarsa ke masa matuk’ar k’una sauk’e ajiyan zuciya yayi kana ya dubi Mamani yace kiyi hak’uri Mamani amma abin baikai ayi saki ba ai.... Lami tashi ki kiramin Zulfa’u....” Ya k’arashe yana duban Aunty Lami...
Jiki na rawa ta mik’e ta nufi sashen Mamy, kafin ta isa sashen Mamy ta keb’e ta shiga neman layin aminyarta...
Wata uwar shewa suka sake daga cikin wayar kafin Aunty Lami taci gaba da fad’in “Na gaya miki Kakar ta tasosa gaba sun taho neman saki, amma fah kinsan banaso ayi sakin nan yanzu gwara tayita yawo a tsakani ita baga zawarci ba ita baga aure ba, bata a gidan uban bata a gidan mijin, kullum tana bisa layi....”
Suka kuma k’ek’yata dariya kafin Aunty tace “Zan kiraki anjima barin k’arasa kada suji shiru.....”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_..............DA RAO_
*09*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Da sallama ta shigo parlorn kanta a k’asa Aunty Lami na biyeda ita.... Hafiz da Mamani suka rakatada mummunar kallo....
Abbah kuwa bayan abubuwan da Hafiz ya zayyano tayi ji yayi tamkar ya mik’e ya tufetada duka...
Cikinsu babu wanda ya amsa sallamarta dukda sanin darajan sallamar, daga can gefen carpet ta risina had’ida furta “Abbah gani nan.....”
Saida ya kwashe mintoci kusan uku kaman bazaice komai ba sai kuma yace “Mai ya had’aki da mijinki...?”
Tasan maganan bazai wuce wannan ba dama, a hankali ta d’ago ta dubi sashen da Hafiz yake, hularsa gaban goshi saima shafa wayarsa da yake alamun babu abinda ya shalleshi, tausayin kanta ya kuma rufeta...
Muryar Abbah ta kuma tsinkayowa cikin fad’a wannan karon “Tambayarki nake, Mai ya had’aki da mijinki...?”
Kafin ta samu zarafin bada amsa Mamani ta cafe “Yo ina zata amsaka tunda tasan batada gaskiya, nidai kawai a sakarwa jikana mara a rabasa da annoba ehe....”
Bud’e baki tayi zatayi magana amma sai taji kuka yazo bakin nata, k’ok’arin saita kanta tayi dukda rawa da muryarta keyi kana tace “Abbah babu komai....”
Mamani ta daka shewa daga zaune kana tace “Kaji ja’ira yo dole kice babu komai tunda kinsan bakida gaskiya..... Munafuka kawai...”
Abbah ya kuma duban Hafiz kana yace “Maimaita abinda ka fad’i... Take Hafiz ya maimaita ko gizau babu a tattaredashi saima cewa “Abbah gaskiya aja mata kunne sosai don gaskiya banso ace na b’ata zumunta sabida taurin kunne irin nata....”
“Yo zumuntan ma ya b’aci mana sai mai me akeda annoba wacce tun haihuwarta babu alkhairi....” Mamani ta fad’i
Kasa daina dubansa tayi hawaye basu daina gangaro mata ba...
Cikin rawar murya ta furta “Ya Hafiz kaji tsoron Allah....”
“Da tsoronki zaiji.... Ja’irar banza...!” Mamani ta kuma fad’i yawa zata dunguro daga saman kujera....
“Zulfa’u da gaske mijinki ya hangoki cikin taron siyasa kuma bashi ya baki izinin hakan ba...?” Abbah ya kuma jefo mata tambaya...
Zulfah na hawaye take jinjina kai lokaci guda take fad’in “Eh Abbah da gaskene amma Abbah....” Cikin daka tsawa ya dakarta da ita kafin yaci gaba da fad’in “Wllhi wllhi kinji na rantse miki kika kashe aurenki bazaki zauna min a gida ba don bakida muhalli cikin gidan nan, muhallinki shine can d’akin mijinki, duk randa kika kaisa bango ya sakoki ki nemi wani gidan uban ba dai gidana ba kinji na fad’a miki.....”. Daga haka mik’ewa yayi ya wuce d’aki ba tareda ya kuma bi takan kowa ba....
Mamani da Hafiz suka mik’e a tare Hafiz na fad’in “Kin gani koh Mamani na fad’a miki wannan annobar bazan tab’a rabuwa da ita cikin dad’in rai ba, ni na sani Abbah hak’uri kurum zai bani.... Nidai kawai an cuceni wllhi....” Ya k’arashe yana ficewa had’ida bubbud’e hanci....
Mamani ta mik’e tana d’angwala k’afa ta isaga Zulfah dake nan durk’ushe a wajen ta shiga surfa mata bala’i kai kace rufeta da bugu zatayi, Aunty Lami sai faman dannar Mamani take cikin zuciyarta kuwa banda rawa da murna bata komai, burinta ya cika tunda bata tab’a haifa ba ita wacce ta haifa d’in dangin babu ne tunda babu mai k’aunar yaran, ta jima tana tsara hakan a rayuwarta bazata bari Mamy ta rik’e gida ba ta haifi yara sannan ta sami soyayya da kulawan kowa, ta d’au alwashi INDA RAI saita tarwatsa farin cikin da tadda Mamy da Abbah a cikinta, sai ta haifar masu da tashin hankali wacce batada ranar k’arewa, saita haifar da gaba tsakanin Mamani da ‘ya’yan Abbah tunda ita bata samu daman haifa mata koda jika guda ba, sannan sai ta zama tauraruwa a gidan dukda cewa itace batada tilon d’ah a gidan... Saita dasa soyayyarta a zuciyar kowa baga Abbah ba baga Mamani ba kai harma Mamy da yaranta sai ta sayi soyayyar kowa ta yanda zata zamto tamkar hasken rana a gidan wanda ke gusar da hasken lantarki, ya zamana ba’a ganin kowa sai ita....
K’iris ya rage Hafiz baiyi karo da Nabila ba wacce tayi k’ebebe a bakin k’ofar...
Banda uwar harara bata aika masa komai, yasan bazata gaishesa ba bazata kuma basa hak’uri ba koda zasu bagaji juna ne hakan yasashi rab’an ta gefenta zai wuce don sarai yasan wacece Nabila...
Har yakai bakin farandar ya tsinkayo muryar Nabila tana fad’in “Duk wanda bai daraja mace ba babban alamace cewa baya daraja uwarsa....”
Hafiz ya dawo da baya shaye da mamaki yake dubansa, shi Nabila ke fad’iwa magana a haka yana a matsayin yayansu gaba d’aya gidan koda ace baya auren Zulfah.... Dawowa yayi da baya yanda take nan a tsaye d’ankwalinta gaban goshi....
“Ke ni kike fad’awa magana...?” Ya tambaya yana faman huci...
Dad’a turo d’ankwalin gaba tayi had’ida basa k’eya kana taci gaba da fad’in “Idan mutum ya tsargu yasan halinsa ne toh shakka babu dashi ake...”
Hafiz ya tunzura ya d’aga hannu zai kwad’a mata mari tayi saurin duk’awa k’asa ya mari iska wanda saida k’arfin marin ta kusan aikasa k’asa badon k’ofa da ya dafe ba da ya tafi ya zube a k’asa...
Ya d’ago yana huci yake kuma k’ok’arin k’arasowa gabanta yana fad’in “Ni sa’anki ne Dan ubanki... Ni zakima rashin kunya...?”
Dariyan rainin hankali tayi kafin lokaci guda ta had’e fuska tace “Wllhi wllhi na girmi duka yanzu a gidan nan, kuma uba baifi uba ba Allah ka sake zagina sai na rama....”
A daidai lokacin da Zulfah ta k’araso wajen bata jira komai ba ta wanke Nabilah da mari tana faman huci, bata daina mamakin kalaman da taji k’anwar tata na fad’iwa mijinta ba wanda yake a matsayin Yayansu gaba d’aya...
“Addah kika mareni kan wannan ungrateful mijin naki....” Bata kai aya ba Zulfah ta fuzgo hannunta suka wuce tana fad’in idan batayi shiru ba zata k’ara mata....
Shi kuwa Hafiz har suka b’acema ganinsa mamakin Nabila yake, bai tab’a tsammanin rashin kunyar Nabilah ya kawo nan ba, lallai dole ya d’au mataki kan yarinyar nan don ko yayarta bata isa ta masa haka ba balle ita... K’ararramar yarinya da ita... INDA RAI sai ya cirewa Nabilah rashin kunyarta... K’wafa yayi kana yasa kai ya fice daga gidan zuciyarsa na masa k’una, dama ko yazo gidan iyakacinsa parlorn Abbah Mamy kuwa ba zuwa gaisheta mussamman yake ba dukda a matsayinta na sirkarsa saidai idan sun had’u a hanya ko a parlorn Abbah ya gaisheta amma bai tab’a taka parlornta da sunan gaisuwa ba...
Zubawa Abbah abinci Mamy take ta kasa k’arasawa, Aunty Lami da zuciyarta tuni tayi haske, murmusawa tayi tana duban Abbah da tuni d’an sauran walwalar fuskar ta d’auke dukda kasancewarsa mutum maras yalwan fari’a...
K’arasowa Aunty Lami tayi ta amshi serving spoon d’in cikeda k’issa tana fad’in “A’a Mamy tashi kije kiji da ita zanjida Abbah....”. Ta k’arashe tana duban Abban da wutsiyar idanunta.... Aiko tamau ta hango fuskar nasa, ta saki murmushi a hankali....
Jiki babu k’wari Mamy ta mik’e ta kamo Nabilah suka fice....
Aunty ta gyara zama tana ci gaba da serving Abbah wanda yabi bada hankalinsa ga kallon tv...
D’an gyaran murya tayi kana tace “Na zuba romon kifin.....?” Kafin yakaiga bata amsa sukaji sallaman Mamani Hafiz na biyeda ita... Tindaga k’ofa take surfa ruwan bala’i....
“Inyi haka kawai, a d’auki alak’ak’ai a lanjab’awa jikana toh wllhi bazai sab’u ba, yo bacin zaman hak’uri da yakeda ita mai zaiyi da ita.... Idan baza’a hukunta ta ba toh wllhi ni da kaina zan guntule wannan aure jikana ya huta... Kan me yaro sai wahala da jarababbiyar yarinya yake wacce sam babu alkhairi tattareda ita....!”
Aunty ta mik’e cikeda nuna damuwa tana fad’in “Yi hak’uri Mamani kada jininki ya hau..... Allah baya son mutuwar aure ki daina fad’in haka, Zauna....” Ta k’arashe tana zaunar da ita bisa sofa tana mai ci gaba da tausarta...
Shiko Hafiz hula gaban goshi sai wani hure huren hanci yake yanajin ya isa.....
Abbah ya dubi Hafiz kana yace “Mai ta maka wannan karon.....?”
Babu kunya balle tsoron Allah Hafiz ya soma fad’in......
“Abbah jiya Zulfah har gida taje taci mutuncin Hajiyana itada k’anwar Mhaifiyarta Bara’atu, sosai ran Hajiya ya b’aci sanda take sanar dani amma ban d’auki wani hukunci kan abinba, yau nace taje ta baiwa Hajiya hak’uri toh shine ta d’ibi k’afa ta tafi taron ‘yan siyasa ashe dama wai itama har siyasan ta shiga tana tara min matan unguwa a gida idan bana nan.... Gaskiya Abbah ni na gaji da zama da Zulfa’u dama dai darajarka takeci....” Ya k’arashe yana mai d’aga kai sama...
Mamani ta kuma gyara zama daga saman sofa tana fad’in “Kaji koh ka daiji da kunnuwanka kuma idan har Hafizu ya saketa ina mai tabbatar maka babu mai kwasanta tinda shima jininta ya kasa da ita....”
Abbah da zuciyarsa ke masa matuk’ar k’una sauk’e ajiyan zuciya yayi kana ya dubi Mamani yace kiyi hak’uri Mamani amma abin baikai ayi saki ba ai.... Lami tashi ki kiramin Zulfa’u....” Ya k’arashe yana duban Aunty Lami...
Jiki na rawa ta mik’e ta nufi sashen Mamy, kafin ta isa sashen Mamy ta keb’e ta shiga neman layin aminyarta...
Wata uwar shewa suka sake daga cikin wayar kafin Aunty Lami taci gaba da fad’in “Na gaya miki Kakar ta tasosa gaba sun taho neman saki, amma fah kinsan banaso ayi sakin nan yanzu gwara tayita yawo a tsakani ita baga zawarci ba ita baga aure ba, bata a gidan uban bata a gidan mijin, kullum tana bisa layi....”
Suka kuma k’ek’yata dariya kafin Aunty tace “Zan kiraki anjima barin k’arasa kada suji shiru.....”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_..............DA RAO_
*09*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Da sallama ta shigo parlorn kanta a k’asa Aunty Lami na biyeda ita.... Hafiz da Mamani suka rakatada mummunar kallo....
Abbah kuwa bayan abubuwan da Hafiz ya zayyano tayi ji yayi tamkar ya mik’e ya tufetada duka...
Cikinsu babu wanda ya amsa sallamarta dukda sanin darajan sallamar, daga can gefen carpet ta risina had’ida furta “Abbah gani nan.....”
Saida ya kwashe mintoci kusan uku kaman bazaice komai ba sai kuma yace “Mai ya had’aki da mijinki...?”
Tasan maganan bazai wuce wannan ba dama, a hankali ta d’ago ta dubi sashen da Hafiz yake, hularsa gaban goshi saima shafa wayarsa da yake alamun babu abinda ya shalleshi, tausayin kanta ya kuma rufeta...
Muryar Abbah ta kuma tsinkayowa cikin fad’a wannan karon “Tambayarki nake, Mai ya had’aki da mijinki...?”
Kafin ta samu zarafin bada amsa Mamani ta cafe “Yo ina zata amsaka tunda tasan batada gaskiya, nidai kawai a sakarwa jikana mara a rabasa da annoba ehe....”
Bud’e baki tayi zatayi magana amma sai taji kuka yazo bakin nata, k’ok’arin saita kanta tayi dukda rawa da muryarta keyi kana tace “Abbah babu komai....”
Mamani ta daka shewa daga zaune kana tace “Kaji ja’ira yo dole kice babu komai tunda kinsan bakida gaskiya..... Munafuka kawai...”
Abbah ya kuma duban Hafiz kana yace “Maimaita abinda ka fad’i... Take Hafiz ya maimaita ko gizau babu a tattaredashi saima cewa “Abbah gaskiya aja mata kunne sosai don gaskiya banso ace na b’ata zumunta sabida taurin kunne irin nata....”
“Yo zumuntan ma ya b’aci mana sai mai me akeda annoba wacce tun haihuwarta babu alkhairi....” Mamani ta fad’i
Kasa daina dubansa tayi hawaye basu daina gangaro mata ba...
Cikin rawar murya ta furta “Ya Hafiz kaji tsoron Allah....”
“Da tsoronki zaiji.... Ja’irar banza...!” Mamani ta kuma fad’i yawa zata dunguro daga saman kujera....
“Zulfa’u da gaske mijinki ya hangoki cikin taron siyasa kuma bashi ya baki izinin hakan ba...?” Abbah ya kuma jefo mata tambaya...
Zulfah na hawaye take jinjina kai lokaci guda take fad’in “Eh Abbah da gaskene amma Abbah....” Cikin daka tsawa ya dakarta da ita kafin yaci gaba da fad’in “Wllhi wllhi kinji na rantse miki kika kashe aurenki bazaki zauna min a gida ba don bakida muhalli cikin gidan nan, muhallinki shine can d’akin mijinki, duk randa kika kaisa bango ya sakoki ki nemi wani gidan uban ba dai gidana ba kinji na fad’a miki.....”. Daga haka mik’ewa yayi ya wuce d’aki ba tareda ya kuma bi takan kowa ba....
Mamani da Hafiz suka mik’e a tare Hafiz na fad’in “Kin gani koh Mamani na fad’a miki wannan annobar bazan tab’a rabuwa da ita cikin dad’in rai ba, ni na sani Abbah hak’uri kurum zai bani.... Nidai kawai an cuceni wllhi....” Ya k’arashe yana ficewa had’ida bubbud’e hanci....
Mamani ta mik’e tana d’angwala k’afa ta isaga Zulfah dake nan durk’ushe a wajen ta shiga surfa mata bala’i kai kace rufeta da bugu zatayi, Aunty Lami sai faman dannar Mamani take cikin zuciyarta kuwa banda rawa da murna bata komai, burinta ya cika tunda bata tab’a haifa ba ita wacce ta haifa d’in dangin babu ne tunda babu mai k’aunar yaran, ta jima tana tsara hakan a rayuwarta bazata bari Mamy ta rik’e gida ba ta haifi yara sannan ta sami soyayya da kulawan kowa, ta d’au alwashi INDA RAI saita tarwatsa farin cikin da tadda Mamy da Abbah a cikinta, sai ta haifar masu da tashin hankali wacce batada ranar k’arewa, saita haifar da gaba tsakanin Mamani da ‘ya’yan Abbah tunda ita bata samu daman haifa mata koda jika guda ba, sannan sai ta zama tauraruwa a gidan dukda cewa itace batada tilon d’ah a gidan... Saita dasa soyayyarta a zuciyar kowa baga Abbah ba baga Mamani ba kai harma Mamy da yaranta sai ta sayi soyayyar kowa ta yanda zata zamto tamkar hasken rana a gidan wanda ke gusar da hasken lantarki, ya zamana ba’a ganin kowa sai ita....
K’iris ya rage Hafiz baiyi karo da Nabila ba wacce tayi k’ebebe a bakin k’ofar...
Banda uwar harara bata aika masa komai, yasan bazata gaishesa ba bazata kuma basa hak’uri ba koda zasu bagaji juna ne hakan yasashi rab’an ta gefenta zai wuce don sarai yasan wacece Nabila...
Har yakai bakin farandar ya tsinkayo muryar Nabila tana fad’in “Duk wanda bai daraja mace ba babban alamace cewa baya daraja uwarsa....”
Hafiz ya dawo da baya shaye da mamaki yake dubansa, shi Nabila ke fad’iwa magana a haka yana a matsayin yayansu gaba d’aya gidan koda ace baya auren Zulfah.... Dawowa yayi da baya yanda take nan a tsaye d’ankwalinta gaban goshi....
“Ke ni kike fad’awa magana...?” Ya tambaya yana faman huci...
Dad’a turo d’ankwalin gaba tayi had’ida basa k’eya kana taci gaba da fad’in “Idan mutum ya tsargu yasan halinsa ne toh shakka babu dashi ake...”
Hafiz ya tunzura ya d’aga hannu zai kwad’a mata mari tayi saurin duk’awa k’asa ya mari iska wanda saida k’arfin marin ta kusan aikasa k’asa badon k’ofa da ya dafe ba da ya tafi ya zube a k’asa...
Ya d’ago yana huci yake kuma k’ok’arin k’arasowa gabanta yana fad’in “Ni sa’anki ne Dan ubanki... Ni zakima rashin kunya...?”
Dariyan rainin hankali tayi kafin lokaci guda ta had’e fuska tace “Wllhi wllhi na girmi duka yanzu a gidan nan, kuma uba baifi uba ba Allah ka sake zagina sai na rama....”
A daidai lokacin da Zulfah ta k’araso wajen bata jira komai ba ta wanke Nabilah da mari tana faman huci, bata daina mamakin kalaman da taji k’anwar tata na fad’iwa mijinta ba wanda yake a matsayin Yayansu gaba d’aya...
“Addah kika mareni kan wannan ungrateful mijin naki....” Bata kai aya ba Zulfah ta fuzgo hannunta suka wuce tana fad’in idan batayi shiru ba zata k’ara mata....
Shi kuwa Hafiz har suka b’acema ganinsa mamakin Nabila yake, bai tab’a tsammanin rashin kunyar Nabilah ya kawo nan ba, lallai dole ya d’au mataki kan yarinyar nan don ko yayarta bata isa ta masa haka ba balle ita... K’ararramar yarinya da ita... INDA RAI sai ya cirewa Nabilah rashin kunyarta... K’wafa yayi kana yasa kai ya fice daga gidan zuciyarsa na masa k’una, dama ko yazo gidan iyakacinsa parlorn Abbah Mamy kuwa ba zuwa gaisheta mussamman yake ba dukda a matsayinta na sirkarsa saidai idan sun had’u a hanya ko a parlorn Abbah ya gaisheta amma bai tab’a taka parlornta da sunan gaisuwa ba...