Sashe 48
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da k’arfin gaske Sawwama ta tura k’ofar wanda yasa k’iris Mamani bata zube k’asa ba, sandarta ta fad’i gefe k’ofar ta bige mata gwiwa kad’an abinka da jikin girma dama ba wai lafiyan k’afafune ya isheta ba...
Rik’eda gwiwarta take fad’in “Wayyo wayyo k’afata....!” Tana duk’e ta kasa d’agowa sai tamke idanu da take...
Sawwama dake tsaye rik’eda k’ugu tana faman yatsine yatsine wani uban tsuka ta buga kana tace “Sabida tsaban jaraba baran taku ta wuce kuyi a bakin hanya sai kun biyo mutane gidajensu kuna tak’ura masu kuna hanasu bacci ko cewa akai sadakar dole ne iyi... Shegen jaraba da fitina irin taku na tsofin mabarata... Zaki b’ace min da gani ko sai na kuma hankad’aki....!” Ta k’arashe cikin daka tsawa....
Da k’yar Mamani ta d’ago idanu tana duban matar dake mata d’iban albarka wanda tsawon rayuwarta babu wanda ya tab’a kwatanta hakan a gareta... Tirk’ashi! Ta fad’i cikin zuciyarta sanda tai tozali da matar....Tai k’ok’arin janyo sandarta ta mik’e sosai tana duban Sawwama dake faman yatsine yatsinen fuska tana jefa mata mugun kallo....
“Bakiji abinda nace bane ki fice ki bani waje..!” Sawwama tace tana mai kuma yamutsa fuska...
Banda kallonta da Mamani take bata iya komai, toh ita kuma wannan d’in wacece....? Da k’yar Mamani ta tsaya bisa k’afafunta tana kanne idanu take duban Sawwama... “Daga duniyarmu kike kokuwa akasinta...?” Ta k’arashe tana zagaye Sawwama datasha matsu cikin ‘yar fingilan riga da wando wanda za’a iya kiransa da 3quater....
Mamani taci gaba da zagayeta tana kallo take fad’in “Ikon Allah gashi dai hausa ce bakinki ba yaren arna ba balle nace babbar kahurace ked’in.... Toh kodai b’atan hanya ne nayi ba nan bane gidan Hafizun....? Ga katarorin naki dai kaman curin sakwara, shi kaw sharab’an gashi dai kaman na masu wasan dambe tsala tsala haka nan, iko sai Allah.... Ke kaw baiwar Allah sanyi bai damunki...?”
Tinda ta soma magana Sawwama ke dubanta baki sake, lallai tsohuwar ta iya cin fuska, tazo har gidanta tana yab’a mata maganganu wanda babu wanda ya tab’a yab’a matasu....
“Ke tsohuwar ashana ki saurareni nan, nafiki iya bariki barin fad’a miki, tun kafin banyi k’asa k’asa dake ba ki fice ki barmin gida bana cikeda k’anan....”
Turo k’ofa da akaine ya sanyasu gaba d’aya maida hankalinsu ga k’ofar... Hafiz ne ya shigo rik’eda ledar kaza hannunsa sai buga sauri yake...
Mamani ta saki baki tana kallon ikon Allah tabbas ba b’atan hanya tayi ba, nan ne dai gidan jikanta Hafiz... Toh ina Zulfa’u..? Sannan wannan mai k’iran arnan kan dutsen mai take cikin gidan...
Tana kallo Sawwama ta k’arasa ta rungume Hafiz had’ida d’alewa jikinsa tanai masa oyoyo cikin salo.... K’iris ya rage Mamani bata saki sandarta ta dogarawa ba tana buga sallallami...
“Laaa ha’ila ha illahu Muhammadarrasulillahi.... Na shiga uku ni Halimah mai zan gani.....?” Ta k’arashe tana neman wajen jinginuwa da zai mata waiji domin kaw tuni Sawwama dai ta tallabo bakin Hafiz ya shiga sumbata... Mamani ta rintse idanunta da k’arfin gaske tana karanto duk lazimin da yazo bakinta....
Shiko Hafiz da dabara ya k’waci kansa hannun Sawwama ya k’araso wajen Mamani cikin sauri yana fad’in “Mamani mai kikeyi a nan... Yaushe kikazo...?”
Har lokacin ta kasa bud’e idanunta balle ta basa amsa sai salati take dokawa tana fad’in abinda da ake fad’I zai faru k’arshen zamani gashi Allah ya kawosu....
Jin zata fara kuka da kururuwa yasa Hafiz kamo hannayenta ya nufi tsakar gidan da ita har wannan lokaci idanun Mamani a rintse suke tana fad’in “Hafizu wacece wannan ince dai ba matan kwararo ka soma kawowa cikin gidan ba... Ohni Jikar mutum hud’u ita Zulfa’un na ina....?”
Sawwama da takaicin tsohuwar ya kuma kamata tare Hafiz tai da fad’in “Ina kuma zaka shigar min ita.... Wllhi karma kayi tunanin kaita parlor na... Wace itama tukuna....?”
Wani irin duba ya aika mata kana ya janyo kujera a nan tsakar gidan ya zaunar da Mamani...
Cikin k’asa da murya yake fad’iwa Mamani... “Matatace Mamani ba karuwa bace, dan Allah kada ki sake dangantata da wannan kalma kinji koh...”
Mamani ta kasa amsashi sai kallon dataci gaba da binshi dashi gaba d’aya kaman ba Hafizunta ba...Tanaji tana gani ya kuma mik’ewa ya nufi Sawwama dake faman cika tana batsewa...
“Kakata ce....” Ya fad’i yana k’asa k’asa da idanu ganin irin muguwar kallon da take aika masa....
Tsuka ta buga kana ta mik’a hannu tana fad’in “Bani nan....” Don tuni hancinta ya jiyo k’amshin kaza....
Kai a k’asa ya mik’a mata ledar ta kuwa wafce kaman jira take...
Mamani ta zuba masu idanu kaman ta samu Tv....
Sawwama ta galla mata harara tana mai ci gaba da fad’in “Kai nake jira kazo ka d’auko min paranti....” Ta k’arashe tana mai zama daga can bakin k’ofar d’akinta ta baje saman tabarma tayi d’ai d’ai ta kuwa bud’e ledar kajin k’anshi sai dakan hancin Mamani yake....
Mamani naji na gani Hafiz ya mik’e babu musu ya nufi kitchen ya d’aukowa Sawwama paranti... Zai mik’e tace “Zauna...”
Ya koma ya zauna... “Bani a baki.....” Nan ma babu musu ya shiga d’auka yana kaiwa bakinta...
Mamani da abin ya koma mata tamkar a shirin wasan kwaikwayo tagumi ta rapka tana kallon ikon Allah, duk wani umarni da Sawwama zata baiwa Hafiz cikin rawar jiki yakeyi...
Tinda take a rayuwarta bata tab’a cin karo da abinda ya sanyar mata da jiki ba irin lamarin Hafizu da sabuwar matarsa, abin mamaki saiga k’walla na neman cikowa idanun Mamani tsananin tausayin jikanta da ya dirar mata, take ta soma tunanin toh ina Zulfa’u ake wannan bidirin a gidan...
“Hafizu...” Ta ambaci sunanshi daga yanda take zaune....
Ya juyo yana dubanta, take yaji jikinsa yayo sanyi sosai ganin irin yanayin da Mamani ta shiga ciki...
“Ina Zulfa’u...?” Ta tambaya tana dubanshi...
Kafin ya sami zarafin bata amsa Sawwama dake taunar nama ta kwashe da dariya tace “Zulfa’u kike nema....? Toh jikarki bata gidan nan don tuni an jima da sakinta, kinga d’akinta can ya zama kango.....” Ta k’arashe tana kuma sakin shewa..
Mamani dataji abin kaman diran aradu kallo tabi Hafiz dashi wanda kansa ke k’asa tsawon wani lokaci...
“Hafizu da gaske ka saki Zulfa’u...?” Ta tambaya tana dubansa...
Saurin girgiza kai ya shigayi yana fad’in “A’a.... Ta tafiya tayi Mamani amma zata dawo...”
Sawwama ta kuma sakin shewa kana tace”Ashe dai bakuda labari, tun wuri ku bazama duniya neman d’iyarku don rabonta da gidan nan watanni hud’u kenan tun kafin a auroni....”
“Hafizu...!” Mamani ta fad’i tana dafe k’irji.... Lokaci guda taci gaba da jero salati tana tana tafe hannaye....Kaman wacce aka sakata mata batir nan ta soma kuka wiwiwi tana fad’in ahalil kitabi ta shanye mata jika...
Haba nan fah Sawwama ta kuma tinzira tana balbala masifawa Hafiz cewa saidai ya fice mata da wannan tsohuwar a gida don idan bata daina zaginta ba tsaf ramawa zatai...
Hafiz yasan Sawwama zata aika abinda tace tuni ya kamo Mamani suka fice daga gidan ko cinyar kazar nan ba’a gutsura mata ba dukda ranta ya biya...
Da kanshi ya tarar mata adaidaita ya sakata ya sanarwa mai adaidaitan yanda zai kaita..
Haka Mamani ta tallabo bakin mayafi tanaci gaba da kuka tana fad’in shikenan Zulfa’u bata lashe Hafizu ba ga Ahalil kitabi ta shanyesa....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*39*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
A daidai k’ofar gidan Baba Alhaji Mamani ta umarci mai keken da ya ijeta...
Ta lalumo kud’i a lalitanta ta biya mai adaidaitan, kai tsaye ta nufi gidan bata daina koke koke tana fad’in shikenan an shanye mata jika ba...
A farfajiyan gidan ta hangi Hajiya Haule sai jibgan Rihanah take tana fad’in sai ta fito mata da kud’inta data d’auke, Kausar na zaune gefe tana kuka fuskarta dama dama da kunu yayinda Sahariyya da Najah ke murnan tsalle suna fad’iwa Hajuyarsu ta daki kud’inta da kyau, sam ko sauraro Mamani basuyi ba...
Ganin za’a kashe mata jika ya sanyata k’ara sauri sai gani sukai Mamani ta tare dukan tana fad’iwa Hajiya ta had’e da ita ta daka...
Gaba d’aya sukabi Mamani da kallon mamaki abinda bata tab’ayi ba shine ta nuna kulawa ko damuwarta kan jikokinta mata sai gashi yau ta tarewa Raiha duka har tana cewa a had’e da ita...
Hajiya dake faman huci tana muzurai sai aikawa Mamani muguwar kallo a kwance take itako Sahariyya datafi kowa shara cewa tayi “Mamani ki kauce ki bada filiwa Hajiya tarbiyawa d’iyarta take, yo da kike cewa a had’e dake mai za’a daka a nan salon a k’arasaki ki janyowa mutane jangwamgwam....!” Batakai aya ba taji sauk’ar sandar Mamani a kafad’arta ta kaw rik’e wajen tana ihu...
Mamani taci gaba da fad’in “Ke ki kiyayeni kinsha rashin kunya a nono koh... Toh billahillazi ki bar ganina haka nan ina dogara sanda tsaf zan murk’usheki wajen nan... Ja’ira maras ta ido...”
Hajiya ta cafi zancen da fad’in “A’a nidai Mamani gaskiya ki daina aibanta min d’iya, idanma tayi rashin ta idon ai kinsan yanda ta samo....” Ta k’arashe tana danna mata harara...
Tsananin mamakin rashin tarbiyan Hajiya da yaranta ya sanya Raihanah girgiza kai tana sosa wajen da aka jibgeta hawaye na kwaranyo mata...
Jinjina kai Mamani tai kana tace “Yayi... Yayi Haule, ai bansan rashin ta idon naki ya kawo nan ba, amma ki jira kiga yanda duniya zatai dake, na tabbata ke kika tilastawa Hafizu sakin Zulfa’u, kin sabautar min da jika ta shige duniya yanzu kin kama wannan ‘yar marainiyar kina neman illatata.... Kiji tsoron gamuwarki da Allah....”
Hajiya ta saki shewa tana tafe hannaye had’ida rangad’a gud’a kana tace “Yau akeyinta... Yanzu ke Mamani bakiji kunya ba, har da kike cewa an sabautar miki da jika, har yaushe kika soma son Zulfa’u a matsayin jikarki, wani irin tsana da muzantawa ne baki mata ba yanzu don Hafizu ya saketa ba abin kimin godiya bane, Toh barikiji na fad’a miki banson kinibibi da bak’in iyayi maza ki kwashi k’afafunki ki ficemin a gida....!” Ta k’arashe cikin d’aga murya tana mai mata nuni da k’ofa...
Mamani da zuciyarta ke mata k’una a hasale ta shiga nuna Hajiya Haule da sandarta tana fad’in “Ke Haule ki kiyayeni idan kin shanye Sarki (Hakan Mamani ke kiran Baba Alhaji a matsayinsa na babban d’anta) baya ganin laifinki toh kul kada ki kuskura ki gwada rashin kunyarki akaina...”
Rik’eda gwiwarta take fad’in “Wayyo wayyo k’afata....!” Tana duk’e ta kasa d’agowa sai tamke idanu da take...
Sawwama dake tsaye rik’eda k’ugu tana faman yatsine yatsine wani uban tsuka ta buga kana tace “Sabida tsaban jaraba baran taku ta wuce kuyi a bakin hanya sai kun biyo mutane gidajensu kuna tak’ura masu kuna hanasu bacci ko cewa akai sadakar dole ne iyi... Shegen jaraba da fitina irin taku na tsofin mabarata... Zaki b’ace min da gani ko sai na kuma hankad’aki....!” Ta k’arashe cikin daka tsawa....
Da k’yar Mamani ta d’ago idanu tana duban matar dake mata d’iban albarka wanda tsawon rayuwarta babu wanda ya tab’a kwatanta hakan a gareta... Tirk’ashi! Ta fad’i cikin zuciyarta sanda tai tozali da matar....Tai k’ok’arin janyo sandarta ta mik’e sosai tana duban Sawwama dake faman yatsine yatsinen fuska tana jefa mata mugun kallo....
“Bakiji abinda nace bane ki fice ki bani waje..!” Sawwama tace tana mai kuma yamutsa fuska...
Banda kallonta da Mamani take bata iya komai, toh ita kuma wannan d’in wacece....? Da k’yar Mamani ta tsaya bisa k’afafunta tana kanne idanu take duban Sawwama... “Daga duniyarmu kike kokuwa akasinta...?” Ta k’arashe tana zagaye Sawwama datasha matsu cikin ‘yar fingilan riga da wando wanda za’a iya kiransa da 3quater....
Mamani taci gaba da zagayeta tana kallo take fad’in “Ikon Allah gashi dai hausa ce bakinki ba yaren arna ba balle nace babbar kahurace ked’in.... Toh kodai b’atan hanya ne nayi ba nan bane gidan Hafizun....? Ga katarorin naki dai kaman curin sakwara, shi kaw sharab’an gashi dai kaman na masu wasan dambe tsala tsala haka nan, iko sai Allah.... Ke kaw baiwar Allah sanyi bai damunki...?”
Tinda ta soma magana Sawwama ke dubanta baki sake, lallai tsohuwar ta iya cin fuska, tazo har gidanta tana yab’a mata maganganu wanda babu wanda ya tab’a yab’a matasu....
“Ke tsohuwar ashana ki saurareni nan, nafiki iya bariki barin fad’a miki, tun kafin banyi k’asa k’asa dake ba ki fice ki barmin gida bana cikeda k’anan....”
Turo k’ofa da akaine ya sanyasu gaba d’aya maida hankalinsu ga k’ofar... Hafiz ne ya shigo rik’eda ledar kaza hannunsa sai buga sauri yake...
Mamani ta saki baki tana kallon ikon Allah tabbas ba b’atan hanya tayi ba, nan ne dai gidan jikanta Hafiz... Toh ina Zulfa’u..? Sannan wannan mai k’iran arnan kan dutsen mai take cikin gidan...
Tana kallo Sawwama ta k’arasa ta rungume Hafiz had’ida d’alewa jikinsa tanai masa oyoyo cikin salo.... K’iris ya rage Mamani bata saki sandarta ta dogarawa ba tana buga sallallami...
“Laaa ha’ila ha illahu Muhammadarrasulillahi.... Na shiga uku ni Halimah mai zan gani.....?” Ta k’arashe tana neman wajen jinginuwa da zai mata waiji domin kaw tuni Sawwama dai ta tallabo bakin Hafiz ya shiga sumbata... Mamani ta rintse idanunta da k’arfin gaske tana karanto duk lazimin da yazo bakinta....
Shiko Hafiz da dabara ya k’waci kansa hannun Sawwama ya k’araso wajen Mamani cikin sauri yana fad’in “Mamani mai kikeyi a nan... Yaushe kikazo...?”
Har lokacin ta kasa bud’e idanunta balle ta basa amsa sai salati take dokawa tana fad’in abinda da ake fad’I zai faru k’arshen zamani gashi Allah ya kawosu....
Jin zata fara kuka da kururuwa yasa Hafiz kamo hannayenta ya nufi tsakar gidan da ita har wannan lokaci idanun Mamani a rintse suke tana fad’in “Hafizu wacece wannan ince dai ba matan kwararo ka soma kawowa cikin gidan ba... Ohni Jikar mutum hud’u ita Zulfa’un na ina....?”
Sawwama da takaicin tsohuwar ya kuma kamata tare Hafiz tai da fad’in “Ina kuma zaka shigar min ita.... Wllhi karma kayi tunanin kaita parlor na... Wace itama tukuna....?”
Wani irin duba ya aika mata kana ya janyo kujera a nan tsakar gidan ya zaunar da Mamani...
Cikin k’asa da murya yake fad’iwa Mamani... “Matatace Mamani ba karuwa bace, dan Allah kada ki sake dangantata da wannan kalma kinji koh...”
Mamani ta kasa amsashi sai kallon dataci gaba da binshi dashi gaba d’aya kaman ba Hafizunta ba...Tanaji tana gani ya kuma mik’ewa ya nufi Sawwama dake faman cika tana batsewa...
“Kakata ce....” Ya fad’i yana k’asa k’asa da idanu ganin irin muguwar kallon da take aika masa....
Tsuka ta buga kana ta mik’a hannu tana fad’in “Bani nan....” Don tuni hancinta ya jiyo k’amshin kaza....
Kai a k’asa ya mik’a mata ledar ta kuwa wafce kaman jira take...
Mamani ta zuba masu idanu kaman ta samu Tv....
Sawwama ta galla mata harara tana mai ci gaba da fad’in “Kai nake jira kazo ka d’auko min paranti....” Ta k’arashe tana mai zama daga can bakin k’ofar d’akinta ta baje saman tabarma tayi d’ai d’ai ta kuwa bud’e ledar kajin k’anshi sai dakan hancin Mamani yake....
Mamani naji na gani Hafiz ya mik’e babu musu ya nufi kitchen ya d’aukowa Sawwama paranti... Zai mik’e tace “Zauna...”
Ya koma ya zauna... “Bani a baki.....” Nan ma babu musu ya shiga d’auka yana kaiwa bakinta...
Mamani da abin ya koma mata tamkar a shirin wasan kwaikwayo tagumi ta rapka tana kallon ikon Allah, duk wani umarni da Sawwama zata baiwa Hafiz cikin rawar jiki yakeyi...
Tinda take a rayuwarta bata tab’a cin karo da abinda ya sanyar mata da jiki ba irin lamarin Hafizu da sabuwar matarsa, abin mamaki saiga k’walla na neman cikowa idanun Mamani tsananin tausayin jikanta da ya dirar mata, take ta soma tunanin toh ina Zulfa’u ake wannan bidirin a gidan...
“Hafizu...” Ta ambaci sunanshi daga yanda take zaune....
Ya juyo yana dubanta, take yaji jikinsa yayo sanyi sosai ganin irin yanayin da Mamani ta shiga ciki...
“Ina Zulfa’u...?” Ta tambaya tana dubanshi...
Kafin ya sami zarafin bata amsa Sawwama dake taunar nama ta kwashe da dariya tace “Zulfa’u kike nema....? Toh jikarki bata gidan nan don tuni an jima da sakinta, kinga d’akinta can ya zama kango.....” Ta k’arashe tana kuma sakin shewa..
Mamani dataji abin kaman diran aradu kallo tabi Hafiz dashi wanda kansa ke k’asa tsawon wani lokaci...
“Hafizu da gaske ka saki Zulfa’u...?” Ta tambaya tana dubansa...
Saurin girgiza kai ya shigayi yana fad’in “A’a.... Ta tafiya tayi Mamani amma zata dawo...”
Sawwama ta kuma sakin shewa kana tace”Ashe dai bakuda labari, tun wuri ku bazama duniya neman d’iyarku don rabonta da gidan nan watanni hud’u kenan tun kafin a auroni....”
“Hafizu...!” Mamani ta fad’i tana dafe k’irji.... Lokaci guda taci gaba da jero salati tana tana tafe hannaye....Kaman wacce aka sakata mata batir nan ta soma kuka wiwiwi tana fad’in ahalil kitabi ta shanye mata jika...
Haba nan fah Sawwama ta kuma tinzira tana balbala masifawa Hafiz cewa saidai ya fice mata da wannan tsohuwar a gida don idan bata daina zaginta ba tsaf ramawa zatai...
Hafiz yasan Sawwama zata aika abinda tace tuni ya kamo Mamani suka fice daga gidan ko cinyar kazar nan ba’a gutsura mata ba dukda ranta ya biya...
Da kanshi ya tarar mata adaidaita ya sakata ya sanarwa mai adaidaitan yanda zai kaita..
Haka Mamani ta tallabo bakin mayafi tanaci gaba da kuka tana fad’in shikenan Zulfa’u bata lashe Hafizu ba ga Ahalil kitabi ta shanyesa....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*39*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
A daidai k’ofar gidan Baba Alhaji Mamani ta umarci mai keken da ya ijeta...
Ta lalumo kud’i a lalitanta ta biya mai adaidaitan, kai tsaye ta nufi gidan bata daina koke koke tana fad’in shikenan an shanye mata jika ba...
A farfajiyan gidan ta hangi Hajiya Haule sai jibgan Rihanah take tana fad’in sai ta fito mata da kud’inta data d’auke, Kausar na zaune gefe tana kuka fuskarta dama dama da kunu yayinda Sahariyya da Najah ke murnan tsalle suna fad’iwa Hajuyarsu ta daki kud’inta da kyau, sam ko sauraro Mamani basuyi ba...
Ganin za’a kashe mata jika ya sanyata k’ara sauri sai gani sukai Mamani ta tare dukan tana fad’iwa Hajiya ta had’e da ita ta daka...
Gaba d’aya sukabi Mamani da kallon mamaki abinda bata tab’ayi ba shine ta nuna kulawa ko damuwarta kan jikokinta mata sai gashi yau ta tarewa Raiha duka har tana cewa a had’e da ita...
Hajiya dake faman huci tana muzurai sai aikawa Mamani muguwar kallo a kwance take itako Sahariyya datafi kowa shara cewa tayi “Mamani ki kauce ki bada filiwa Hajiya tarbiyawa d’iyarta take, yo da kike cewa a had’e dake mai za’a daka a nan salon a k’arasaki ki janyowa mutane jangwamgwam....!” Batakai aya ba taji sauk’ar sandar Mamani a kafad’arta ta kaw rik’e wajen tana ihu...
Mamani taci gaba da fad’in “Ke ki kiyayeni kinsha rashin kunya a nono koh... Toh billahillazi ki bar ganina haka nan ina dogara sanda tsaf zan murk’usheki wajen nan... Ja’ira maras ta ido...”
Hajiya ta cafi zancen da fad’in “A’a nidai Mamani gaskiya ki daina aibanta min d’iya, idanma tayi rashin ta idon ai kinsan yanda ta samo....” Ta k’arashe tana danna mata harara...
Tsananin mamakin rashin tarbiyan Hajiya da yaranta ya sanya Raihanah girgiza kai tana sosa wajen da aka jibgeta hawaye na kwaranyo mata...
Jinjina kai Mamani tai kana tace “Yayi... Yayi Haule, ai bansan rashin ta idon naki ya kawo nan ba, amma ki jira kiga yanda duniya zatai dake, na tabbata ke kika tilastawa Hafizu sakin Zulfa’u, kin sabautar min da jika ta shige duniya yanzu kin kama wannan ‘yar marainiyar kina neman illatata.... Kiji tsoron gamuwarki da Allah....”
Hajiya ta saki shewa tana tafe hannaye had’ida rangad’a gud’a kana tace “Yau akeyinta... Yanzu ke Mamani bakiji kunya ba, har da kike cewa an sabautar miki da jika, har yaushe kika soma son Zulfa’u a matsayin jikarki, wani irin tsana da muzantawa ne baki mata ba yanzu don Hafizu ya saketa ba abin kimin godiya bane, Toh barikiji na fad’a miki banson kinibibi da bak’in iyayi maza ki kwashi k’afafunki ki ficemin a gida....!” Ta k’arashe cikin d’aga murya tana mai mata nuni da k’ofa...
Mamani da zuciyarta ke mata k’una a hasale ta shiga nuna Hajiya Haule da sandarta tana fad’in “Ke Haule ki kiyayeni idan kin shanye Sarki (Hakan Mamani ke kiran Baba Alhaji a matsayinsa na babban d’anta) baya ganin laifinki toh kul kada ki kuskura ki gwada rashin kunyarki akaina...”