Sashe 115
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Washe gari ta kama juma’a, tafe suke itada Atika a farfajiyan ofishin nasu, fitowarsu kenan daga d’akin gudanar da shirye shirye, ga tsananin rana da ake kwand’arawa... A gajjiye suka iso d’akin hutun nasu had’ida zubewa saman kujeru a gajjiye.... Atika ta rage mayafinta tana mai gaida Aunty Zilai colleague d’insu dake shirin fita daga d’akin sai zolayarsu take musamman Zulfa’u dashike Aunty Zilai mace ce mai barkwanci da son mutane...
Sauk’e ajiyan zuciya Zulfah tai sanda d’akin ya rage saura su biyu tana mai fifita da takardan dake hannunta a hankali...
Gyara zama Atika tai had’ida tsare k’awar tata da idanu.... D’an dubanta Zulfa’u tai kana tace “Ke kuma fah, wannan kallon na menene... Meke faruwa?”
Atika ta d’an murmusa kad’an kana tace “Ai ke zan tambaya meke faruwa..? Irin wannan ajiyan zuciya da kiketa faman sauk’ewa akai akai tin muna hanya, kodai kiran manager d’in ne bakiso zuwa ba... Ni bakima sanar dani mi ya faru ba... Don’t tell me kin sauya ra’ayi dashi za’ai...?”
Gajeren tsuka Zulfa’u tai kana tace “Ke ai kinga matsalarki kenan, you talk too much, har mutum ya rasa wanne zai amsa miki....”
Atika ta d’an dara kad’an “Zulfa’u mai farin jini mai masoya... Nidai banga aibun Akram ba kuma shima Manager baida wani aibu wllhi, matarsa ma mutuniyar arziki ce takanzo gidan radio d’in nan kwanakin baya, very simple and friendly wllhi...”
Harara Zulfah ta galla mata kana tace “Bazakiyi shaidan mace akan kishi ba, kinsan ance kumallon mata, kibar mace akan mijinta, duk kyaun halinta da kirkinta dole tai kishin abinda take so, ke ni wai ce miki nayi ina sonsa ne ma... Wllhi Atika ni dik kin isheni bari Oga Ameer ya shigo na kaiki sammaci kotunsa....”
Atika ta dara kad’an kana tace “Aunty Zulai ma tayi ta barni, randa dik bana station d’in nan sai kunyi kewata... Kinga tashi mu samu muyi sallah mu koma kafin d’an nacin nan Ameer ya soma kirana, sam banson a had’ani program dashi Wllhi, fidda ficce ne dashi kaman mace...”
Zulfah ta d’an dara tana mai fad’in “Ai Wllhi babu maganin surutun nan naki irin Ameer, jekiyo alwalwa ni na mik’a nawa tintini...” Ta k’arashe tana mai kurb’an bottle water dake rik’e hannunta...
“Aw shine na biyeki naketa zuba, ashe kin riga liman tintini, ai sai kimin bayani...” Tai maganar tana mai d’an jan skirt d’inta sama kad’an, kana ta nufi d’auro alwala...
Tab’e baki kad’an Zulfah tai murmushi saman fuskarta take furta “Ke dai kika sani kuma, uwar ‘yan zuba...”
Wani ajiyan zuciyar ta kuma sauk’ewa tana tunanin encounter da jiya ta samu da Hafiz, ta tina abinda ya fad’i mata cewa bazata tsere masa ba dik rintsi sai ta dawo gareshi, he would make sure of that, ita d’in tasa ce shi kad’ai and no one else... Fuzar da iska mai d’umi tai a hankali, daidai nan wayarta ta soma ringing.... Takai dubantaga wayar dake aje saman table, lamba ce babu suna, ta d’an d’auki lokaci tana duban lambar har saida ta kusan tsinkewa kana ta d’aga da sallama... Shiru ba’a ce mata komai daga d’aya b’angaren ba, ta kuma yin sallama a karo na biyu nan ma shiru ba’ace komai ba, toh waye wannan mai kiranta yai shiru, tin kwanaki hakan ke faruwa da ita tin tana gidan Aunty Bara’atu, sai a kirata ai shiru kuma kaman da different lines ake mata hakan, da ace da layi guda ne tabbas da tai noticing layin ta daina d’agawa... D’an tab’e baki tai kana ta katse kiran tana mai addu’an neman tsari daga duk mai nemanta da sharri cikin zuciyarta.... Katse kiran keda wuya taji sautin shigowar message a inbox d’inta, saurin bud’ewa tai da niyyan karance sak’on, saidai abinda ta gani cikin sak’on ya bala’in d’aure mata kai had’ida bata mamaki...
_Sallamarki kad’ai ta wadatarda zuciyar dake k’ishin ruwan sauraren muryarki_
Ta karance sak’on yafi sau abinda yafi, ta lura dik ranar da ba itace on duty na gudanar da shirin da take yi ba sai mai kiran nata ya kirata a ranan, dik randa itace da duty ta gudanarda program toh ko shakka babu mai kiran nata bazai kira ba... Toh waye wannan...? Tambayar daya tsaya mata a Rai, a haka Atika ta k’araso ta sameta, bata b’oyewa Atika komai ba harta sak’on saida ta nuna mata...
Atika ma sosai abin ya bata mamaki, Toh ko waye shi kuma wannan sai Allah.... Dafa Zulfa’u Atika tai kana tace “Karkisa komai ma ranki k’awata, ci gaba da fawwalla wa Allah lamuranki da sannu zai rik’i ragamar al’amranki... Ki kwantar da hankalinki kinji koh... Dikda bamusan wanene wannan Mr Unknown d’in ba shima ki sakashi cikin jerin masu neman aurenki wa ya sani ko da Mr Unknown za’ai...” Ta k’arashe cikeda shak’iyanci....
Zulfah ta galla mata harara kana tace “Ai ke matsalarki kenan komai sai kin sako wasa ciki, wllhi dikdai wanda ya zamto mijinki nada aiki, ni ki tashi muje kafin su soma damun mu da waya...” Ta k’arashe tana gyara zaman mayafinta had’ida mik’ewa tsaye...
Dariya Atika keyi suna tafe tana kuma zolayarta da *Mr Unknown*
A haka dai har ranar ta k’are masu tinanin sak’o da wayar Mr Unknown kaman yanda suka saka mashi itada Atika bai k’yaleta ba... A hanya suna tafe suna neman adaidaita Manager ya k’araso, babu yanda baiyi ba ya rage masu hanya atafau Zulfa’u tak’i ala dole Manager ya k’yalesu badon yaso ba, haka Atika ta dinga mata mita a hanya.... Zulfah dai cewa tai taji amma wllhi bazasu shiga motar Manager ba... Kaman daga sama sai ganin Hafiz sukai gabansu tamkar wanda aka jefo... Take wutan fuskar Zulfa’u ya d’auke gaba d’aya, Atikar ma had’e rai tai tana watsa masa muguwar kallo....
Gaban Zulfa’u yaja ya tsaya yana wani huci shi kad’ai “Baba Alhaji ya sanar dani yanda sukaida Abbah... Zulfah kar mu bawa iyayenmu wahala, lokaci yayi da zaki daina wannan game d’in naki ki dawo gidan mijinki....” Kaman jira Atika take nan ya katsesa da fad’in “Wane mijin...? Ko tayi aure ne ban sani ba... Ko haka shi Baba Alhajin yace maka...?”
Da tsananin mamaki ya kaikaito yana duban Atika, lokaci guda ya d’aura hannayensa saman kunkuminsa yana k’are mata duba ta wulak’anci “Ke kuma wacece da ina magana da matata zaki tsoma baki... How dare you..?!”
Atika kaw dikda k’irjinta dake bugawa bata fasa aika masa harara ba tana fad’in “Ni ce bakinta idan ita bazata bud’e baki ta saka ka a yanda ya dace dakai ba... Ka fitar hark’arta ka daina wahalar da iyayenka don Zulfa’u ta maka wuya wllhi, ta riga tai maka nisa, nisarda har abada bazaka kuma hangota ba...”
“Ke...!!” Ya fad’i cikeda mamaki yana mai matsowa kusanta, daidai lokacin Zulfa’u ta shiga tsakaninsu, har lokacin fuskarta a tamke yake... “Ya Hafiz banson sauran mutuncin da nake ganinka dashi ya k’are, kaiwa Allah ka fita hark’ata ko ba don komai ba ko dan darajan Khausar dake kwance k’asa...!”
Mamaki ya cika Hafiz, bai daina huci yana duban Zulfah ba, fad’i yake “Ni kike cewa na fita hark’arki Zulfah... Kinajin abinda kike fad’i kuwa... Ni Hafiz kike cema na fita hark’arki... Toh waye kike so ki aura.. Wancan d’an iska karen farautar ‘yan siyasan ko kuwa wannan manemin matan banzan manager d’in naku kike so... Tell me waye kike so cikinsu...”
“Kan hanya muke Ya Hafiz, zaka iya adana rashin hankalin naka har mu bar bakin kwalta?...”. Bata kai aya ba ya d’aga hannu da niyyan kai mata mari yake fad’in “Ke ni kike fad’iwa magana haka saikace wani sa’arki....!”
Bai ankara ba sai ji yai an damk’e hannunsa ya gagara koda motsata.... Gaba d’aya suka kai dubansu gareshi don suma kansu basuji zuwan nasa ba....
Cikin dakekkiyar murya Akram Ke fad’in “If you dare lay a finger on her, zan nuna maka akwai banbanci tsakanin namijin K’warai da kuma namijin da ya rako mata duniya....”
Magaji dake gefe sai sannan ya k’araso yana janye Hafiz yake baiwa su Zulfa’u da Akram hak’uri.. Yana jan Hafiz d’in yake ci gaba da fad’in “Da ace nasan rashin daraja zakazo yi wllhi ban kawoka ba, Dan Allah kuyi hak’uri... Zulfa’u Kiyi hak’uri, laifina ne dana kawosa, bansan abinda zaizo miki ba kenan... A kullum nuna mana yake ya canza bansan har yanzu yana nan da halinsa ba... Kuyi hak’uri Dan Allah..”
Fincika Hafiz yai yana fad’in “Sai wani basu hak’uri kake saikace an masu wani abin... Baka ganine I’m the real victim here, wannan d’an iskan d’an siyasan shi yake hure mata kunne, kuma Zulfa’u k’anwata ce zan iya hukuntata a ko ina a kuma koda yaushe...”
Ya kuma fincika ya tako gaban Akram yana ci gaba da huci yake fad’in “Bari kaji na fad’a maka, ka rubuta ka ajiye kai Karen farautan ‘yan siyasa... Zaka iya hure mata kunne ta saurareka amma na sani kud’inka bazai tab’a sayan soyayyar Zulfa’u ba don abin duniya bai rufe mata ido ba ni zan baka shaida akan haka... Amma ka sani abinda har ka mutu bazaka tab’a samu daga gareta ba...” Yai wata murmushi har lokacin fuskarsa dab dana Akram kana yaci gaba da fad’in “I’m her first husband her first love... Na saka gudan jinina cikin jikinta tai wata tara ta fito duniya ta kuma raineta... Kar ka mance sunce da tsohuwar zuma ake magani...”
Murmushi da gefen baki kurum Akram keyi kana yace “Duk abinda ka fad’i are now in the past, and I promise you gabanta zaifi bayanta kyau, ka rubuta ka ajiye....!”Ya k’arashe maganar yana mai murmusawa cikeda k’asaita, k’asa k’asa suke maganar don tuni Yusuf ya bud’ewa su Zulfah da Atika mota sun shige...
Hafiz da zuciyarsa ke tsananin masa d’aci ya yunk’ura zai kai damk’awa Akram... Akram ya kuma gyara tsayuwarsa kana yace “And one more thing, kar ka kuskura ko labari na sake jin kana harassing d’inta,... Idan ba haka ba...?” Ya kuma yin wata murmushi kana yasa hannu ya d’an bubbuga kafad’an Hafiz yace “I’ll forget kaida ita kun had’a jini...” Daga haka sa kai yayi ya nufi mota...
Hafiz naci gaba da huci ya shiga bibbige yanda Akram ya dafasa... Magaji na janyoshi yana wani doguwa yake fad’in “Toh mai zaka min, ‘yan dabanku na siyasa zaka turo min ko mene... Kai naci uwarka a bariki barikaji mu mai license mukai...”
Dafasa Magaji yai yana mai ci gaba da sababi kana Magaji yace “Yanzu kuma da waye kake wai, baka ganin yayi gaba ne ya Barka da k’ura.... Abokina magana ta gaskiya lokaci yayi da zaka daina wannan haukar taka kaje gida ka rungumi Sawwamarka ku sasanta kuyi zaman lafiya, ka k’yale Zulfa’u ta auri wanda take so...” Ya k’arashe maganar yana k’unshe dariyarsa
Harara Hafiz ya galla masa kana yace “Ai na jima da sanin kaima hassadar dawowar matata kake min, kuma wllhi duk sai na baku mamaki sai na dawo da matata gareni... Wannan d’an siyasan da ‘yan daba yake tak’ama toh baisan da wa yake takara ba, zan nuna masa neman aure ba takaran kujeran mulki bane da ake saya da tsabar kud’i...”
Magaji na murmushi yake fad’in “Shima soyayyar akwai wanda ake saye da kud’i sai kai hattara...”
Hafiz na ci gaba da watsa masa harara yake fad’in “Wllhi banda Zulfa’u banida haufi akanta...” Yai murmushi yana mai shafa hab’arsa kad’an kana yace “Zan b’ullo masa ta yanda bai tsammani ba, badai gadaransa ‘yaniskan gari bane... Toh mu zuba nida shi... Sawwama...!” Yayi wata murmushi yana mai duban Magaji da bai fahimci nufinsa ba... Dafa Magani yai kad’an kana yace “Zata min amfani abokina... Tada babur muje kaji...” Shi kad’ai sai sakin murmushi yake yana ayyana yanda plan d’insa zatai aiki....
Magaji dai girgiza kai kawai yai kana ya tada mashin d’insa yana fad’in “Allah ya kyauta...”
Sauk’e ajiyan zuciya Zulfah tai sanda d’akin ya rage saura su biyu tana mai fifita da takardan dake hannunta a hankali...
Gyara zama Atika tai had’ida tsare k’awar tata da idanu.... D’an dubanta Zulfa’u tai kana tace “Ke kuma fah, wannan kallon na menene... Meke faruwa?”
Atika ta d’an murmusa kad’an kana tace “Ai ke zan tambaya meke faruwa..? Irin wannan ajiyan zuciya da kiketa faman sauk’ewa akai akai tin muna hanya, kodai kiran manager d’in ne bakiso zuwa ba... Ni bakima sanar dani mi ya faru ba... Don’t tell me kin sauya ra’ayi dashi za’ai...?”
Gajeren tsuka Zulfa’u tai kana tace “Ke ai kinga matsalarki kenan, you talk too much, har mutum ya rasa wanne zai amsa miki....”
Atika ta d’an dara kad’an “Zulfa’u mai farin jini mai masoya... Nidai banga aibun Akram ba kuma shima Manager baida wani aibu wllhi, matarsa ma mutuniyar arziki ce takanzo gidan radio d’in nan kwanakin baya, very simple and friendly wllhi...”
Harara Zulfah ta galla mata kana tace “Bazakiyi shaidan mace akan kishi ba, kinsan ance kumallon mata, kibar mace akan mijinta, duk kyaun halinta da kirkinta dole tai kishin abinda take so, ke ni wai ce miki nayi ina sonsa ne ma... Wllhi Atika ni dik kin isheni bari Oga Ameer ya shigo na kaiki sammaci kotunsa....”
Atika ta dara kad’an kana tace “Aunty Zulai ma tayi ta barni, randa dik bana station d’in nan sai kunyi kewata... Kinga tashi mu samu muyi sallah mu koma kafin d’an nacin nan Ameer ya soma kirana, sam banson a had’ani program dashi Wllhi, fidda ficce ne dashi kaman mace...”
Zulfah ta d’an dara tana mai fad’in “Ai Wllhi babu maganin surutun nan naki irin Ameer, jekiyo alwalwa ni na mik’a nawa tintini...” Ta k’arashe tana mai kurb’an bottle water dake rik’e hannunta...
“Aw shine na biyeki naketa zuba, ashe kin riga liman tintini, ai sai kimin bayani...” Tai maganar tana mai d’an jan skirt d’inta sama kad’an, kana ta nufi d’auro alwala...
Tab’e baki kad’an Zulfah tai murmushi saman fuskarta take furta “Ke dai kika sani kuma, uwar ‘yan zuba...”
Wani ajiyan zuciyar ta kuma sauk’ewa tana tunanin encounter da jiya ta samu da Hafiz, ta tina abinda ya fad’i mata cewa bazata tsere masa ba dik rintsi sai ta dawo gareshi, he would make sure of that, ita d’in tasa ce shi kad’ai and no one else... Fuzar da iska mai d’umi tai a hankali, daidai nan wayarta ta soma ringing.... Takai dubantaga wayar dake aje saman table, lamba ce babu suna, ta d’an d’auki lokaci tana duban lambar har saida ta kusan tsinkewa kana ta d’aga da sallama... Shiru ba’a ce mata komai daga d’aya b’angaren ba, ta kuma yin sallama a karo na biyu nan ma shiru ba’ace komai ba, toh waye wannan mai kiranta yai shiru, tin kwanaki hakan ke faruwa da ita tin tana gidan Aunty Bara’atu, sai a kirata ai shiru kuma kaman da different lines ake mata hakan, da ace da layi guda ne tabbas da tai noticing layin ta daina d’agawa... D’an tab’e baki tai kana ta katse kiran tana mai addu’an neman tsari daga duk mai nemanta da sharri cikin zuciyarta.... Katse kiran keda wuya taji sautin shigowar message a inbox d’inta, saurin bud’ewa tai da niyyan karance sak’on, saidai abinda ta gani cikin sak’on ya bala’in d’aure mata kai had’ida bata mamaki...
_Sallamarki kad’ai ta wadatarda zuciyar dake k’ishin ruwan sauraren muryarki_
Ta karance sak’on yafi sau abinda yafi, ta lura dik ranar da ba itace on duty na gudanar da shirin da take yi ba sai mai kiran nata ya kirata a ranan, dik randa itace da duty ta gudanarda program toh ko shakka babu mai kiran nata bazai kira ba... Toh waye wannan...? Tambayar daya tsaya mata a Rai, a haka Atika ta k’araso ta sameta, bata b’oyewa Atika komai ba harta sak’on saida ta nuna mata...
Atika ma sosai abin ya bata mamaki, Toh ko waye shi kuma wannan sai Allah.... Dafa Zulfa’u Atika tai kana tace “Karkisa komai ma ranki k’awata, ci gaba da fawwalla wa Allah lamuranki da sannu zai rik’i ragamar al’amranki... Ki kwantar da hankalinki kinji koh... Dikda bamusan wanene wannan Mr Unknown d’in ba shima ki sakashi cikin jerin masu neman aurenki wa ya sani ko da Mr Unknown za’ai...” Ta k’arashe cikeda shak’iyanci....
Zulfah ta galla mata harara kana tace “Ai ke matsalarki kenan komai sai kin sako wasa ciki, wllhi dikdai wanda ya zamto mijinki nada aiki, ni ki tashi muje kafin su soma damun mu da waya...” Ta k’arashe tana gyara zaman mayafinta had’ida mik’ewa tsaye...
Dariya Atika keyi suna tafe tana kuma zolayarta da *Mr Unknown*
A haka dai har ranar ta k’are masu tinanin sak’o da wayar Mr Unknown kaman yanda suka saka mashi itada Atika bai k’yaleta ba... A hanya suna tafe suna neman adaidaita Manager ya k’araso, babu yanda baiyi ba ya rage masu hanya atafau Zulfa’u tak’i ala dole Manager ya k’yalesu badon yaso ba, haka Atika ta dinga mata mita a hanya.... Zulfah dai cewa tai taji amma wllhi bazasu shiga motar Manager ba... Kaman daga sama sai ganin Hafiz sukai gabansu tamkar wanda aka jefo... Take wutan fuskar Zulfa’u ya d’auke gaba d’aya, Atikar ma had’e rai tai tana watsa masa muguwar kallo....
Gaban Zulfa’u yaja ya tsaya yana wani huci shi kad’ai “Baba Alhaji ya sanar dani yanda sukaida Abbah... Zulfah kar mu bawa iyayenmu wahala, lokaci yayi da zaki daina wannan game d’in naki ki dawo gidan mijinki....” Kaman jira Atika take nan ya katsesa da fad’in “Wane mijin...? Ko tayi aure ne ban sani ba... Ko haka shi Baba Alhajin yace maka...?”
Da tsananin mamaki ya kaikaito yana duban Atika, lokaci guda ya d’aura hannayensa saman kunkuminsa yana k’are mata duba ta wulak’anci “Ke kuma wacece da ina magana da matata zaki tsoma baki... How dare you..?!”
Atika kaw dikda k’irjinta dake bugawa bata fasa aika masa harara ba tana fad’in “Ni ce bakinta idan ita bazata bud’e baki ta saka ka a yanda ya dace dakai ba... Ka fitar hark’arta ka daina wahalar da iyayenka don Zulfa’u ta maka wuya wllhi, ta riga tai maka nisa, nisarda har abada bazaka kuma hangota ba...”
“Ke...!!” Ya fad’i cikeda mamaki yana mai matsowa kusanta, daidai lokacin Zulfa’u ta shiga tsakaninsu, har lokacin fuskarta a tamke yake... “Ya Hafiz banson sauran mutuncin da nake ganinka dashi ya k’are, kaiwa Allah ka fita hark’ata ko ba don komai ba ko dan darajan Khausar dake kwance k’asa...!”
Mamaki ya cika Hafiz, bai daina huci yana duban Zulfah ba, fad’i yake “Ni kike cewa na fita hark’arki Zulfah... Kinajin abinda kike fad’i kuwa... Ni Hafiz kike cema na fita hark’arki... Toh waye kike so ki aura.. Wancan d’an iska karen farautar ‘yan siyasan ko kuwa wannan manemin matan banzan manager d’in naku kike so... Tell me waye kike so cikinsu...”
“Kan hanya muke Ya Hafiz, zaka iya adana rashin hankalin naka har mu bar bakin kwalta?...”. Bata kai aya ba ya d’aga hannu da niyyan kai mata mari yake fad’in “Ke ni kike fad’iwa magana haka saikace wani sa’arki....!”
Bai ankara ba sai ji yai an damk’e hannunsa ya gagara koda motsata.... Gaba d’aya suka kai dubansu gareshi don suma kansu basuji zuwan nasa ba....
Cikin dakekkiyar murya Akram Ke fad’in “If you dare lay a finger on her, zan nuna maka akwai banbanci tsakanin namijin K’warai da kuma namijin da ya rako mata duniya....”
Magaji dake gefe sai sannan ya k’araso yana janye Hafiz yake baiwa su Zulfa’u da Akram hak’uri.. Yana jan Hafiz d’in yake ci gaba da fad’in “Da ace nasan rashin daraja zakazo yi wllhi ban kawoka ba, Dan Allah kuyi hak’uri... Zulfa’u Kiyi hak’uri, laifina ne dana kawosa, bansan abinda zaizo miki ba kenan... A kullum nuna mana yake ya canza bansan har yanzu yana nan da halinsa ba... Kuyi hak’uri Dan Allah..”
Fincika Hafiz yai yana fad’in “Sai wani basu hak’uri kake saikace an masu wani abin... Baka ganine I’m the real victim here, wannan d’an iskan d’an siyasan shi yake hure mata kunne, kuma Zulfa’u k’anwata ce zan iya hukuntata a ko ina a kuma koda yaushe...”
Ya kuma fincika ya tako gaban Akram yana ci gaba da huci yake fad’in “Bari kaji na fad’a maka, ka rubuta ka ajiye kai Karen farautan ‘yan siyasa... Zaka iya hure mata kunne ta saurareka amma na sani kud’inka bazai tab’a sayan soyayyar Zulfa’u ba don abin duniya bai rufe mata ido ba ni zan baka shaida akan haka... Amma ka sani abinda har ka mutu bazaka tab’a samu daga gareta ba...” Yai wata murmushi har lokacin fuskarsa dab dana Akram kana yaci gaba da fad’in “I’m her first husband her first love... Na saka gudan jinina cikin jikinta tai wata tara ta fito duniya ta kuma raineta... Kar ka mance sunce da tsohuwar zuma ake magani...”
Murmushi da gefen baki kurum Akram keyi kana yace “Duk abinda ka fad’i are now in the past, and I promise you gabanta zaifi bayanta kyau, ka rubuta ka ajiye....!”Ya k’arashe maganar yana mai murmusawa cikeda k’asaita, k’asa k’asa suke maganar don tuni Yusuf ya bud’ewa su Zulfah da Atika mota sun shige...
Hafiz da zuciyarsa ke tsananin masa d’aci ya yunk’ura zai kai damk’awa Akram... Akram ya kuma gyara tsayuwarsa kana yace “And one more thing, kar ka kuskura ko labari na sake jin kana harassing d’inta,... Idan ba haka ba...?” Ya kuma yin wata murmushi kana yasa hannu ya d’an bubbuga kafad’an Hafiz yace “I’ll forget kaida ita kun had’a jini...” Daga haka sa kai yayi ya nufi mota...
Hafiz naci gaba da huci ya shiga bibbige yanda Akram ya dafasa... Magaji na janyoshi yana wani doguwa yake fad’in “Toh mai zaka min, ‘yan dabanku na siyasa zaka turo min ko mene... Kai naci uwarka a bariki barikaji mu mai license mukai...”
Dafasa Magaji yai yana mai ci gaba da sababi kana Magaji yace “Yanzu kuma da waye kake wai, baka ganin yayi gaba ne ya Barka da k’ura.... Abokina magana ta gaskiya lokaci yayi da zaka daina wannan haukar taka kaje gida ka rungumi Sawwamarka ku sasanta kuyi zaman lafiya, ka k’yale Zulfa’u ta auri wanda take so...” Ya k’arashe maganar yana k’unshe dariyarsa
Harara Hafiz ya galla masa kana yace “Ai na jima da sanin kaima hassadar dawowar matata kake min, kuma wllhi duk sai na baku mamaki sai na dawo da matata gareni... Wannan d’an siyasan da ‘yan daba yake tak’ama toh baisan da wa yake takara ba, zan nuna masa neman aure ba takaran kujeran mulki bane da ake saya da tsabar kud’i...”
Magaji na murmushi yake fad’in “Shima soyayyar akwai wanda ake saye da kud’i sai kai hattara...”
Hafiz na ci gaba da watsa masa harara yake fad’in “Wllhi banda Zulfa’u banida haufi akanta...” Yai murmushi yana mai shafa hab’arsa kad’an kana yace “Zan b’ullo masa ta yanda bai tsammani ba, badai gadaransa ‘yaniskan gari bane... Toh mu zuba nida shi... Sawwama...!” Yayi wata murmushi yana mai duban Magaji da bai fahimci nufinsa ba... Dafa Magani yai kad’an kana yace “Zata min amfani abokina... Tada babur muje kaji...” Shi kad’ai sai sakin murmushi yake yana ayyana yanda plan d’insa zatai aiki....
Magaji dai girgiza kai kawai yai kana ya tada mashin d’insa yana fad’in “Allah ya kyauta...”