Sashe 106
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ‘yan kwanaki biyun da Khalid yai dasu Aunty Daula kaman yanda yake kiran matar Baban nashi sosai suka saba, daga ita har yaran nata sosai Khalid yaji dad’in zama dasu suma kuma sunji dad’in zama dashi har saida Aunty Daula da yaranta suka buk’aci Khalid ya k’ara masu kwanaki, abu kaman wasa sai gashi har sun doshi sati, wani irin rayuwa mai dad’i da babu hayaniya ko tashin hankali cikinta yake experiencing, rayuwar da sam bai samu da mahaifiyarsa da ‘yaruwarsa ba wanda su a kullum son kansu suke ba kaman Aunty Daula da yaranta ba wanda soyayyan ‘yan uwa ya cika zukatansu.... Ji yayi ya sake sosai dasu har bayaso ya baro su, inama zasu had’u gaba d’aya harda Siyama da Ammi suyi irin wannan rayuwa mai ban sha’awa da tarin memories masu d’ad’in tunawa.... Da k’yar su Humaira da Ijlaal sukai sallama da Khalid saida Aunty Daula da Daddy sukaita fama dasu Khalid d’inma ya masu alk’awarin sake visiting d’insu soon sauk’in abin ma su Irfaan cousins d’insu sunzo sai suka d’ebe masu kewan Yayan nasu.... Wasa wasa satityikw sun shud’e, a ko wane b’angare shirye shirye suke gudanarwa, can Kano gidan Abbah shirye shiryen Bikin Sahariyya da Sameer suke dikda cewa a b’angaren ango ba haka take ba, gaba d’aya shi ya yama mance da wani shirin biki da ake yafi bada muhimmanci ga aikinsa Wanda yake ceton rayukan al’umma ne, har yau ko saka amaryar tasa a ido baiyi ba, kaman yanda ba hakan ta kasance ga b’angaren amaryar ba, dikda cewa bata ida warkewa sosai ba hakan bai hanata gudanar da shirye shiryenta ba, daga ita har Haule basu sama basu k’asa, dik wannan buduri da suke Najah dai kallonsu kawai take da matuk’ar sanyin jiki... Anya idan ta bari burin iyayenta na aurawa Ya Ma’aruf Addarta Sahariyya tayi daidai, Ta tina binda taji iyayen nata suna tattaunawa kwanaki a asibiti lokacin kwanciyar Hajiya, tagumi ta rafka tana neman mafita, fad’in gaskiya na daidai da tonuwar asirin iyayenta ne, Toh amma idan tai shiru kuma abin sai yafi muni, ta basu dama suci gaba da b’arna a doron k’asa ne... A hankali ta rintse idanunta tana rok’on Allah ya kawo mata mafita....
A b’angaren Akram ma yanzu kam sun sansanta sosai da Zulfa’u har yana maganan turo magabata dikda cewa itace mai d’an taka masa birki, ga Hafiz ma da har yanzu ya kasa ya tsare sai matarsa ta koma garesa yayinda a can b’angaren Daddy kuma a nan Kaduna ya k’udiri niyyan farantawa d’ansa Khalid koda hakan zai haifar da tashin hankali tsakaninsa da matarsa, duk yanda Siyama taso ta shawo kan Sameer su shirya abu ya gagara, Ammi da Laila kaw sosai suka sa azamar raba Sameer da Siyama rabuwa ta har abada, wannan ya baiwa Laila da Sultan daman cika burinsu (Idan baku mance ba Sultan abokin Sameer ne wanda suka taso a nan Kaduna tare kuma yake cin dunduniyarsa sabida wata manufa tasa)... Wasa wasa har takai Laila ta soma k’ulla wata dangantaka tsakanin Siyama da Sultan dikda cewa sun kwana da sanin tsakanin Sultan d’in da Sameer....
Yauma suna zaune a wani waje na shak’atawa su ukun, sai k’ok’arin cheering Siyama suke wacce gaba d’aya da ganinta kasan hankalinta bai jikinta, mik’ewa Sultan yai kana yace yana zuwa... Laila ta masa wani duba Kafin ya shige.... Dafa hannayenta dake zube saman table Laila tai kana tace “K’awata Wai meye ne haka, dan Allah ki saki ranki baki ganin we’re here to make you feel better, Sultan zaiji babu dad’i idan yaga duk efforts d’insa kina basarwa...”
Da mamaki Siyama ke duban Laila kana tace “Laila kin San abinda kike fad’i kuwa...? Nifa ban gane wannan kyautatawa da Sultan ke min ba bayan duk abinda nayima abokinsa... Ni bansan wayace ki gayyato mana shi ba ma....”
Murmushi Laila tai kana tace “Aw ke yanzu baki gane nufin Sultan akanki ba...? Toh idan baki gane ba ki bud’e idanunki sosai ki fahimcesa... Sultan is trying to give you what Sameer refuses to give you... Sultan zai iya maye gurbin Sameer a wajenki idan kin basa dama kuma ya baki duk wata kulawa da soyayya da Sameer ya kasa baki....”
Wannan karon tsaye Siyama ta mik’e cikin tsananin b’acin Rai take duban Lailar... Lokaci guda take furta “Kin faran shan k’waya ne Laila ban sani ba, da auren Sameer akaina kike cewa na baiwa wani chance waninma of all people abokinsa... you must be insane Laila...”
Kamo hannunta Laila tai ta zaunarta, saida ta gyara zama kafin taci gaba da fad’in “Haba Siyama ya kike neman ki badani, saikace wata ba wayeyyiba, ki dubeki son kowa kin wanda ya rasa, gaki kyakkyawa gaki da karatunki gaki d’iyar masu kud’i... Duk wad’annan qualities d’in kin had’a sannan ki bari wani namiji yake baki wahala, haba Siyama karfa ki mance ke kin juyawa mahaifiyarki baya a sabida shi sannan shi ya kasa defending d’inki gaban family d’insa, think about it Sameer ba sonki yake ba, da ace yana sonki da bai miki haka ba... Da duk wad’annan features d’in da kikeda ki tsaya namiji k’wara yana baki wahala, tell me meye Sameer yafi Sultan dashi, profession d’insu guda idanma kasancewarsa likita ne ya rufe miki idanu kika kasa gameda shi.. Saidai kuma idan kyaun hakittarsa ne ke rud’inki...”
Wani duba Siyama ta watsawa Laila kana tace “Laila sanin kanki ne ban tab’a son wani d’a namiji ba sai Sameer kinsan hakan tin muna high school, banjima kuma akwai wani d’ah namiji da zan mallaka masa gurbin da Sameer ya mallaka cikin zuciyata... I cannot...”
Tab’e baki Laila tai tana dubanta kafin ta mik’e a fusace tana fad’in “Toh gaskiya ni idan bazaki bud’e idanunki kiga abindake faruwa a gabanki ba zan barki da iyawarki, kiyita wulak’anta kanki kan wanda bai d’aukeki da wata daraja ba, Kinga tafiyata.!””” Daga haka Laila tasa hannu ta d’auki jakarta ta wuce fuuu tamkar mai shirin tashi sama... Siyama ta bita da kallo tana kiran sunanta inaa Laila ko juyowa batai ba... Daidai nan Sultan ya k’araso hannunsa rik’eda cup d’in ice cream guda biyu.... Murmushi ya sakar mata kana yace “Ina k’awar taki..?”
Murmushin yak’e Siyamar tai kana tace “Ta ta wuce I guess....”
Sultan ya zauna yana mai aje mata kofin ice cream guda yake fad’in “Too bad gashi na kawo maku ice cream din nan da nake baku labari duk garin nan babu mai dad’insa kuyi tasting da kanku kuji...” Yayi maganar da siga ta barkwanci...
Tak’aitaccen dariya Siyamar ma tai...
Daga yanda Laila ke tsaye shu’umin murmushi tai kana ta ciro wayarta cikin jaka ta shiga kashe masu hotuna lokaci guda take furta “Saini Laila amaryar Sameer... Bani sa abu a gaba naga kasawa, na sami shaidu k’warara da zanyi amfani dasu wajen datse aurenki da Sameer, na farko shaidar zubar masa da ciki da kikayi na biyu cin amanansa da abokinsa...” Ta kuma tintsirewa da dariya had’ida jefa wayarta cikin jaka kana ta bar wajen....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*78*
Gaba d’aya Hajiya Haule da Baba Alhaji sun hura wuta sosai kan maganar auren Sameer da Sahariyya, babu yanda Abbah baiyi ba su d’an k’ara lokaci amma inaa sun azalzala ayi ayi auren, ko Sahariyyar dake matuk’ar d’aukin auren bata rawar k’afar da iyayenta keyi gashi har rana mai kaman ta yau basuga idon ango ba, Hajiya Haule ta tasa Baba Alhaji gaba da cewa yaje ya sami k’aninsa da batun, don gaba d’aya basu san wanne Sameer ke ciki ba....
Hafiz dake gefe ya cika yayi fam sai hura hanci yake yana aikama iyayen nasa kallon wulak’anci....
Hajiya takai dubansa garesa yanda ya cika yai fam kana tace “Kai kuma fah....?”
K’wafa yai a hankali “Amma Hajiya gaskiya ni baku kyauta min, nayi abinda Baba Alhaji keso na maida tsinanniyar can d’akinta maiyasa ni baza’a cika min nawa burinba, maiyasa za’a min alk’awarin dawo min da matata kuma ak’i cikawa... Idan duniya da gaskiya idan ba wani al’amarin kuke b’oyewa gameda aurawa Sameer Sahariyya ba ai nima sai ku hura wuta a had’a auren da nawa...”
Hajiya ta tab’e baki kad’an tana duban Baba Alhaji kana tace “A’ah toh, ai ga Baban naka... Babu yanda banyi ba yayi maganar dawoda Zulfa’u amma yayi k’ememe yayi banza dani, bansan wata kalar muguwar asiri Magajiya da d’iyarta suka hura masa ba... Gashi nan tambayesa kaji daga bakinsa....”
Baba Alhaji dake muzurai cikeda fad’a ya soma fad’in “Ni ba wai nak’i Zulfa’u ta koma gidan Hafiz bane, ince shika uku ya mata, a ina kuka tab’a jin anyi shika uku an gyara aure... Kuma banda abinka me ita wannan yarinya Sawwama ta rageka dashi...”
Baikai aya ba Hafiz ya mik’e cikin hura hanci da d’aga kafad’u sama yake fad’in “Nifah Baba Alhaji saki d’aya tak naiwa matata don haka babu wanda ya isa yace bazan iya maidata ba, kuma idan bazaka sa baki ba a had’a aurenmu da Sahariyya wllhi wllhi kaji na maka rantsuwa zan tono ko mene shirinku kuma zan fallasaku a bainar jama’a, sannan bayan haka zan rabuda Sawwama ta hanyar da bakai zato ba...” Ya k’arashe tamkar zaikaiwa mahaifin nasa bugu, sai faman hura hanci da d’aga kafad’a da wuya yake....
Hajiya da ‘yan hanjinta suka kad’a don tasan tsaf Hafiz zai aika abinda yace, idan yaso tsaf zai binciko sirrinsu, murmusawa tai kana tace “Sha kuruminka d’ah na idan dai Zulfa’u ce ta koma gidanka an gama babu shegen da ya isa ya datse aurenku, ince nice nan sanadin rabuwarku, toh ka kwantar da hankalinka aurenku ya koma an gama... Ka kwantar da hankalinka kaji d’ah na Zulfa’u ta dawo gareka an gama...”
A b’angaren Akram ma yanzu kam sun sansanta sosai da Zulfa’u har yana maganan turo magabata dikda cewa itace mai d’an taka masa birki, ga Hafiz ma da har yanzu ya kasa ya tsare sai matarsa ta koma garesa yayinda a can b’angaren Daddy kuma a nan Kaduna ya k’udiri niyyan farantawa d’ansa Khalid koda hakan zai haifar da tashin hankali tsakaninsa da matarsa, duk yanda Siyama taso ta shawo kan Sameer su shirya abu ya gagara, Ammi da Laila kaw sosai suka sa azamar raba Sameer da Siyama rabuwa ta har abada, wannan ya baiwa Laila da Sultan daman cika burinsu (Idan baku mance ba Sultan abokin Sameer ne wanda suka taso a nan Kaduna tare kuma yake cin dunduniyarsa sabida wata manufa tasa)... Wasa wasa har takai Laila ta soma k’ulla wata dangantaka tsakanin Siyama da Sultan dikda cewa sun kwana da sanin tsakanin Sultan d’in da Sameer....
Yauma suna zaune a wani waje na shak’atawa su ukun, sai k’ok’arin cheering Siyama suke wacce gaba d’aya da ganinta kasan hankalinta bai jikinta, mik’ewa Sultan yai kana yace yana zuwa... Laila ta masa wani duba Kafin ya shige.... Dafa hannayenta dake zube saman table Laila tai kana tace “K’awata Wai meye ne haka, dan Allah ki saki ranki baki ganin we’re here to make you feel better, Sultan zaiji babu dad’i idan yaga duk efforts d’insa kina basarwa...”
Da mamaki Siyama ke duban Laila kana tace “Laila kin San abinda kike fad’i kuwa...? Nifa ban gane wannan kyautatawa da Sultan ke min ba bayan duk abinda nayima abokinsa... Ni bansan wayace ki gayyato mana shi ba ma....”
Murmushi Laila tai kana tace “Aw ke yanzu baki gane nufin Sultan akanki ba...? Toh idan baki gane ba ki bud’e idanunki sosai ki fahimcesa... Sultan is trying to give you what Sameer refuses to give you... Sultan zai iya maye gurbin Sameer a wajenki idan kin basa dama kuma ya baki duk wata kulawa da soyayya da Sameer ya kasa baki....”
Wannan karon tsaye Siyama ta mik’e cikin tsananin b’acin Rai take duban Lailar... Lokaci guda take furta “Kin faran shan k’waya ne Laila ban sani ba, da auren Sameer akaina kike cewa na baiwa wani chance waninma of all people abokinsa... you must be insane Laila...”
Kamo hannunta Laila tai ta zaunarta, saida ta gyara zama kafin taci gaba da fad’in “Haba Siyama ya kike neman ki badani, saikace wata ba wayeyyiba, ki dubeki son kowa kin wanda ya rasa, gaki kyakkyawa gaki da karatunki gaki d’iyar masu kud’i... Duk wad’annan qualities d’in kin had’a sannan ki bari wani namiji yake baki wahala, haba Siyama karfa ki mance ke kin juyawa mahaifiyarki baya a sabida shi sannan shi ya kasa defending d’inki gaban family d’insa, think about it Sameer ba sonki yake ba, da ace yana sonki da bai miki haka ba... Da duk wad’annan features d’in da kikeda ki tsaya namiji k’wara yana baki wahala, tell me meye Sameer yafi Sultan dashi, profession d’insu guda idanma kasancewarsa likita ne ya rufe miki idanu kika kasa gameda shi.. Saidai kuma idan kyaun hakittarsa ne ke rud’inki...”
Wani duba Siyama ta watsawa Laila kana tace “Laila sanin kanki ne ban tab’a son wani d’a namiji ba sai Sameer kinsan hakan tin muna high school, banjima kuma akwai wani d’ah namiji da zan mallaka masa gurbin da Sameer ya mallaka cikin zuciyata... I cannot...”
Tab’e baki Laila tai tana dubanta kafin ta mik’e a fusace tana fad’in “Toh gaskiya ni idan bazaki bud’e idanunki kiga abindake faruwa a gabanki ba zan barki da iyawarki, kiyita wulak’anta kanki kan wanda bai d’aukeki da wata daraja ba, Kinga tafiyata.!””” Daga haka Laila tasa hannu ta d’auki jakarta ta wuce fuuu tamkar mai shirin tashi sama... Siyama ta bita da kallo tana kiran sunanta inaa Laila ko juyowa batai ba... Daidai nan Sultan ya k’araso hannunsa rik’eda cup d’in ice cream guda biyu.... Murmushi ya sakar mata kana yace “Ina k’awar taki..?”
Murmushin yak’e Siyamar tai kana tace “Ta ta wuce I guess....”
Sultan ya zauna yana mai aje mata kofin ice cream guda yake fad’in “Too bad gashi na kawo maku ice cream din nan da nake baku labari duk garin nan babu mai dad’insa kuyi tasting da kanku kuji...” Yayi maganar da siga ta barkwanci...
Tak’aitaccen dariya Siyamar ma tai...
Daga yanda Laila ke tsaye shu’umin murmushi tai kana ta ciro wayarta cikin jaka ta shiga kashe masu hotuna lokaci guda take furta “Saini Laila amaryar Sameer... Bani sa abu a gaba naga kasawa, na sami shaidu k’warara da zanyi amfani dasu wajen datse aurenki da Sameer, na farko shaidar zubar masa da ciki da kikayi na biyu cin amanansa da abokinsa...” Ta kuma tintsirewa da dariya had’ida jefa wayarta cikin jaka kana ta bar wajen....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*78*
Gaba d’aya Hajiya Haule da Baba Alhaji sun hura wuta sosai kan maganar auren Sameer da Sahariyya, babu yanda Abbah baiyi ba su d’an k’ara lokaci amma inaa sun azalzala ayi ayi auren, ko Sahariyyar dake matuk’ar d’aukin auren bata rawar k’afar da iyayenta keyi gashi har rana mai kaman ta yau basuga idon ango ba, Hajiya Haule ta tasa Baba Alhaji gaba da cewa yaje ya sami k’aninsa da batun, don gaba d’aya basu san wanne Sameer ke ciki ba....
Hafiz dake gefe ya cika yayi fam sai hura hanci yake yana aikama iyayen nasa kallon wulak’anci....
Hajiya takai dubansa garesa yanda ya cika yai fam kana tace “Kai kuma fah....?”
K’wafa yai a hankali “Amma Hajiya gaskiya ni baku kyauta min, nayi abinda Baba Alhaji keso na maida tsinanniyar can d’akinta maiyasa ni baza’a cika min nawa burinba, maiyasa za’a min alk’awarin dawo min da matata kuma ak’i cikawa... Idan duniya da gaskiya idan ba wani al’amarin kuke b’oyewa gameda aurawa Sameer Sahariyya ba ai nima sai ku hura wuta a had’a auren da nawa...”
Hajiya ta tab’e baki kad’an tana duban Baba Alhaji kana tace “A’ah toh, ai ga Baban naka... Babu yanda banyi ba yayi maganar dawoda Zulfa’u amma yayi k’ememe yayi banza dani, bansan wata kalar muguwar asiri Magajiya da d’iyarta suka hura masa ba... Gashi nan tambayesa kaji daga bakinsa....”
Baba Alhaji dake muzurai cikeda fad’a ya soma fad’in “Ni ba wai nak’i Zulfa’u ta koma gidan Hafiz bane, ince shika uku ya mata, a ina kuka tab’a jin anyi shika uku an gyara aure... Kuma banda abinka me ita wannan yarinya Sawwama ta rageka dashi...”
Baikai aya ba Hafiz ya mik’e cikin hura hanci da d’aga kafad’u sama yake fad’in “Nifah Baba Alhaji saki d’aya tak naiwa matata don haka babu wanda ya isa yace bazan iya maidata ba, kuma idan bazaka sa baki ba a had’a aurenmu da Sahariyya wllhi wllhi kaji na maka rantsuwa zan tono ko mene shirinku kuma zan fallasaku a bainar jama’a, sannan bayan haka zan rabuda Sawwama ta hanyar da bakai zato ba...” Ya k’arashe tamkar zaikaiwa mahaifin nasa bugu, sai faman hura hanci da d’aga kafad’a da wuya yake....
Hajiya da ‘yan hanjinta suka kad’a don tasan tsaf Hafiz zai aika abinda yace, idan yaso tsaf zai binciko sirrinsu, murmusawa tai kana tace “Sha kuruminka d’ah na idan dai Zulfa’u ce ta koma gidanka an gama babu shegen da ya isa ya datse aurenku, ince nice nan sanadin rabuwarku, toh ka kwantar da hankalinka aurenku ya koma an gama... Ka kwantar da hankalinka kaji d’ah na Zulfa’u ta dawo gareka an gama...”