Sashe 100
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can parlorn Abbah ma jajen rashin dawowar Sameer d’in da Raihanan suke ga kuma wayarsa da bata shiga, sannan ga matarsa data bayyana wanda sam Sameer d’in bai sanar dasu zuwan nata ba.....
Mamy ta kuma dialing wayar amma bata shiga... Jigum tai tana mai furta “Allah sa dai lafiya suke...”
Abbah dake faman zagaye parlorn hannayensa hard’e a baya iska ya fuzar kana yace “Amma ai koda emergency ne ya taso masa sai ya kira ya sanar damu don kar mu damu, ba ya d’auki yarinya ya tafi da ita...”
Mamy tace “Alhaji Raihanah fah patient d’insa ce ta yuwu zuwa asibitin da ita ne ya kama shisa ya tafi da ita...”
Abbah yace “Wannan duk ba hujja bace....”
Bata kuma cewa komai ba sai sadda kanta k’asa da tai....
Abin magana da bai kasawa a gidan, tuni an soma yayatawa tsakanin sashensu Basma su Sakina, Ya Ma’aruf ya d’auki Raihanah daga islamiya ba’asan yanda sukaje ba ga matarsa ma nan gidan tana jiransa.... Lami ma tuni tayi waya ta shafawa k’awarta Haule halinda ake ciki.....
Haule kaw tace bataga ta zama ba, dama ya samesu, dole suyi amfani da wannan damar....
Sahariyya da Hajiya ta ida wayar a gabanta bore ta dingayi tana fad’in wllhi sai taci uwar Raihanah muddin bata janye idanunta kan Ya Ma’aruf, shegiya k’onanniyar banza....
Najah dai batace uffan ba saima mik’ewa da take k’ok’arinyi.... Sahariyya ta janyota daga nan yanda take zaune tace “Munafuka hardake kuke had’e kai da wancan k’onanniyar... Shine dan munafunci ko ki fad’a min shi yaje islamiyar taku ya d’auketa.... Toh wllhi idan za’a mutu ni ce nan zan aureshi kuma sai na mata iyaka da mijina....”
Najah kallonta’yaruwar tata take kana ta tintsire da dariya tace “Addah Sahariyya kina bani dariya Wllhi, shin duk fah wannan kunfan baki da hura hanci da d’aga jijiyan wuya da kike shifa Ya Ma’aruf d’in baima San kinayi ba, kuma ai inaga ba akan Raiha zaki d’aga hankali ba, kan matarsa data iso zaki d’aga hankali, indai Raihanah ce na rantse miki bai d’auketa matsayin komai ba face ‘yar k’aramar k’anwa kuma patient d’insa da yai treating d’inta....Ki tada hankali kan Aunty Siyama wacce taji gayu tasha gayu ta k’oshi, ki soma tunanin yanda zakiyi gogawa da ita wajen kishi amma ba Raihanah ba...” Ta k’arashe tana mai janye hannunta had’ida kuma tintsirewa da dariya....
Jikina sanyaye Sahariyya ta sakar mata hannu, tana mai k’arewa kanta kallo maganganun Najah na mata yawo a kwanyarta cewa tai tunanin idan zata gogawa da matarsa wacce take ‘yar gayu wajen kishi.... Kai dole koda d’ingishi ne sai taje taga matar Ya Ma’aruf taga kalanta.... Ta d’aga kai tana duban Hajiya dake faman cangwala k’afafu da k’yar tana kuma aza mayafi lokaci guda ta dubi Sahariyyar tace “Idan Alhaji ya dawo kice na tafi can gidan....” Ai bata kai aya ba Sahariyya ta katseta da fad’in “Nima zanje Hajiya...”
Haule ta dubeta shek’ek’e kana tace “Da wannan k’afar taki da bata ida warkewa ba, idan abin gudu ya biyomu a hanya nayi yaya dake...?”
Sahariyya batako kulata ba ta rarrafa ta d’auko wata sandar gora da Hajiya ke jinginewa bayan k’ofa ta dafa tace “Wllhi sai naje naga matar tasa naga mai zata nuna min....”
Tsaki kurum Hajiya tai don ta yadda Sahariyya ta gama haukacewa kan Ma’aruf, ita batama san a halin yanzu so take ta janye yunk’urin had’in yaranta da Ma’aruf d’in dataso ayi muddin ta sami hanyar salwantar dashi cikin sauk’i.... Ko sauraren Hajiya bata kumayi ba ta soma dogarawa tai gaba abinta... Hajiya ta take mata baya cikin cangwala k’afafu itama don dukansu biyu basu warke daga jinyar da suke ba....
Kallo Najah tabisu dashi had’ida girgiza kai tanai masu addu’an shiriya...
Tana zaune Sahariyya ta shigo tana faman kumbure kumbure tana mitan Baba Alhaji ne ya korota yabi Hajiya suka tafi gidan Abbah
Najah dai batace komai ba sai k’unshe dariyarta da tai, Sahariya ta galla mata harara tana fad’in “Dariyar mai kike...?”
Najah tace “Allah baki hak’uri ta Ya Ma’aruf...”
Wannan suna da Najah ta kira Sahariyya dashi sai taji gaba d’aya bak’in cikinta ya yaye...
***
A can asibiti kuwa tinda ta amsa kiran matarsa mistakenly bata kuma bi takan wayarsa ba, ta matsu baizo sun tafi ba, babu kalan tagumin da batayi ba, alla alla take yazo yakaita gida... Tana nan zaune tana tunanin taji an turo k’ofa, muryoyinsu takeji wanda ko ba’ace ba shida abokin aikinsa ne, tanajin abokin nai masa sallama had’ida masa tinin wani conference na likitoci musamman surgeons da zasu halarta gobe....
shab shikam yama mance da wata Raihanah, har saida ya danno kai cikin Office d’in kafin ya tuna ashe tare sukazo, yai saurin kusto kai cikin Office d’in yana tunanin halinda ‘yar mutane da ya barta a ciki take....
Aiko tana ganinsa ta mik’e zumbur tamkar wacce aka zabura...
Idanu suka k’urama juna kafin Raihanah tai saurin sadda nata idanun k’asa.... Fuzar da iska ya d’anyi kana yace “Sorry na barki jiran office, bansan zan jima haka ba... Aikin ne yazo da complications...”
Cikin sauri ta soma girgiza kai kana tace “A’a babu komai Yaya.... Idanma ka jima ai ceton rai ka tsaya yi, nasan ciwo da rad’ad’in k’unan wuta wanda bana fata ko mak’iyina ne yayi experiencing abinda naji... Da fatan aikin naku ya tafi yanda kuke so....?”
Idanunsa akanta tamkar mai nazari kana ya jinjina kai a hankali yace “It was successful....”
Yana kallon bakinta yanda take furta “Alhamdulillah” a hankali....
Kaman babu mai cewa komai cikinsu sai kuma yace “Muje nakaiki gida nasan suma sun damu....”
Tamkar wacce take kan k’aya tai wuf ta nufi k’ofa tana mai jinjina kai....
Sameer ya kuma binta da kallo kana ya knarasa table d’insa ya d’auki wayar salulansa da ya mance nan.... Baiji mamakin ganin tarin kira ba don hakan ne wasu lokuta kan kasancewa dashi idan ya shiga aiki ya mance wayar a kunne... Jefata a ljihu kurum yai kafin ya takewa Raihanah baya ya rufo office d’in....
Suna tafe yana observing d’inta yanda take taka k’afar nata... Sunanta taji ya ambata for the first time wanda ya haifar mata da fad’uwan gaba ta kasa ci gaba da tafiya....
Sameer ya k’araso bai janye idanunsa daga k’afar nata ba....
“Sau nawa Salma ta miki dressing yau..?” Ya tambaya still idanunsa akan k’afar nata wanda ke rufe cikin uniform d’in islamiyarta....
Ba tareda ta d’ago ta dubesa ba tace “Yau batazo ba dama taje akwai yanda zataje yau d’in bazata samu zuwa ba....”
Jinjina kai yai a hankali kana yace “Kenan yau ba’ai dressing ba...?”
Nanma jinjina masa kai kurum tai still idanunta na k’asa....
Still yai tamkar mai nazari sai kuma yace “Biyoni....” Yai maganar yanabin wata k’ofa....
Babu musu ta take masa baya dikda bugu da k’irjinta keyi, tana mai zullumin ina kuma suka nufa...
Dressing room taga an rubuta a k’ofar yanda suka nufa, kasancewar dare ne shiyasa babu jama’a sosai a asibitin, nurses d’inma wanda suke duty basu da yawa kaman na rana, da alama ma babu kowa cikin d’akin.... Offices d’in da suke wajen ya d’an lellek’a ko zai sami wacce zata mata dressing amma shiru bai samu ba...
Ita dai kallon ikon Allah kurum take, tana gani ya isa jikin wasu drawers ya soma d’ibo kayan aiki, innalillahi ai nan bugun zuciyar Raihanah ya k’aru, mai Ya Sameer ke k’ok’arin yi... Kaman wanda yasan tinanin da take... Idanunsa naga bandage d’in da yake had’awa yace “Tsorona kike...? I can hear your heartbeat.... Don’t worry I promise to be gentle....” Ita dai batace komai ba saima kallon hannunsa da take yanda yake shirya kayan dressing d’in... Sameer ya murmusa da gefen bakinsa still idanunsa naga abinda yake yace “Next time idan Salma ta sanar dake bazata sami zuwa ba ki sanar dani right away kinji koh, ya riga ya fara healing idan an bari aiki zai koma baya...” Jinjina masa kai kurum take amma sosai k’irjinta ke bugawa....
Ya d’ago idanunsa yana dubanta, sosai tsoro ya wanzu saman fuskarta, idanunta suka kuma firfitowa waje... Tinani take ta yanda zata fara bud’e k’afarta gashi kuma wando ne jikinta... Innalillahi itakam bala’in kunyarsa takeji, tsaye yayi yana nazarinta kaman wanda yasan tinanin da take.... Suna a haka muryar Awwab da wata nurse Christian wanda suka fito daga theatre tare ya katsesu... Mamaki ya cika Awwab ganin Sameer a d’akin dressing
“A a Doc you still here, baka tafi ba wai....I thought ka tafi tuntunin.... Wait what are you doing here....?” Sam bai lura da Raihanah dake zaune gefe ba yaketa jerowa Sameer wad’annan tambayoyi...
“Kaman muryar Margret naji, ko ba tare kuke ba...? Sameer ya bid’a ba tareda ya amsa d’aya daga cikin tambayoyin Awwab d’in ba....
“Eh tare muke she’s on duty....” Awwab yace yana mai duban Sameer d’in
“Akwai wani abu ne...?” Ya tambaya yana kuma suban Sameer d’in....
D’an turo baki gaba kad’an yai had’ida duban cikin d’akin yanda Raihanah ke zaune... Le k’asa Awwab yai ya hango Raihanar....
“Who’s she...?” Awwab ya tambaya yana mai duban Sameer d’in..... Turasa Sameer yai suka fice gaba d’aya yana fad’in “Zaka kiramin Margret d’in ne tai mata dressing... I’ve to take this call...” Ya k’arashe yana k’ara wayar Abbah a kunnensa
Da fad’a Abbah ya soma masa cewa ina ya d’auki Raihanah ya kaita, ga dare kuma bai sanarda kowa ba....
Sameer ya d’an sosa k’eyarsa kad’an kanshi a k’asa kaman Abban na kallonsa “Em Abbah ai hak’uri, kiran gaggawa na samu daga asibiti, amma gamu a hanya in sha Allah....”
Mamy ta kuma dialing wayar amma bata shiga... Jigum tai tana mai furta “Allah sa dai lafiya suke...”
Abbah dake faman zagaye parlorn hannayensa hard’e a baya iska ya fuzar kana yace “Amma ai koda emergency ne ya taso masa sai ya kira ya sanar damu don kar mu damu, ba ya d’auki yarinya ya tafi da ita...”
Mamy tace “Alhaji Raihanah fah patient d’insa ce ta yuwu zuwa asibitin da ita ne ya kama shisa ya tafi da ita...”
Abbah yace “Wannan duk ba hujja bace....”
Bata kuma cewa komai ba sai sadda kanta k’asa da tai....
Abin magana da bai kasawa a gidan, tuni an soma yayatawa tsakanin sashensu Basma su Sakina, Ya Ma’aruf ya d’auki Raihanah daga islamiya ba’asan yanda sukaje ba ga matarsa ma nan gidan tana jiransa.... Lami ma tuni tayi waya ta shafawa k’awarta Haule halinda ake ciki.....
Haule kaw tace bataga ta zama ba, dama ya samesu, dole suyi amfani da wannan damar....
Sahariyya da Hajiya ta ida wayar a gabanta bore ta dingayi tana fad’in wllhi sai taci uwar Raihanah muddin bata janye idanunta kan Ya Ma’aruf, shegiya k’onanniyar banza....
Najah dai batace uffan ba saima mik’ewa da take k’ok’arinyi.... Sahariyya ta janyota daga nan yanda take zaune tace “Munafuka hardake kuke had’e kai da wancan k’onanniyar... Shine dan munafunci ko ki fad’a min shi yaje islamiyar taku ya d’auketa.... Toh wllhi idan za’a mutu ni ce nan zan aureshi kuma sai na mata iyaka da mijina....”
Najah kallonta’yaruwar tata take kana ta tintsire da dariya tace “Addah Sahariyya kina bani dariya Wllhi, shin duk fah wannan kunfan baki da hura hanci da d’aga jijiyan wuya da kike shifa Ya Ma’aruf d’in baima San kinayi ba, kuma ai inaga ba akan Raiha zaki d’aga hankali ba, kan matarsa data iso zaki d’aga hankali, indai Raihanah ce na rantse miki bai d’auketa matsayin komai ba face ‘yar k’aramar k’anwa kuma patient d’insa da yai treating d’inta....Ki tada hankali kan Aunty Siyama wacce taji gayu tasha gayu ta k’oshi, ki soma tunanin yanda zakiyi gogawa da ita wajen kishi amma ba Raihanah ba...” Ta k’arashe tana mai janye hannunta had’ida kuma tintsirewa da dariya....
Jikina sanyaye Sahariyya ta sakar mata hannu, tana mai k’arewa kanta kallo maganganun Najah na mata yawo a kwanyarta cewa tai tunanin idan zata gogawa da matarsa wacce take ‘yar gayu wajen kishi.... Kai dole koda d’ingishi ne sai taje taga matar Ya Ma’aruf taga kalanta.... Ta d’aga kai tana duban Hajiya dake faman cangwala k’afafu da k’yar tana kuma aza mayafi lokaci guda ta dubi Sahariyyar tace “Idan Alhaji ya dawo kice na tafi can gidan....” Ai bata kai aya ba Sahariyya ta katseta da fad’in “Nima zanje Hajiya...”
Haule ta dubeta shek’ek’e kana tace “Da wannan k’afar taki da bata ida warkewa ba, idan abin gudu ya biyomu a hanya nayi yaya dake...?”
Sahariyya batako kulata ba ta rarrafa ta d’auko wata sandar gora da Hajiya ke jinginewa bayan k’ofa ta dafa tace “Wllhi sai naje naga matar tasa naga mai zata nuna min....”
Tsaki kurum Hajiya tai don ta yadda Sahariyya ta gama haukacewa kan Ma’aruf, ita batama san a halin yanzu so take ta janye yunk’urin had’in yaranta da Ma’aruf d’in dataso ayi muddin ta sami hanyar salwantar dashi cikin sauk’i.... Ko sauraren Hajiya bata kumayi ba ta soma dogarawa tai gaba abinta... Hajiya ta take mata baya cikin cangwala k’afafu itama don dukansu biyu basu warke daga jinyar da suke ba....
Kallo Najah tabisu dashi had’ida girgiza kai tanai masu addu’an shiriya...
Tana zaune Sahariyya ta shigo tana faman kumbure kumbure tana mitan Baba Alhaji ne ya korota yabi Hajiya suka tafi gidan Abbah
Najah dai batace komai ba sai k’unshe dariyarta da tai, Sahariya ta galla mata harara tana fad’in “Dariyar mai kike...?”
Najah tace “Allah baki hak’uri ta Ya Ma’aruf...”
Wannan suna da Najah ta kira Sahariyya dashi sai taji gaba d’aya bak’in cikinta ya yaye...
***
A can asibiti kuwa tinda ta amsa kiran matarsa mistakenly bata kuma bi takan wayarsa ba, ta matsu baizo sun tafi ba, babu kalan tagumin da batayi ba, alla alla take yazo yakaita gida... Tana nan zaune tana tunanin taji an turo k’ofa, muryoyinsu takeji wanda ko ba’ace ba shida abokin aikinsa ne, tanajin abokin nai masa sallama had’ida masa tinin wani conference na likitoci musamman surgeons da zasu halarta gobe....
shab shikam yama mance da wata Raihanah, har saida ya danno kai cikin Office d’in kafin ya tuna ashe tare sukazo, yai saurin kusto kai cikin Office d’in yana tunanin halinda ‘yar mutane da ya barta a ciki take....
Aiko tana ganinsa ta mik’e zumbur tamkar wacce aka zabura...
Idanu suka k’urama juna kafin Raihanah tai saurin sadda nata idanun k’asa.... Fuzar da iska ya d’anyi kana yace “Sorry na barki jiran office, bansan zan jima haka ba... Aikin ne yazo da complications...”
Cikin sauri ta soma girgiza kai kana tace “A’a babu komai Yaya.... Idanma ka jima ai ceton rai ka tsaya yi, nasan ciwo da rad’ad’in k’unan wuta wanda bana fata ko mak’iyina ne yayi experiencing abinda naji... Da fatan aikin naku ya tafi yanda kuke so....?”
Idanunsa akanta tamkar mai nazari kana ya jinjina kai a hankali yace “It was successful....”
Yana kallon bakinta yanda take furta “Alhamdulillah” a hankali....
Kaman babu mai cewa komai cikinsu sai kuma yace “Muje nakaiki gida nasan suma sun damu....”
Tamkar wacce take kan k’aya tai wuf ta nufi k’ofa tana mai jinjina kai....
Sameer ya kuma binta da kallo kana ya knarasa table d’insa ya d’auki wayar salulansa da ya mance nan.... Baiji mamakin ganin tarin kira ba don hakan ne wasu lokuta kan kasancewa dashi idan ya shiga aiki ya mance wayar a kunne... Jefata a ljihu kurum yai kafin ya takewa Raihanah baya ya rufo office d’in....
Suna tafe yana observing d’inta yanda take taka k’afar nata... Sunanta taji ya ambata for the first time wanda ya haifar mata da fad’uwan gaba ta kasa ci gaba da tafiya....
Sameer ya k’araso bai janye idanunsa daga k’afar nata ba....
“Sau nawa Salma ta miki dressing yau..?” Ya tambaya still idanunsa akan k’afar nata wanda ke rufe cikin uniform d’in islamiyarta....
Ba tareda ta d’ago ta dubesa ba tace “Yau batazo ba dama taje akwai yanda zataje yau d’in bazata samu zuwa ba....”
Jinjina kai yai a hankali kana yace “Kenan yau ba’ai dressing ba...?”
Nanma jinjina masa kai kurum tai still idanunta na k’asa....
Still yai tamkar mai nazari sai kuma yace “Biyoni....” Yai maganar yanabin wata k’ofa....
Babu musu ta take masa baya dikda bugu da k’irjinta keyi, tana mai zullumin ina kuma suka nufa...
Dressing room taga an rubuta a k’ofar yanda suka nufa, kasancewar dare ne shiyasa babu jama’a sosai a asibitin, nurses d’inma wanda suke duty basu da yawa kaman na rana, da alama ma babu kowa cikin d’akin.... Offices d’in da suke wajen ya d’an lellek’a ko zai sami wacce zata mata dressing amma shiru bai samu ba...
Ita dai kallon ikon Allah kurum take, tana gani ya isa jikin wasu drawers ya soma d’ibo kayan aiki, innalillahi ai nan bugun zuciyar Raihanah ya k’aru, mai Ya Sameer ke k’ok’arin yi... Kaman wanda yasan tinanin da take... Idanunsa naga bandage d’in da yake had’awa yace “Tsorona kike...? I can hear your heartbeat.... Don’t worry I promise to be gentle....” Ita dai batace komai ba saima kallon hannunsa da take yanda yake shirya kayan dressing d’in... Sameer ya murmusa da gefen bakinsa still idanunsa naga abinda yake yace “Next time idan Salma ta sanar dake bazata sami zuwa ba ki sanar dani right away kinji koh, ya riga ya fara healing idan an bari aiki zai koma baya...” Jinjina masa kai kurum take amma sosai k’irjinta ke bugawa....
Ya d’ago idanunsa yana dubanta, sosai tsoro ya wanzu saman fuskarta, idanunta suka kuma firfitowa waje... Tinani take ta yanda zata fara bud’e k’afarta gashi kuma wando ne jikinta... Innalillahi itakam bala’in kunyarsa takeji, tsaye yayi yana nazarinta kaman wanda yasan tinanin da take.... Suna a haka muryar Awwab da wata nurse Christian wanda suka fito daga theatre tare ya katsesu... Mamaki ya cika Awwab ganin Sameer a d’akin dressing
“A a Doc you still here, baka tafi ba wai....I thought ka tafi tuntunin.... Wait what are you doing here....?” Sam bai lura da Raihanah dake zaune gefe ba yaketa jerowa Sameer wad’annan tambayoyi...
“Kaman muryar Margret naji, ko ba tare kuke ba...? Sameer ya bid’a ba tareda ya amsa d’aya daga cikin tambayoyin Awwab d’in ba....
“Eh tare muke she’s on duty....” Awwab yace yana mai duban Sameer d’in
“Akwai wani abu ne...?” Ya tambaya yana kuma suban Sameer d’in....
D’an turo baki gaba kad’an yai had’ida duban cikin d’akin yanda Raihanah ke zaune... Le k’asa Awwab yai ya hango Raihanar....
“Who’s she...?” Awwab ya tambaya yana mai duban Sameer d’in..... Turasa Sameer yai suka fice gaba d’aya yana fad’in “Zaka kiramin Margret d’in ne tai mata dressing... I’ve to take this call...” Ya k’arashe yana k’ara wayar Abbah a kunnensa
Da fad’a Abbah ya soma masa cewa ina ya d’auki Raihanah ya kaita, ga dare kuma bai sanarda kowa ba....
Sameer ya d’an sosa k’eyarsa kad’an kanshi a k’asa kaman Abban na kallonsa “Em Abbah ai hak’uri, kiran gaggawa na samu daga asibiti, amma gamu a hanya in sha Allah....”