Sashe 42
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Batakai aya ba Mamani ta sauk’e mata sanda a baya tana fad’in “Toh islamiyya babu kalan wanda banyi ba ja’irar yarinya mai halin tsiya na uwarta... Yo wani alfanu zakuyiwa Adamu bayan cinye masa d’an abincin da yake fafutika da kuke...” Batakai aya ba ta hangi Basmah ta tsallake abinta ta barta nan tsaye tana sababin da babu gaira balle dalili...
Mamani ta shiga doka salallami tana aikawa Basmah zagi daga tsallake had’ida nunata da sanda, lokaci guda tasa kai zata tsallake k’iris ya rage mai motar dake tafe saman kwalta d’in bai d’agata ba, Allah yaso ba wani tsananin gudu yake ba...
Mamani ta d’ago masa hannu biyu sanda yaci birki tana fad’in “Toh bawan Allah naga dai kwalta d’in nan ta gwamnati ce don haka a dakata a barni na shige....” Tana tsallakewa tanai masa gwalo had’ida furta “Oho dai baka kad’eni ba dai jeka dai...”
Maimaikon tsohuwar ta basa takaici saima dariya data basa, yaja gefe yai parking ya fito yana gaida Mamani had’ida furta “Sannu Baaba bakidaiji ciwo ba....?”
Basmah tabishi da kallo tana tunanin inda ta sanshi nan ta tuna k’ofar gidansu ta tab’a ganinshi tareda Addah Nabilan Baffah Usman.....
Mamani tace “Yanda ka gani yaro am babu abinda ya sameni, kyan k’irane dani...”
Khalid ya d’an dara kana yace “Gaskiya Baaba na yarda kinada kyaun k’ira, ayi hak’uri dai ba tuk’in ganganci nake ba...”
Mamani data fahimci ya mata zubin masu kud’i tace “Ahtoh idan kunga talaka saman kwalta yanda kasan gwamnatin nakune ku kad’ai, yaro yanzu dubi maton da kake tuk’awa saikace ta gwamna da shugaban k’asa... Oh wasu iyayen dai Allah ya amshi addu’arsu sun haifi masu mulki da masu arziki...”
Jin zata saki layi yasa Basmah janyota tana fad’in “Mamani muje kar dare ya mana...”
“Ke da Allah cikani dacan ba guduna kike ba, saidai ki k’arasa tafiyarki amma nikam saina d’ana wannan maton mai kama data gwamna, yaro zoka bud’emin...”
Khalid na murmushi ya bud’e mata ya rik’e mata sandarta ya gyara mata yanda zataji dad’in zama, Basmah dai sai kallon ikon Allah take wato da ace bata gane Mutumin ba ahikenan idanma d’an yanke kai ne Mamani sabida tsabagen kwad’ayi da son abin duniyarta ta shige abinta, girgiza kai Basmah tai had’ida yin k’wafa ta shige ta rik’e Mamani kafin tai masa wani b’aranb’araman a motar, lokaci guda take tunanin yanda Nabilah zata d’au abin...
Khalid na tafe Dattijuwar na jansa da hira wanda akasarin hiran nata marassa kangado ne ko ba’ace maka ba kasan tsufa ke d’awainiya da ita..
Bai ida shan mamaki ba saida Basmah ta nuna masa gidan nasu... Ya dubesu yana mamaki zuciyarsa na masa fari k’al don idan har wannan Kakar Nabilah ce tabbas yasan zai samu wajen zama sosai ta wajenta...
Mamani sai yaba hankalinsa take yayinda Khalid yaji dad’in ci gaba da janta da fira... K’arahe dai har Basmah ta shige gida takaiwa iyayenta rahoton abindake faruwa, sukakaw yo gangami don ganema idanunsu dama tun kwanakin baya suke kad’a gurmi tsakaninsu cewa wani had’edd’en saurayi ke zuwa wajen Nabilah saidai babu wanda ya isa ya fito fili ya fasa gurmin sanin cewa wacece Nabilah...
Nan suka hangesu tafe sun nufi sahen Mamanin da Khalid d’in...
Nabilah kaw da dawowarta kenan daga makaranta ta sauk’a a adaidaita ta hangi motar Khalid k’ofar gidansu, mamaki ya isheta musamman data iso wajen taga alamun babu kowa cikin motar.. Gabanta na dukan tara tara ta nufi cikin gida....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*35*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Tinda ta shigo gida ta kasa zaune ta kasa tsaye, yanda take tunanin zataga Khalid bata ganshi ba, toh kodai ba motarsa bace... No she can’t be mistaken tabbas motarsa ce, toh ina yake...? Kodai aje motar kawai yai k’ofar gidansu...? Amma mai zai kawo motar tasa k’ofar gidan nasu...?
Ita kad’ai sai sak’e sak’e take, ta sak’a wannan ta warware wancan, Marliya dake zaune gaban socket tana gugan kaya hankalce take da ‘yar uwar tata, a ‘yan kwanakin sosai ta fahimci canzawa da Nabilah tai, wasu lokutan ko magana kake mata bata amsawa sai ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi, balle daren jiya yanda taji tana waya ta tabbata da wani take wayar...
Nabilah ta kuma mik’ewa zata fice a karo na kusan hud’u... Marliya ta katseta da fad’in “Wai ina kike zuwa ne... Lafiya kuwa...?”
D’an dubanta Nabilah tai a yatsine kana tace “Toh uwar sa ido kitchen zani wajen Mamy, koda magana ne... Uwata...?”
K’unshe dariyarta Marliya tai kana tace “A’a Allah baki hak’uri...”
Nabilah tai gajeren tsuka kana ta fice... Saida ta kuma sad’ad’awa ta lek’a sashen Abbah kaman wata munafuka kafin ta dawo kitchen ta tadda Mamy tuni ta ida abincin dare ta zuzzuba...
Gaisar da Mamy ta somayi tana tayata jere abincin....
Mamy da tun ganin Sameer take fama da tinane tinane sama sama ta amsa Nabilar kana ta umarceta ta d’au abincin Mamani takai, Nabilah a duniyarta ta tsani a aiketa sashen Mamani, gaisuwa ma don dole ke kaita tasan saura sarai idan ta tsallake kwana guda bataje ta gaidata ba d’aid’aya Mamy zata mata...
Babu halin ta doje taje ga Marliya a parlor na zaune bataga fuskan hakan ba balle ma ko a mafarki bata isa ta fad’iwa mahaifiyar tata haka ba...
D’aukan abincin tai ta fice yanda taci karo da Marliya a hanya ta ida gugan zata nufo kitchen wajen Mamy kafin Mamy tai mata tatas daga ita har gugan nata tace wasanta ta zaunayi tana ganinta a kitchen donma itace ba Nabilah ba datasaba shan mitan Mamy wanda gwara ai maka duka a cewar Nabilah...
Tareta Nabilah tai da fad’in “Ke Leeya wai bakiga bak’o ya shigo gidan nan ba....?”
Marliya ta dubeta da mamaki kana ta girgiza kai tace bak’o kuma...?”
Nabilah ta jinjina kai tace “Eh mana Abbah baiyi bak’o ba...?”
Marliya ta d’anyi shiru tamkar mai tunani kana ta girgiza kai tace “Gaskiya ni banga wani bak’o ba hasalima Abbah bai dawo ba ko kinga motarsa a gareji ne...?”
Nabilah ta d’an tab’e baki tace “Yo ina na lura, kinga zo kishige kafin Mamy ta lek’o...”
Aiko bata kai aya ba Mamyn ta lek’o tana fad’in “Wai ba aikanki akai ba Nabilah... Ke kuma kin tsaya biyeta naki aikan na jiranki.... Tsayuwar mai kuke ne..?”
Ko wacce tai hanyarta suna baiwa Mamy hak’uri, Marliya ta rab’a ta gefenta ta shige tana tunanin yau d’ain kaman wani abin na damun Mamy...
Tana tafe tana tunanin mai ya kawo motarsa k’ofar gidansu, kaman daga sama ta hangesa da Mamani biyedashi da alama ya fito tafiya ne...
K’iris ya rage Nabilah bata kifar da abincin ba, wannan wane irin mutum ne... Yau Abbanta gobe Kakarta... Shin miye tsakanin Khalid da mutanen gidan....
K’irjinta yaci gaba da wani irin bugu.... Tai saurin sa kai zata juya saidai tuni Khalid ya hangota...
Bud’e murya yai kafin ta fice a k’ofar Mamanin yace “Aah k’araso mana aima tafiya zanyi....”
Maganar da yayi ya sanya Mamani dake faman masa zuba kai dubanta ga k’ofar...
Nabilah ta tsaya cak ta kasa ci gaba da tafiya, tamkar ta zunduma a guje haka taji gashi ta kasa juyowa...
Mamani kaw ganin yarinyar da ake magana da ita tak’i juyowa ya sanyata yab’e baki tace “Ke wacece tsaye wajen nan ko bakijin magana ne...?” Nan ma Nabilah bata juyo ba sai rintse idanunta da tai da k’arfin gaske...
Mamani ta nufeta cikin dogara sandarta tana fad’in “Ai wato ina fad’a maka Haladu sam yaran gidan nan basajin magana, gado sukai wajen iyayensu mata...”
Jin zata saki layi ya sanya Nabilah saurin juyowa tana aika mata mugun kallo baki a cune, fuska babu alamun walwala tace “Aini aika na kawo kuma bansan kinada bak’o ba...” Tasa kai abinta zata shige d’akin dukda cewa Khalid tsaye yake wajen, da k’yar ta wuce gabansa musamman data tuna ko mayafi babu jikinta...
Mamani ta dawo da baya tana fad’in “Kaga rashin kunyar tasu koh... Toh wannan ina fad’i maka itace babbarsu a rashin ta ido, batada kunya ina fad’a maka babban abin takaicinma wai sunana gareta...”
Khalid kaw banda murmushi yana satan kallon Nabilah data had’e gabas da yamma baya komai, Mamani tace dashi shigo ai kaci abinci, baka bar gidan nan ba sai kaci abinci Yaron arziki Haladu....”
Wato har cikin ransa yakejin banbarak’wai d’in nan idan ta kirasa Haladu shi bai tab’a sanin mai suna Khalid ake fad’iwa hakan ba sai a baki Mamani...
Ya d’an shafi kansa kad’an yace “Baaba ba Haladu ba Khalid sunan...”
Mamani ta dubesa tsegege kana tace “Kajimin dai, wayace maka ba sunan kenan ba, ai asalin sunan kenan Haladu mu haka muka sani, kuma ka kirani Mamani don haka kowa ke kirana kaji koh shige muje...” Ta k’arashe tana turo shi ciki ta dawo dashi parlorn, sosai sukaso baiwa Nabilah dariya ganin draman Khalid kesha shida Mamani...
Batabi takansu ba ta mik’e zata fice Khalid ya bita da kallo yanda tai tamkar bata tab’a saninsa ba ko gaisuwar fatar baki bata masa ba...
Mamani ta tsareta da fad’in “Ke ke dakata shige ki kawo masa faranti da cokali yaci abinci... Kuma ki kawo na ‘yan gayu don kin gansa sarai d’an gaye ne...”
Nabilah ta dubeta a kufule kana takai dubanta ga Khalid wanda fuskarsa kega wayar salulansa, tana jira taji yace bazaici ba ta sami excuse d’in tafiya amma da yake d’an duniya ne shiru yai alamun zaicin kenan...
Mamani ta katseta da fad’in “Zaki wuce ne kokuwa....?”
K’wafa tai a hankali kana tasa kai ta shige kitchen d’in Mamanin da ba girki ake ciki ba kawai dai kayan amfani ne ciki...
Plate da spoon ta d’auko ta d’auraye had’ida serving spoon ta ijiye saman tray ta dawo fuska a d’aure ta dangwala kusada k’afafunsa....
“Kaga rashin hankalin nata koh, toh k’one masa k’afafu su zama bak’ak’e tinda naki bak’i ne....”
Nabilah datazo wuya hak’urinta ya gaza tace “Aidai wajenki na samo bak’in k’afar tinda na Mamy na fari ne tass....” Tai maganar tana murgud’a baki....
“Kaji koh.. Kaji rashin kunyar tata, ai Manu ya rasa d’ah tinda ya Ma’aruf sauran kam duk gayyan yuyuyu ne... Zuba mashi abincin...” Ta k’arashe tana gwagwiyan goro lokaci guda ta mik’e ta nufi d’aki kaman mai neman wani abin...
Mamani ta shiga doka salallami tana aikawa Basmah zagi daga tsallake had’ida nunata da sanda, lokaci guda tasa kai zata tsallake k’iris ya rage mai motar dake tafe saman kwalta d’in bai d’agata ba, Allah yaso ba wani tsananin gudu yake ba...
Mamani ta d’ago masa hannu biyu sanda yaci birki tana fad’in “Toh bawan Allah naga dai kwalta d’in nan ta gwamnati ce don haka a dakata a barni na shige....” Tana tsallakewa tanai masa gwalo had’ida furta “Oho dai baka kad’eni ba dai jeka dai...”
Maimaikon tsohuwar ta basa takaici saima dariya data basa, yaja gefe yai parking ya fito yana gaida Mamani had’ida furta “Sannu Baaba bakidaiji ciwo ba....?”
Basmah tabishi da kallo tana tunanin inda ta sanshi nan ta tuna k’ofar gidansu ta tab’a ganinshi tareda Addah Nabilan Baffah Usman.....
Mamani tace “Yanda ka gani yaro am babu abinda ya sameni, kyan k’irane dani...”
Khalid ya d’an dara kana yace “Gaskiya Baaba na yarda kinada kyaun k’ira, ayi hak’uri dai ba tuk’in ganganci nake ba...”
Mamani data fahimci ya mata zubin masu kud’i tace “Ahtoh idan kunga talaka saman kwalta yanda kasan gwamnatin nakune ku kad’ai, yaro yanzu dubi maton da kake tuk’awa saikace ta gwamna da shugaban k’asa... Oh wasu iyayen dai Allah ya amshi addu’arsu sun haifi masu mulki da masu arziki...”
Jin zata saki layi yasa Basmah janyota tana fad’in “Mamani muje kar dare ya mana...”
“Ke da Allah cikani dacan ba guduna kike ba, saidai ki k’arasa tafiyarki amma nikam saina d’ana wannan maton mai kama data gwamna, yaro zoka bud’emin...”
Khalid na murmushi ya bud’e mata ya rik’e mata sandarta ya gyara mata yanda zataji dad’in zama, Basmah dai sai kallon ikon Allah take wato da ace bata gane Mutumin ba ahikenan idanma d’an yanke kai ne Mamani sabida tsabagen kwad’ayi da son abin duniyarta ta shige abinta, girgiza kai Basmah tai had’ida yin k’wafa ta shige ta rik’e Mamani kafin tai masa wani b’aranb’araman a motar, lokaci guda take tunanin yanda Nabilah zata d’au abin...
Khalid na tafe Dattijuwar na jansa da hira wanda akasarin hiran nata marassa kangado ne ko ba’ace maka ba kasan tsufa ke d’awainiya da ita..
Bai ida shan mamaki ba saida Basmah ta nuna masa gidan nasu... Ya dubesu yana mamaki zuciyarsa na masa fari k’al don idan har wannan Kakar Nabilah ce tabbas yasan zai samu wajen zama sosai ta wajenta...
Mamani sai yaba hankalinsa take yayinda Khalid yaji dad’in ci gaba da janta da fira... K’arahe dai har Basmah ta shige gida takaiwa iyayenta rahoton abindake faruwa, sukakaw yo gangami don ganema idanunsu dama tun kwanakin baya suke kad’a gurmi tsakaninsu cewa wani had’edd’en saurayi ke zuwa wajen Nabilah saidai babu wanda ya isa ya fito fili ya fasa gurmin sanin cewa wacece Nabilah...
Nan suka hangesu tafe sun nufi sahen Mamanin da Khalid d’in...
Nabilah kaw da dawowarta kenan daga makaranta ta sauk’a a adaidaita ta hangi motar Khalid k’ofar gidansu, mamaki ya isheta musamman data iso wajen taga alamun babu kowa cikin motar.. Gabanta na dukan tara tara ta nufi cikin gida....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*35*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Tinda ta shigo gida ta kasa zaune ta kasa tsaye, yanda take tunanin zataga Khalid bata ganshi ba, toh kodai ba motarsa bace... No she can’t be mistaken tabbas motarsa ce, toh ina yake...? Kodai aje motar kawai yai k’ofar gidansu...? Amma mai zai kawo motar tasa k’ofar gidan nasu...?
Ita kad’ai sai sak’e sak’e take, ta sak’a wannan ta warware wancan, Marliya dake zaune gaban socket tana gugan kaya hankalce take da ‘yar uwar tata, a ‘yan kwanakin sosai ta fahimci canzawa da Nabilah tai, wasu lokutan ko magana kake mata bata amsawa sai ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi, balle daren jiya yanda taji tana waya ta tabbata da wani take wayar...
Nabilah ta kuma mik’ewa zata fice a karo na kusan hud’u... Marliya ta katseta da fad’in “Wai ina kike zuwa ne... Lafiya kuwa...?”
D’an dubanta Nabilah tai a yatsine kana tace “Toh uwar sa ido kitchen zani wajen Mamy, koda magana ne... Uwata...?”
K’unshe dariyarta Marliya tai kana tace “A’a Allah baki hak’uri...”
Nabilah tai gajeren tsuka kana ta fice... Saida ta kuma sad’ad’awa ta lek’a sashen Abbah kaman wata munafuka kafin ta dawo kitchen ta tadda Mamy tuni ta ida abincin dare ta zuzzuba...
Gaisar da Mamy ta somayi tana tayata jere abincin....
Mamy da tun ganin Sameer take fama da tinane tinane sama sama ta amsa Nabilar kana ta umarceta ta d’au abincin Mamani takai, Nabilah a duniyarta ta tsani a aiketa sashen Mamani, gaisuwa ma don dole ke kaita tasan saura sarai idan ta tsallake kwana guda bataje ta gaidata ba d’aid’aya Mamy zata mata...
Babu halin ta doje taje ga Marliya a parlor na zaune bataga fuskan hakan ba balle ma ko a mafarki bata isa ta fad’iwa mahaifiyar tata haka ba...
D’aukan abincin tai ta fice yanda taci karo da Marliya a hanya ta ida gugan zata nufo kitchen wajen Mamy kafin Mamy tai mata tatas daga ita har gugan nata tace wasanta ta zaunayi tana ganinta a kitchen donma itace ba Nabilah ba datasaba shan mitan Mamy wanda gwara ai maka duka a cewar Nabilah...
Tareta Nabilah tai da fad’in “Ke Leeya wai bakiga bak’o ya shigo gidan nan ba....?”
Marliya ta dubeta da mamaki kana ta girgiza kai tace bak’o kuma...?”
Nabilah ta jinjina kai tace “Eh mana Abbah baiyi bak’o ba...?”
Marliya ta d’anyi shiru tamkar mai tunani kana ta girgiza kai tace “Gaskiya ni banga wani bak’o ba hasalima Abbah bai dawo ba ko kinga motarsa a gareji ne...?”
Nabilah ta d’an tab’e baki tace “Yo ina na lura, kinga zo kishige kafin Mamy ta lek’o...”
Aiko bata kai aya ba Mamyn ta lek’o tana fad’in “Wai ba aikanki akai ba Nabilah... Ke kuma kin tsaya biyeta naki aikan na jiranki.... Tsayuwar mai kuke ne..?”
Ko wacce tai hanyarta suna baiwa Mamy hak’uri, Marliya ta rab’a ta gefenta ta shige tana tunanin yau d’ain kaman wani abin na damun Mamy...
Tana tafe tana tunanin mai ya kawo motarsa k’ofar gidansu, kaman daga sama ta hangesa da Mamani biyedashi da alama ya fito tafiya ne...
K’iris ya rage Nabilah bata kifar da abincin ba, wannan wane irin mutum ne... Yau Abbanta gobe Kakarta... Shin miye tsakanin Khalid da mutanen gidan....
K’irjinta yaci gaba da wani irin bugu.... Tai saurin sa kai zata juya saidai tuni Khalid ya hangota...
Bud’e murya yai kafin ta fice a k’ofar Mamanin yace “Aah k’araso mana aima tafiya zanyi....”
Maganar da yayi ya sanya Mamani dake faman masa zuba kai dubanta ga k’ofar...
Nabilah ta tsaya cak ta kasa ci gaba da tafiya, tamkar ta zunduma a guje haka taji gashi ta kasa juyowa...
Mamani kaw ganin yarinyar da ake magana da ita tak’i juyowa ya sanyata yab’e baki tace “Ke wacece tsaye wajen nan ko bakijin magana ne...?” Nan ma Nabilah bata juyo ba sai rintse idanunta da tai da k’arfin gaske...
Mamani ta nufeta cikin dogara sandarta tana fad’in “Ai wato ina fad’a maka Haladu sam yaran gidan nan basajin magana, gado sukai wajen iyayensu mata...”
Jin zata saki layi ya sanya Nabilah saurin juyowa tana aika mata mugun kallo baki a cune, fuska babu alamun walwala tace “Aini aika na kawo kuma bansan kinada bak’o ba...” Tasa kai abinta zata shige d’akin dukda cewa Khalid tsaye yake wajen, da k’yar ta wuce gabansa musamman data tuna ko mayafi babu jikinta...
Mamani ta dawo da baya tana fad’in “Kaga rashin kunyar tasu koh... Toh wannan ina fad’i maka itace babbarsu a rashin ta ido, batada kunya ina fad’a maka babban abin takaicinma wai sunana gareta...”
Khalid kaw banda murmushi yana satan kallon Nabilah data had’e gabas da yamma baya komai, Mamani tace dashi shigo ai kaci abinci, baka bar gidan nan ba sai kaci abinci Yaron arziki Haladu....”
Wato har cikin ransa yakejin banbarak’wai d’in nan idan ta kirasa Haladu shi bai tab’a sanin mai suna Khalid ake fad’iwa hakan ba sai a baki Mamani...
Ya d’an shafi kansa kad’an yace “Baaba ba Haladu ba Khalid sunan...”
Mamani ta dubesa tsegege kana tace “Kajimin dai, wayace maka ba sunan kenan ba, ai asalin sunan kenan Haladu mu haka muka sani, kuma ka kirani Mamani don haka kowa ke kirana kaji koh shige muje...” Ta k’arashe tana turo shi ciki ta dawo dashi parlorn, sosai sukaso baiwa Nabilah dariya ganin draman Khalid kesha shida Mamani...
Batabi takansu ba ta mik’e zata fice Khalid ya bita da kallo yanda tai tamkar bata tab’a saninsa ba ko gaisuwar fatar baki bata masa ba...
Mamani ta tsareta da fad’in “Ke ke dakata shige ki kawo masa faranti da cokali yaci abinci... Kuma ki kawo na ‘yan gayu don kin gansa sarai d’an gaye ne...”
Nabilah ta dubeta a kufule kana takai dubanta ga Khalid wanda fuskarsa kega wayar salulansa, tana jira taji yace bazaici ba ta sami excuse d’in tafiya amma da yake d’an duniya ne shiru yai alamun zaicin kenan...
Mamani ta katseta da fad’in “Zaki wuce ne kokuwa....?”
K’wafa tai a hankali kana tasa kai ta shige kitchen d’in Mamanin da ba girki ake ciki ba kawai dai kayan amfani ne ciki...
Plate da spoon ta d’auko ta d’auraye had’ida serving spoon ta ijiye saman tray ta dawo fuska a d’aure ta dangwala kusada k’afafunsa....
“Kaga rashin hankalin nata koh, toh k’one masa k’afafu su zama bak’ak’e tinda naki bak’i ne....”
Nabilah datazo wuya hak’urinta ya gaza tace “Aidai wajenki na samo bak’in k’afar tinda na Mamy na fari ne tass....” Tai maganar tana murgud’a baki....
“Kaji koh.. Kaji rashin kunyar tata, ai Manu ya rasa d’ah tinda ya Ma’aruf sauran kam duk gayyan yuyuyu ne... Zuba mashi abincin...” Ta k’arashe tana gwagwiyan goro lokaci guda ta mik’e ta nufi d’aki kaman mai neman wani abin...