Sashe 96
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Murmushi kwance saman fuskar Akram yace “Ka wuce haka a wajena your Excellency, ban biyaka rabin abubuwan da kake min ba dama family na gaba d’aya, you made me who I am... Bama ni kad’ai ba d’imbin mutanen da suka zama abinda suka zama yau ta dalilinka bazasu k’irgu ba, Allah ne kawai zai biyaka, muna kuma fatan Allah ya k’ara mana irinku cikin al’umma....”
Daidai nan Muhibbah ta shigo d’aukeda farantin fruits ta zuba gayu cikin riga da skirt English wears wanda suka zauna a jikinta sosai ga k’amshin turaren humra dake tashi a jikin nata wanda duk d’ah namijin data giftasa dole tsikar jikinsa ya tsargar masa....
Akram yai saurin mik’ewa kana ya risina yaceda ubagidan nasa “Sir ni zan wuce...”
Engr ya jinjina kai yace “Alright Akram, ka samu Sufi ya baka list d’in k’ungiyoyin masu neman taimakon nan sai asan abinda za’a fara taimaka masu dashi koh....”
Ya jinjina kai yana mai furta “Alright your Excellency right away...”
Ko kallon yanda Muhibbah take baiyi ba ya fice cikin sauri duka irin shu’umin kallon da take aika masa....
Akram na ficewa ta kuma matsowa jikin mijin nata tana mai fad’in “Excellency na ga fruits na kawo maka, nasan idan na biye naka bazakaci komai ba har sai ka jira yaran nan sun dawo daga islamiya....” Ta k’arashe tana mai d’auko yankakkiyar kankana da cokalin fork.....
Girgiza kai ya d’anyi had’ida kauda kai gefe kana yace “Shin wai wane irin kunnen k’ashi ne dake Muhibbah, sau nawa zance maki idan ina tare da bak’i a parlorn nan kar ki shigo, kin fito babu ko mayafi cikin wannan shiga kin wuce duk tarin ma’aikatan dake cikin gidan nan a haka kin nufo har parlorn nan... Kanki d’aya Muhibbah....”
Murmusawa tai jin Wai yau Engr ke damuwa da ita har haka, ashe dai har yanzu yana k’aunarta tinda gashi yana kishinta.... Aje plate d’in ta d’anyi kana tace “Toh Banda abinka Excellency na gani nai daga kai sai Akram ne ai...”
“Akram d’in muharammin ki ne shi...?” Ya jefo mata tambayar...
Gyara zama ta kumayi kana tace “Toh ai gani nai Akram ya riga ya zama d’an gida a gidan nan kuma ai.....”
Dakatar da ita yai ta hanyar d’aga mata hannu kana yace “That doesn’t justify your actions, kinyi kuskure karki sake nan gaba...”
A hankali cikin yanayi na shagwab’a da turo baki gaba tace “Bazan sake ba in sha Allah... kuma ai gani nayi yanzu baka wani kulawa dani a gidan nan dukda k’ok’arin da nake wajen ganin ka janye k’udirinka akaina, Ma’aruf dan Allah ka yafemin haka nan mu koma tamkar yanda muke da, I promise to be a good housewife kaji please.... Ko dai neman aure kake ban sani ba...?”
Statement d’inta na k’arshe ya sanyashi d’agowa yana d’an dubanta, sai kuma ta basa tausayi sakamakon hango k’walla tab idanunta da yayi, ya sani Muhibbah ta canza sosai akan yanda take da idan zai mata adalci ya kamata ya zamto mai yafiya a gareta tinda duk d’an Adam ajizine, daidai da yaransu yanzu takan d’an basu kula fiyeda yanda take balagazantar dasu a baya don har wani sabo ne da SHAK’UWA ya soma shiga tsakaninta da yaran wanda ko shakka babu yaji dad’in hakan.....
A hankali yasa hannu ya tallafota ya fad’o jikinsa, kaman jira take Aiko nan ta saki kuka mai tsuma zuciyar mai saurare... Ya shiga lallashinta yanda salon nasu ya soma canzawa, aiko nan ta sami damar janyo hankalin mijin nata har saida ta sami kulawa da soyayyarsa wanda ta jima bata sami irinsa ba.....
***
Mamani taci gaba da salallami tana duban Sameer
“Ikon Allah yanzu shi yaron nan Haladu ashe d’anuwan iyalinka ne...?”
Sameer ya jinjina kai yace “Su biyu ne wajen iyayensu Mamani...”
Mamani ta jinjina kai tace “Allah sarki Aiko Haladu yaron kirki ne, ni ai tuni munyi sabo dashi, lallai kaje gidan mutunci kayi aure Ubana, na tabbata matar taka ma mutuniyar arziki zata zama, yakamata yanzu kam ka kawo mana ita nan mu ganta mu saba, dama nayi magana da mahaifinka sashen gefena nan za’a gyara maka ku d’an zauna ko na k’ank’anin lokaci ne musan matar taka mu saba, Kaga ai yafi ta shigo cikin dangi a santa a saba da ita tinda Allah yayika D’an zuri’a....”
Murmushi Sameer ya sakar mata kana yace “Babu damuwa Mamani yanda duk kikace hakan za’ai....”
Mamani ta Washe baki cikeda jin dad’i kana tace “Yauwa Ubana Allah dai shi maka Albarka, kai naji dad’in yin na’am da hukuncina da kayi.... Allah ya shiga lamuranka....”
Sameer ya amsada Ameen Mamaninah ... Yai maganar yana d’an waige waige ganin baiji d’uriyar Raihanah ba... Kaman wacce ta kula yana neman wani abin tace “Akwai wani abin ne Ubana...?”
D’an girgiza kai yayi kana yace “Em nace ina Raihaan take ne ban ganta ba...?”
Mamani ta yab’e baki tace “Aw Raihanatu ai kuwa d’azu Marliya da Naja’atu suka shigo suka jajib’eta Wai sun tafi islamiya, babu yanda banyi ba ta bari jikin nata ya ida warkewa amma sai cemin tayi zata iya zuwa Wai hadda ya taru mata gwara taje ta rage....”
D’an girgiza kai yai yana mai mik’ewa tsaye yake fad’in “Ciwon nata da saura bai gama warkewa ba she might catch infection out there... Ina ne islamiya nasu....?” Yanda yai maganar sosai damuwa ya nuna a fuskarsa har saida Mamani ta fahimci damuwar da fuskar nasa ya nuna....
“Nan layin baya ne, masu jajayen kaya zaka gansu....”
Jinjina kai kurum Sameer yai kana ya nufi k’ofa yana fad’in “Sai na dawo Mamani.....”
“A dawo lafiya...” Ta fad’i tana mai bin bayansa da kallo yanda ya fice cikin sauri.....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*74*
Layin bayansu ya nufa kaman yanda Mamani ta sanar dashi islamiyansu Raihanah nan yake, Aiko nan ya hangi wani dogon gini yanda sautin karatu ke fitowa ko shakka nan ne makarantar sannan ga baburan malaman a pappake a waje... Lokaci guda Sameer ya nufi ginin, a gefe ya paka motarsa kana ya sauk’a ya nufi cikin makarantar, wasu malamai ya samu kusan su hud’u a k’ofar wani aji tamkar tattaunawa suke, Sameer ya k’arasa ya masu sallama, gaba d’aya suka amsa mashi suna mai basa hannu alamun masabaha....
Nan Sameer d’in ya sanar dasu abindake tafe dashi... Malam Isyaku d’aya daga cikin malaman yace “Amma kuwa Raihana yarinyace mai k’wazo idan dai har zata iya zama inaga babu laifi a barta taci gaba da zuwa makarantar sabida ko d’azu da zan shige ajinsu naji tana bada haddarta tiryan tiryan harma tafi wad’anda suke zuwa makarantar, irinsu datse masu karatun babu dad’i....”
D’an murmushi da gefen bakinsa Sameer yai kana yace “Wato Malam ba nak’i ta zauna bane, shi ciwo musamman k’una idan bai gama warkewa ba sam ba’a so ana shiga wajen da k’wayoyin cuta zasu iya shafan ciwon, ayi hak’uri a barta ta k’ara samun sauk’i sosai kafin ta dawo makarantar mai gaba d’aya...”
Su Malam Ayuba suka shiga jinjina kai suna fad’in “Wannan gaskiya ne, ai komai saida lafiya....”
Malam Isyaku da yaji hujjojin Sameer yafi nasa yana murmushi yake fad’in “Amma dai rankashidad’e kai d’in likitane... Don idan ba likita ba babu wanda zai tsaro wannan bayanai...”
Gaba d’aya d’an darawa sukai kafin Malam Ayuba ya mik’e yana fad’in bari a kirawota....
Sameer yai masa godiya yanda sauran Malaman sukaci gaba da tattaunawarsu....
Mamakine ya cika Raihanah jin cewa Yayanta ne yazo d’aukanta, hartasu Marliya da Najah suma mamakin ne ya kamasu, gaba d’aya ma sai suka rasa wane yayan nasu ne yazo d’aukan Raihanah tinda abu ne mai kaman wuya kaji wani nasu yazo makarantar a baya, ko PTA meeting ne saidai suga ana zuwama wasu amma banda su shiyasa sosai abin ya basu mamaki..
Daidai nan Muhibbah ta shigo d’aukeda farantin fruits ta zuba gayu cikin riga da skirt English wears wanda suka zauna a jikinta sosai ga k’amshin turaren humra dake tashi a jikin nata wanda duk d’ah namijin data giftasa dole tsikar jikinsa ya tsargar masa....
Akram yai saurin mik’ewa kana ya risina yaceda ubagidan nasa “Sir ni zan wuce...”
Engr ya jinjina kai yace “Alright Akram, ka samu Sufi ya baka list d’in k’ungiyoyin masu neman taimakon nan sai asan abinda za’a fara taimaka masu dashi koh....”
Ya jinjina kai yana mai furta “Alright your Excellency right away...”
Ko kallon yanda Muhibbah take baiyi ba ya fice cikin sauri duka irin shu’umin kallon da take aika masa....
Akram na ficewa ta kuma matsowa jikin mijin nata tana mai fad’in “Excellency na ga fruits na kawo maka, nasan idan na biye naka bazakaci komai ba har sai ka jira yaran nan sun dawo daga islamiya....” Ta k’arashe tana mai d’auko yankakkiyar kankana da cokalin fork.....
Girgiza kai ya d’anyi had’ida kauda kai gefe kana yace “Shin wai wane irin kunnen k’ashi ne dake Muhibbah, sau nawa zance maki idan ina tare da bak’i a parlorn nan kar ki shigo, kin fito babu ko mayafi cikin wannan shiga kin wuce duk tarin ma’aikatan dake cikin gidan nan a haka kin nufo har parlorn nan... Kanki d’aya Muhibbah....”
Murmusawa tai jin Wai yau Engr ke damuwa da ita har haka, ashe dai har yanzu yana k’aunarta tinda gashi yana kishinta.... Aje plate d’in ta d’anyi kana tace “Toh Banda abinka Excellency na gani nai daga kai sai Akram ne ai...”
“Akram d’in muharammin ki ne shi...?” Ya jefo mata tambayar...
Gyara zama ta kumayi kana tace “Toh ai gani nai Akram ya riga ya zama d’an gida a gidan nan kuma ai.....”
Dakatar da ita yai ta hanyar d’aga mata hannu kana yace “That doesn’t justify your actions, kinyi kuskure karki sake nan gaba...”
A hankali cikin yanayi na shagwab’a da turo baki gaba tace “Bazan sake ba in sha Allah... kuma ai gani nayi yanzu baka wani kulawa dani a gidan nan dukda k’ok’arin da nake wajen ganin ka janye k’udirinka akaina, Ma’aruf dan Allah ka yafemin haka nan mu koma tamkar yanda muke da, I promise to be a good housewife kaji please.... Ko dai neman aure kake ban sani ba...?”
Statement d’inta na k’arshe ya sanyashi d’agowa yana d’an dubanta, sai kuma ta basa tausayi sakamakon hango k’walla tab idanunta da yayi, ya sani Muhibbah ta canza sosai akan yanda take da idan zai mata adalci ya kamata ya zamto mai yafiya a gareta tinda duk d’an Adam ajizine, daidai da yaransu yanzu takan d’an basu kula fiyeda yanda take balagazantar dasu a baya don har wani sabo ne da SHAK’UWA ya soma shiga tsakaninta da yaran wanda ko shakka babu yaji dad’in hakan.....
A hankali yasa hannu ya tallafota ya fad’o jikinsa, kaman jira take Aiko nan ta saki kuka mai tsuma zuciyar mai saurare... Ya shiga lallashinta yanda salon nasu ya soma canzawa, aiko nan ta sami damar janyo hankalin mijin nata har saida ta sami kulawa da soyayyarsa wanda ta jima bata sami irinsa ba.....
***
Mamani taci gaba da salallami tana duban Sameer
“Ikon Allah yanzu shi yaron nan Haladu ashe d’anuwan iyalinka ne...?”
Sameer ya jinjina kai yace “Su biyu ne wajen iyayensu Mamani...”
Mamani ta jinjina kai tace “Allah sarki Aiko Haladu yaron kirki ne, ni ai tuni munyi sabo dashi, lallai kaje gidan mutunci kayi aure Ubana, na tabbata matar taka ma mutuniyar arziki zata zama, yakamata yanzu kam ka kawo mana ita nan mu ganta mu saba, dama nayi magana da mahaifinka sashen gefena nan za’a gyara maka ku d’an zauna ko na k’ank’anin lokaci ne musan matar taka mu saba, Kaga ai yafi ta shigo cikin dangi a santa a saba da ita tinda Allah yayika D’an zuri’a....”
Murmushi Sameer ya sakar mata kana yace “Babu damuwa Mamani yanda duk kikace hakan za’ai....”
Mamani ta Washe baki cikeda jin dad’i kana tace “Yauwa Ubana Allah dai shi maka Albarka, kai naji dad’in yin na’am da hukuncina da kayi.... Allah ya shiga lamuranka....”
Sameer ya amsada Ameen Mamaninah ... Yai maganar yana d’an waige waige ganin baiji d’uriyar Raihanah ba... Kaman wacce ta kula yana neman wani abin tace “Akwai wani abin ne Ubana...?”
D’an girgiza kai yayi kana yace “Em nace ina Raihaan take ne ban ganta ba...?”
Mamani ta yab’e baki tace “Aw Raihanatu ai kuwa d’azu Marliya da Naja’atu suka shigo suka jajib’eta Wai sun tafi islamiya, babu yanda banyi ba ta bari jikin nata ya ida warkewa amma sai cemin tayi zata iya zuwa Wai hadda ya taru mata gwara taje ta rage....”
D’an girgiza kai yai yana mai mik’ewa tsaye yake fad’in “Ciwon nata da saura bai gama warkewa ba she might catch infection out there... Ina ne islamiya nasu....?” Yanda yai maganar sosai damuwa ya nuna a fuskarsa har saida Mamani ta fahimci damuwar da fuskar nasa ya nuna....
“Nan layin baya ne, masu jajayen kaya zaka gansu....”
Jinjina kai kurum Sameer yai kana ya nufi k’ofa yana fad’in “Sai na dawo Mamani.....”
“A dawo lafiya...” Ta fad’i tana mai bin bayansa da kallo yanda ya fice cikin sauri.....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*74*
Layin bayansu ya nufa kaman yanda Mamani ta sanar dashi islamiyansu Raihanah nan yake, Aiko nan ya hangi wani dogon gini yanda sautin karatu ke fitowa ko shakka nan ne makarantar sannan ga baburan malaman a pappake a waje... Lokaci guda Sameer ya nufi ginin, a gefe ya paka motarsa kana ya sauk’a ya nufi cikin makarantar, wasu malamai ya samu kusan su hud’u a k’ofar wani aji tamkar tattaunawa suke, Sameer ya k’arasa ya masu sallama, gaba d’aya suka amsa mashi suna mai basa hannu alamun masabaha....
Nan Sameer d’in ya sanar dasu abindake tafe dashi... Malam Isyaku d’aya daga cikin malaman yace “Amma kuwa Raihana yarinyace mai k’wazo idan dai har zata iya zama inaga babu laifi a barta taci gaba da zuwa makarantar sabida ko d’azu da zan shige ajinsu naji tana bada haddarta tiryan tiryan harma tafi wad’anda suke zuwa makarantar, irinsu datse masu karatun babu dad’i....”
D’an murmushi da gefen bakinsa Sameer yai kana yace “Wato Malam ba nak’i ta zauna bane, shi ciwo musamman k’una idan bai gama warkewa ba sam ba’a so ana shiga wajen da k’wayoyin cuta zasu iya shafan ciwon, ayi hak’uri a barta ta k’ara samun sauk’i sosai kafin ta dawo makarantar mai gaba d’aya...”
Su Malam Ayuba suka shiga jinjina kai suna fad’in “Wannan gaskiya ne, ai komai saida lafiya....”
Malam Isyaku da yaji hujjojin Sameer yafi nasa yana murmushi yake fad’in “Amma dai rankashidad’e kai d’in likitane... Don idan ba likita ba babu wanda zai tsaro wannan bayanai...”
Gaba d’aya d’an darawa sukai kafin Malam Ayuba ya mik’e yana fad’in bari a kirawota....
Sameer yai masa godiya yanda sauran Malaman sukaci gaba da tattaunawarsu....
Mamakine ya cika Raihanah jin cewa Yayanta ne yazo d’aukanta, hartasu Marliya da Najah suma mamakin ne ya kamasu, gaba d’aya ma sai suka rasa wane yayan nasu ne yazo d’aukan Raihanah tinda abu ne mai kaman wuya kaji wani nasu yazo makarantar a baya, ko PTA meeting ne saidai suga ana zuwama wasu amma banda su shiyasa sosai abin ya basu mamaki..