Sashe 145
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can gidan Haule fah? Tashin hankali wanda ba’a saka masa rana... Mamaki ya cikata sanda ta kutsa cikin gidan ‘yandaudun nan sukai chaaa suna ele suna fad’in ga babbar Yaya ta iso a bata fili.... Suka janyo hannayen Haule dake binsu da kallon mamaki, tuni suka jefa Haule tsakiyar filin rawa suna gewayeta gurmi da garaya naci gaba da tashi... Can Haule ta hango Sawwama da d’aurin nan nata gaba na kallon yamma bayan na kallon gabasa sai karkad’a k’afa take tana jijjiga alamun rawa daga zaune....
Haule ta murmusa dan dik a zatonta Sawwama tayi haka ne ta kwaso ‘yan daudu da mai gurmi dan ta cazagawa Sahariyya bak’in ciki tinda an fasa bikinta.... Haule ta k’arasa gaban Sawwama tana huci tana nunata da ‘yar yatsa “Ke k’aramar kilaki, k’aramar shed’aniya ni nafi k’arfin kizo har cikin gidana kice zaki cazga min bak’in ciki... Naci uwarki a bariki barikiji na fad’a miki... Tin wuri ki tattari wad’annan ‘yaniskan ku fice min gida tinda ba bayan gari bane...!” Ta k’arashe tana kuma fincika....
‘Yan daudun nan suka shiga kame baki cikin salo suna fad’in “Aaaa Haba yayarmu tarban da zaki mana kenan... Kuma ma ai nan gidan Ubanmu ne zama daram babu fashe Billahillazi...!” Suka k’arashe suna tafe hannaye...
Kan Haule ya d’aure ta dubesu tace “Waye Uban naku....?!”
Salo sukai suna masu kame baki da tafe hannaye suke furta “Chaasss! Ayyye Lantana shafa mata...!” D’ayan yace
Wanda aka kirada Lantana gyara d’aurin k’irji yai had’ida rik’e hab’a kana yace “Waa ki rufa min asiri in mutu a d’aki maza su kaini... Ba’a ji mutuwar sarki a bakina ba wllhi....!”
Haule fah ta soma firgita da lamarin dan har yanzu bama ta lura da matar dake daga gefen mai garaya fuskarta lullub’e cikin mayafi ba.... Harta Sahariyya dake cikin nata damuwar gyara zama tai bayan ta ida birgimanta a k’asa tana kallon wannan show dake gudana a gidansu, kai kowa a wajen tsayuwa baima idanunsa abinci yai da ganin wannan ikon Allah...
Haule ta k’arasa a fusace ta finciko Sawwama tana fad’in “Ke dan uwarki me kike shirya ma d’ahna bak’ar mayya zuri’an jarababbu...” Batakai aya ba Magajiya ta mik’e had’ida yaye rufin kanta tai d’amara da gyalenta ta finciki d’iyarta Sawamma ta koma baya kana tai tsaye gaban Haule tana mai furta “Ke kada ki kuskura ki kuma tab’a min lafiyar d’iya dan wllhi kinji na rantse miki wad’annan mata mazan da kike gani su sauya miki kamanni....!”
Al’ajabi had’ida mamaki ya kuma kama Haule... Dariyar datafi kama data takaici Haule tai kana tace “Yo ai sai kuce min tafe kuke gaba d’aya, kuce bayan gari ne yau gaba d’aya a gidan namu, au ta kasa ne shine bari ta d’auko uwarta ta tayata... Yo ai kun bani kunya tinda kukayo zugan wad’annan asararrun... Ashe dai na cika aji shakkun tunk’arata...!”
Wannan karon murmushi Magajiya tai tana mai k’arema Haule duba daga sama har k’asa kana tace “Sauk’inki d’aya baki kai na zuba kishi dake ba, dan haka gwara ki saduda kiyi biyayya mu zauna lafiya...”
Haule fah bataji batun da kyau ba, mai wannan kilakin take fad’i ne....? Bata ankara ba tajiyo muryar Magajiya tana fad’in Mai gurmi yaci gaba da aikinsa, tana fad’i tana tik’an rawa daga tsakiya ashararrunta na tayata....
Su Amara k’irjin biki mai zasuyi itada k’awayenta banda dariya, harta Sahariyya saida taji dariya ya kufce mata ganin wannan drama dake faruwa a gidansu wanda yafi kama da wasan kwaikwayo tama mance itama cikin nata damuwar take, harta su Fa’iza k’awayen Sahariyya dariya Kawai suke suna fad’in saidai fah Sahariyya tai hak’uri amma wannan al’amari dole su dara su kuma kai gaba...
Haule da duniyar ta kuma juya mata a matuk’ar sanyaye ta isa gaban Magajiya tana fad’in “Mai kikace...?” Wannan karon cikin sanyin gwiwa sosai tai maganar...
Magajiya ta murmusa tace “Yafi miki da kika saduda da wuri... Ki jira mijinki shi zaizo yai maki sauran jawabi, kina iya shigowa fili mu taka a halin yanzu...” Ta k’arshe tana mai janyo hannun Haule tana sakata tai rawa tana bin sautin garayar tana furta “Rawa Haule rawa Haule....!”
Bibbiyu Haule ta soma gani... Itace Alhaji zai mata wannan cin kashin... Aure! Aure yai ba tareda saninta ba, aurenma ya rasa waye zai auro mata sai Magajiya... Take taji wani irin kuka na zuwa mata dan dik yanda takai da ganin ya d’aure bata isa ba bazata iya ba, tana jin yanda zuciyarta Ke fincika daga k’irjinta kaman zai fice... Itakam ta gwammci mutuwa da ganin irin wannan rana.... Zame hannayenta tai daga rik’onda Magajiya tai mata had’ida zama dirshan a k’asa ta jinginu jikin garu ta dafe kai tana furta “Na shiga uku ni Haule... Na shiga uku... Hafiz ya kawo mana annoba cikin zuri’a da ya auro d’iyar matar nan... Yanzu jarabawar bai tsaya akanshi kawai ba harda mijina... Na mutu, Haule k’arshenki yazo...!” Ta k’arashe tana mai sakin wani irin kuka da batasan ya kufce mata ba, suko su Magajiya da ayarinta basu fasa shagalinsu ba su Amara na tayasu....
A haka Hafiz ya shigo gidan ya tadda wannan kwamacala dake faruwa a gidan mahaifin nasa...
***
A can gidan Abbah kaw yanke shawarin had’uwa Washe gari sukai gaba d’aya a can gidan Babbar Yayarsu Abidah bayan kowa ya d’an sami natsuwa zuwa goben... Haka yayi masu gaba d’aya, saidai yau d’in sun kasa rabuwa da juna suka yanke shawarin kwana su duka hud’un a gidan ‘yar uwarsu Mariya, dan yau d’in ji suke tamkar kada su kuma rabuwa da juna, ga yaran Daula tuni sun sake suma sunata murna yau Mominsu ta had’uda family d’inta, tuni dama Daula tayi waya ma Daddy ta sanar dashi halinda ake ciki Farin ciki da al’ajabi ya cika Daddy, yace tai zamanta cikin ‘yan uwanta don da har zai turo driver ya d’aukosu zuwa masauk’i itada yara... Abin fah sai son barka ta ko wanne b’angare Farin ciki ne maras misaltuwa, daga bisani Engr da Sameer sukaima iyayen nasu sallama suka fice kaman kada su rabu da juna, nan Sameer yai rakiyawa Engr zuwa waje suna tafe suna kuma tattaunawa, bayan Engr ya wuce shima Sameer d’in sashen Mahaifinsa ya nufa yana mai zullumin halinda zai tadda mahifin nasa ciki bayan tulin abubuwan da suka faru a yau d’in....
Da sallama saman bakinsa ya nufo cikin parlorn sanda Abbah yai masa izinin shigowa... Ga mamakin Sameer murmushi ya gani kwance saman fuskan Abbah sam bazakace yanada damuwa ba sai ka karancesa sosai ka iya gano hakan....
“Shigo abinka, k’araso Ma’aruf... Dama ina nemanka akwai maganar da zamu tattauna....”
Sameer ya zauna daga gefen k’afan Abbah yana mai gaida Abban... Abbah ya amsa masa har lokacin murmushi ne saman fuskarsa wanda ko ba’ace ba kasan k’arfin hali kawai yake...
Bayan Sameer ya zauna Abbah yaci gaba da fad’in “Akan batun aurenka da d’iyar wajen Yaya...!”
Gaban Sameer ya yanke ya fad’i, dan shi har ya mance da batun wata Sahariyya.... Ya sinkayo Abbah naci gaba da fad’in “ Nasan mai yuwa kanada labarin an sauya aurenka da k’anwar Sahariyya...”
Wannan karon d’agowa ya d’anyi cikeda mamaki kana Abba ya jinjina kai yace “Da alama bakada labari... Ma’aruf..!” Ya kuma kiran sunansa cikeda kulawa...
Wannan karon jiki a sanyaye ya d’ago yana duban Abban...
Abba yaci gaba da fad’in “An maida aurenka kan ‘yaruwarka RAIHANAH... Bayan dik abinda suka faru nasan bakada wani tambayar da zakai gameda wannan al’amari... Kasan Raihanah itace matar da Allah ya zab’ar maka kuma inaso ka rik’eta amana, kada ka dubi abinda mahaifinta yai mana nida mahaifiyarka harma da kai... Ita d’in yarinyar kirkice, Allah Ubangiji yai maku albarka, ya azirtaku da ziri’a d’ayyiba... Ina labarin d’aya matar taka...?”
Sameer da ya tsinci zancen tamkar sauk’ar aradu dikda cewa yaji wani irin sanyi na sauk’ar masa cikin zuciyarsa sanda akace bai aure d’iyar Haule ba, saidai baima San mai yakeji gameda auren Raihanar ba, wani feeling ne da bai isa ya fasalta ba a halin yanzu... Muryar Abbah ya sinkayo yana fad’in “Kai nake tambaya Ma’aruf.... Ina labarin matarka...?”
Sameer ya d’an sosa kansa kad’an kana yace “Em Abbah dama... Dama sai naje Kaduna na dubata...”
Abba ya jinjina kai yace “Toh dama lallai lallai kaje ka duba iyalinka, ka had’e kan iyalanka ku zauna lafiya kaji koh..”
Sameer ya jinjina kai a hankali yana mai furta “Zanyi yanda kace in sha Allah Abbah...”
Abbah ya murmusa kana yace “Allah shi maka albarka...”
Kai a k’asa ya amsada Ameen Abbah a daidai sanda Mamy ta shigo da sallama... Kallo guda zakai mata ka fahimci ta damu da damuwan mijin nata, Sameer yai mata sannu da shigowa kana ya mik’e ya basu waje, can k’asar zuciyar tinanin al’amran da suka saka shi a tsaka yake, ala dole ya amsama Abbah gameda maganan aurensa da Siyama dan bazai iya musama Abbah ba sannan a halinda Abbah yake ciki yanzu bai buk’atan k’arin tashin hankali, ya saki murmushi a hankali sanda ya tuna aurensa da d’iyar Haule Wai ya juye kan Raihanah... Al’amarin Allah kenan, haka yake gudanar da al’amaransa ba tareda shawartan kowa ba.... Ya lumshe idanunsa a hankali yana tuno tin sanda ya soma had’uwa da ita farkon dawowarsa Kano sanda ya kusan bigeta da mota tun kan yasan sud’in ‘yanuwan juna ne.... Ya kuma sakin murmushi a hankali kana yasa kai ya fice...
Haule ta murmusa dan dik a zatonta Sawwama tayi haka ne ta kwaso ‘yan daudu da mai gurmi dan ta cazagawa Sahariyya bak’in ciki tinda an fasa bikinta.... Haule ta k’arasa gaban Sawwama tana huci tana nunata da ‘yar yatsa “Ke k’aramar kilaki, k’aramar shed’aniya ni nafi k’arfin kizo har cikin gidana kice zaki cazga min bak’in ciki... Naci uwarki a bariki barikiji na fad’a miki... Tin wuri ki tattari wad’annan ‘yaniskan ku fice min gida tinda ba bayan gari bane...!” Ta k’arashe tana kuma fincika....
‘Yan daudun nan suka shiga kame baki cikin salo suna fad’in “Aaaa Haba yayarmu tarban da zaki mana kenan... Kuma ma ai nan gidan Ubanmu ne zama daram babu fashe Billahillazi...!” Suka k’arashe suna tafe hannaye...
Kan Haule ya d’aure ta dubesu tace “Waye Uban naku....?!”
Salo sukai suna masu kame baki da tafe hannaye suke furta “Chaasss! Ayyye Lantana shafa mata...!” D’ayan yace
Wanda aka kirada Lantana gyara d’aurin k’irji yai had’ida rik’e hab’a kana yace “Waa ki rufa min asiri in mutu a d’aki maza su kaini... Ba’a ji mutuwar sarki a bakina ba wllhi....!”
Haule fah ta soma firgita da lamarin dan har yanzu bama ta lura da matar dake daga gefen mai garaya fuskarta lullub’e cikin mayafi ba.... Harta Sahariyya dake cikin nata damuwar gyara zama tai bayan ta ida birgimanta a k’asa tana kallon wannan show dake gudana a gidansu, kai kowa a wajen tsayuwa baima idanunsa abinci yai da ganin wannan ikon Allah...
Haule ta k’arasa a fusace ta finciko Sawwama tana fad’in “Ke dan uwarki me kike shirya ma d’ahna bak’ar mayya zuri’an jarababbu...” Batakai aya ba Magajiya ta mik’e had’ida yaye rufin kanta tai d’amara da gyalenta ta finciki d’iyarta Sawamma ta koma baya kana tai tsaye gaban Haule tana mai furta “Ke kada ki kuskura ki kuma tab’a min lafiyar d’iya dan wllhi kinji na rantse miki wad’annan mata mazan da kike gani su sauya miki kamanni....!”
Al’ajabi had’ida mamaki ya kuma kama Haule... Dariyar datafi kama data takaici Haule tai kana tace “Yo ai sai kuce min tafe kuke gaba d’aya, kuce bayan gari ne yau gaba d’aya a gidan namu, au ta kasa ne shine bari ta d’auko uwarta ta tayata... Yo ai kun bani kunya tinda kukayo zugan wad’annan asararrun... Ashe dai na cika aji shakkun tunk’arata...!”
Wannan karon murmushi Magajiya tai tana mai k’arema Haule duba daga sama har k’asa kana tace “Sauk’inki d’aya baki kai na zuba kishi dake ba, dan haka gwara ki saduda kiyi biyayya mu zauna lafiya...”
Haule fah bataji batun da kyau ba, mai wannan kilakin take fad’i ne....? Bata ankara ba tajiyo muryar Magajiya tana fad’in Mai gurmi yaci gaba da aikinsa, tana fad’i tana tik’an rawa daga tsakiya ashararrunta na tayata....
Su Amara k’irjin biki mai zasuyi itada k’awayenta banda dariya, harta Sahariyya saida taji dariya ya kufce mata ganin wannan drama dake faruwa a gidansu wanda yafi kama da wasan kwaikwayo tama mance itama cikin nata damuwar take, harta su Fa’iza k’awayen Sahariyya dariya Kawai suke suna fad’in saidai fah Sahariyya tai hak’uri amma wannan al’amari dole su dara su kuma kai gaba...
Haule da duniyar ta kuma juya mata a matuk’ar sanyaye ta isa gaban Magajiya tana fad’in “Mai kikace...?” Wannan karon cikin sanyin gwiwa sosai tai maganar...
Magajiya ta murmusa tace “Yafi miki da kika saduda da wuri... Ki jira mijinki shi zaizo yai maki sauran jawabi, kina iya shigowa fili mu taka a halin yanzu...” Ta k’arshe tana mai janyo hannun Haule tana sakata tai rawa tana bin sautin garayar tana furta “Rawa Haule rawa Haule....!”
Bibbiyu Haule ta soma gani... Itace Alhaji zai mata wannan cin kashin... Aure! Aure yai ba tareda saninta ba, aurenma ya rasa waye zai auro mata sai Magajiya... Take taji wani irin kuka na zuwa mata dan dik yanda takai da ganin ya d’aure bata isa ba bazata iya ba, tana jin yanda zuciyarta Ke fincika daga k’irjinta kaman zai fice... Itakam ta gwammci mutuwa da ganin irin wannan rana.... Zame hannayenta tai daga rik’onda Magajiya tai mata had’ida zama dirshan a k’asa ta jinginu jikin garu ta dafe kai tana furta “Na shiga uku ni Haule... Na shiga uku... Hafiz ya kawo mana annoba cikin zuri’a da ya auro d’iyar matar nan... Yanzu jarabawar bai tsaya akanshi kawai ba harda mijina... Na mutu, Haule k’arshenki yazo...!” Ta k’arashe tana mai sakin wani irin kuka da batasan ya kufce mata ba, suko su Magajiya da ayarinta basu fasa shagalinsu ba su Amara na tayasu....
A haka Hafiz ya shigo gidan ya tadda wannan kwamacala dake faruwa a gidan mahaifin nasa...
***
A can gidan Abbah kaw yanke shawarin had’uwa Washe gari sukai gaba d’aya a can gidan Babbar Yayarsu Abidah bayan kowa ya d’an sami natsuwa zuwa goben... Haka yayi masu gaba d’aya, saidai yau d’in sun kasa rabuwa da juna suka yanke shawarin kwana su duka hud’un a gidan ‘yar uwarsu Mariya, dan yau d’in ji suke tamkar kada su kuma rabuwa da juna, ga yaran Daula tuni sun sake suma sunata murna yau Mominsu ta had’uda family d’inta, tuni dama Daula tayi waya ma Daddy ta sanar dashi halinda ake ciki Farin ciki da al’ajabi ya cika Daddy, yace tai zamanta cikin ‘yan uwanta don da har zai turo driver ya d’aukosu zuwa masauk’i itada yara... Abin fah sai son barka ta ko wanne b’angare Farin ciki ne maras misaltuwa, daga bisani Engr da Sameer sukaima iyayen nasu sallama suka fice kaman kada su rabu da juna, nan Sameer yai rakiyawa Engr zuwa waje suna tafe suna kuma tattaunawa, bayan Engr ya wuce shima Sameer d’in sashen Mahaifinsa ya nufa yana mai zullumin halinda zai tadda mahifin nasa ciki bayan tulin abubuwan da suka faru a yau d’in....
Da sallama saman bakinsa ya nufo cikin parlorn sanda Abbah yai masa izinin shigowa... Ga mamakin Sameer murmushi ya gani kwance saman fuskan Abbah sam bazakace yanada damuwa ba sai ka karancesa sosai ka iya gano hakan....
“Shigo abinka, k’araso Ma’aruf... Dama ina nemanka akwai maganar da zamu tattauna....”
Sameer ya zauna daga gefen k’afan Abbah yana mai gaida Abban... Abbah ya amsa masa har lokacin murmushi ne saman fuskarsa wanda ko ba’ace ba kasan k’arfin hali kawai yake...
Bayan Sameer ya zauna Abbah yaci gaba da fad’in “Akan batun aurenka da d’iyar wajen Yaya...!”
Gaban Sameer ya yanke ya fad’i, dan shi har ya mance da batun wata Sahariyya.... Ya sinkayo Abbah naci gaba da fad’in “ Nasan mai yuwa kanada labarin an sauya aurenka da k’anwar Sahariyya...”
Wannan karon d’agowa ya d’anyi cikeda mamaki kana Abba ya jinjina kai yace “Da alama bakada labari... Ma’aruf..!” Ya kuma kiran sunansa cikeda kulawa...
Wannan karon jiki a sanyaye ya d’ago yana duban Abban...
Abba yaci gaba da fad’in “An maida aurenka kan ‘yaruwarka RAIHANAH... Bayan dik abinda suka faru nasan bakada wani tambayar da zakai gameda wannan al’amari... Kasan Raihanah itace matar da Allah ya zab’ar maka kuma inaso ka rik’eta amana, kada ka dubi abinda mahaifinta yai mana nida mahaifiyarka harma da kai... Ita d’in yarinyar kirkice, Allah Ubangiji yai maku albarka, ya azirtaku da ziri’a d’ayyiba... Ina labarin d’aya matar taka...?”
Sameer da ya tsinci zancen tamkar sauk’ar aradu dikda cewa yaji wani irin sanyi na sauk’ar masa cikin zuciyarsa sanda akace bai aure d’iyar Haule ba, saidai baima San mai yakeji gameda auren Raihanar ba, wani feeling ne da bai isa ya fasalta ba a halin yanzu... Muryar Abbah ya sinkayo yana fad’in “Kai nake tambaya Ma’aruf.... Ina labarin matarka...?”
Sameer ya d’an sosa kansa kad’an kana yace “Em Abbah dama... Dama sai naje Kaduna na dubata...”
Abba ya jinjina kai yace “Toh dama lallai lallai kaje ka duba iyalinka, ka had’e kan iyalanka ku zauna lafiya kaji koh..”
Sameer ya jinjina kai a hankali yana mai furta “Zanyi yanda kace in sha Allah Abbah...”
Abbah ya murmusa kana yace “Allah shi maka albarka...”
Kai a k’asa ya amsada Ameen Abbah a daidai sanda Mamy ta shigo da sallama... Kallo guda zakai mata ka fahimci ta damu da damuwan mijin nata, Sameer yai mata sannu da shigowa kana ya mik’e ya basu waje, can k’asar zuciyar tinanin al’amran da suka saka shi a tsaka yake, ala dole ya amsama Abbah gameda maganan aurensa da Siyama dan bazai iya musama Abbah ba sannan a halinda Abbah yake ciki yanzu bai buk’atan k’arin tashin hankali, ya saki murmushi a hankali sanda ya tuna aurensa da d’iyar Haule Wai ya juye kan Raihanah... Al’amarin Allah kenan, haka yake gudanar da al’amaransa ba tareda shawartan kowa ba.... Ya lumshe idanunsa a hankali yana tuno tin sanda ya soma had’uwa da ita farkon dawowarsa Kano sanda ya kusan bigeta da mota tun kan yasan sud’in ‘yanuwan juna ne.... Ya kuma sakin murmushi a hankali kana yasa kai ya fice...