Sashe 109
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Yaya ina zakaje kuma bacin ko gaisawa bamuyi ba...” Tai maganar tamkar mai shirin kuka...
Cak ya tsaya ba tareda ya juyo ya dubeta ba, ganin yaja ya tsaya yasa Sahariyya ci gaba da fad’in “Kaga fah ko ruwan da aka kawo maka baka sha ba, dan Allah ka tsaya ko ruwan ka d’an sha...” Tai saurin k’arasawa ta shiga k’ok’arin bud’e drinks d’in tana zubawa a cup...
Yanda tai maganar cikeda girmamawa ya hana Sameer gwaleta, karkatowa yai kad’an yana duban yanda take serving drink d’in har rawa jikinta keyi.... Ta d’ago kai sukai ido hud’u nan taga dai har lokacin fuskarsa tamau, ta maida kanta k’asa tana mai furta “Ina yini...”
Saida ya kwashe wasu sakanni kaman mai nazarin wani abin sai kuma yace “Lafiya..” A tak’aice...
“Yaya ka zauna dan Allah...” Ta fad’i cikin kashe murya, wani duban ya mata ya sanyata had’iye sauran kalaman nata, duk duniya Sahariyya bata tab’a cin karo da wanda takejin bala’in shakkarsa kaman Sameer ba, ikon Allah wai ita Sahariyya kejin shakku da tsoro had’ida fargaban wani bil’adam kaman haka, a iyakacin saninta tsabagen k’aurin suna da tai na rashin kunya da rashin mutunci yasa duk saurayin da yazo wajenta idan halinta bai koresa ba toh kuwa jama’an unguwa sai sun koresa, amma yau ita ke jin azabebben fad’uwan gaba da tsananin shakkun wani mutum haka... Ta had’i miyau da k’yar, har lokacin tana nan duk’a gabansa dikda cewa k’afar tata bai ida warkewa ba amma ko zafin tsugunon da tai bataji....
Sameer ya d’an gyara tsayuwarsa kad’an yana karantarta kana yace “Yaya jikin naki...?”
Nan fah Sahariyya taji maganar tasa tamkar wacce aka jefota, dad’i ya cika zuciyarta ashe har ya damu da ita haka.... Cikeda jin dad’i ta amsa masa da cewa “Da sauk’i Yaya aima saura kad’an ne, gobe muke komawa wajen mai d’aurin dama...”
Jinjina kansa yai har lokacin tsaye gabanta yake hannayensa dafe da kunkumimnsa, saida ya d’an gyara tsayuwarsa kana yace “Menene asalin abinda ya sameki, me ya janyo faruwar ciwon...?”
D’agowa tai tana dubansa wani irin dad’i na mamaye illahirin zuciyarta, a hankali ta furta “K’addara ce Yaya...”
Sameer ya jinjina kai kana ya maimaita “K’addara... Kin yarda da k’addara...?”
Wannan karon a d’an zabure ta d’ago tana dubansa, lokaci guda ta saki murmushi wanda yafi kamada yak’e kana tace “Na yarda da k’addara Yaya...”
“Good..” Ya furta a hankali yana mai jinjina kai yayinda Sahariyya ta shagala sosai da annashuwa, sinkayo muryarsa tai yana fad’in “Idan kin yarda da k’addara kaman yanda kika fad’i maiyasa kika biyewa mahaifiyarki kuke aibanta k’anwarki Raihaan don kawai bata kasance d’iyaga mahaifiyarki ba..?”
Wannan karon azabebben fad’uwan gaba taji ya sauk’a mata, ta tuna farin zuwansa gidan tun Kafin susan cewa shine Ma’aruf, nan fah Sahariyya ta shiga muzurai tana neman abin fad’i lokaci guda ta soma kame kame da inda inda... Sameer ya girgiza kai a hankali yana mai aika mata wani kallo lokaci guda ya sakale hannayensa cikin aljihun wandonsa kana yaci gaba da fad’in “Wacce kika k’ona da ganganci itace ta yarda da k’addara amma bake ba, nasan kinsan wa nake nufi.... Anyways Allah ya baki lafiya, ni zan wuce suna kirana a asibiti.... Idan Baba Alhaji yazo sai ki fad’a mishi nazo ban sameshi ba....” Daga haka bai jira cewarta ba yasa kai ya fice...
Sahariyya dake dab’e wajen tamkar wacce aka dasa kasa motsa koda d’an yatsarta tai, dik a tunaninta Sameer damuwarsa akanta yake nuna mata ashe ba haka bane, magana yaso yab’a mata kuma ba akan kowa ba sai kan shegiyar k’anwar nan nata... Wani irin zogi da rad’ad’i taji zuciyarta na mata, idanunta suka kad’a sukai jazir hawayen da basu shirya fitowa ba suka shiga zarya a kumatunta, wani irin tsanar Raihanah takeji kaman ta shak’eta ta mutu, fuskar Raihanah take hangowa tana mai furtawa a fili “Na tsaneki na tsaneki shegiya stinanniya munafuka algunguma mayya..!” Idanunta na zuban hawaye masu rad’ad’i take maganar cikin tsananin karaji...
A haka Haule ta shigo ta taddata, ganinta a duk’e tana hawaye ya sanya Haule k’arasawa da sauri ta shiga jijjigata tana fad’in “Ke Sahariyya... Lafiya... Meke faruwa.. Ina Ma’aruf d’in....?”
Sahariyya na hawaye take fad’in “Hajiya dik laifin munafukar Raihanar nan ne, annamimiya mai halin munafukan farko, nunawa take itace mutumiyar arziki keda ‘ya’yanki faragurbi... Munafuka wayasan kalan salon munafuncin da take masa can gidan Mamanin... Ni wllhi Hajiya kisa Baba Alhaji ya dawo da ita gida, Allah kad’ai yasan mai take masa acan mai shegen son mazan bala’i....” Ta k’arashe tana goge hawayen da suka wanke mata fuska...
Murmusawa kad’an Haule tai kana tace “Banda abinki mai Ma’aruf zai da wannan banzar yarinyar tausayice kawai take basa, kinsan shi ya mata aiki lokacinda ta k’one kuma Allah yayisa mai tausayi da tausasawa bacin haka ke ko a hanya yayi kama da wanda zai tarayya da Raihanah ne ai Ma’aruf saike naki ne, domin kaw an gama magana ki kwantar da hankalinki yanzu zan kira mahaifiyarsa mujin batun lefe a ina anka tsaya... Karma wannan ya tada miki hankali, ci gaba da shirye shiryenki, ki kirawo Fa’iza yau kuje ku cire ankonku muma ku ciro mana ankon gida iyanin....”
Kalaman Hajiya ya d’an tausasa zuciyar Sahariyya, ta saki murmushi tana mai furta “Shisa nake sonki Hajiyata...” Hajiya ta rungumeta tana fad’in “Aikinfi min wancan shashashar k’anwar taki wacce bata k’aunar uwarta....” Ta k’arashe tana aikama Naja’atu dake tattara wajen hrara... Giriza kai kurum Najah tai ba tareda cewa komai ba ta fice da parantin dake hannunta....
***
Kasancewar washe gari baida zuwa asibiti da wuri ya sanyashi yada zango gidansu abokinsa Shamsu don sun kwana biyu basu had’u ba, Shamsun ma wata k’aramar kwangila ya samu nan cikin gari da wata company shisa shima d’in bai zauna ba kwana biyun.... A parlor Sameer ya samu Mama suka gaisa tana masa tsiyan shida abokinsa aiki duk ya b’oyesu gwarama shi nada iyali amma abokin nasa bai ije kowa ba sai bautan neman kud’i....
Sameer ya d’an sosa k’eyarsa yana mai furta “Zai aje ne Mama....” Yai maganar yana duban k’ofa yanda Shamsu ke k’arasowa cikin parlorn hannunsa rik’eda mug alamun bai jima da tashi ba...
Mama ta dubi Shamsun baki a tab’e kana tace “Allah yasa yaji gori ya aje d’in, mutum gansameme kullum saidai ya tashi ya ishi mutane da tsifface tsiffacen baison cin wannan da safe baison cin wancan, idan kaji gori kai aure muma ma huta da wannan tsirin naka... K’aton kawai...” Ta k’arashe tana yab’a masa muguwar kallo...
Sameer kaw sai sakin murmushi yake yana duban yanda abonkin nasa ya had’e gira sosai....
“Mama fah safiyar da saura dan Allah a k’yaleni haka nan, kofa karin kumallo banyi ba...”
“Tafi can ka rufewa mutane baki, Kaga Sameer ka d’auki hotonsa ka raba a masallatai ko Allah zaisa a dace...”
“Mama neman kai kike dani...?” Shamsu yace yana mai mik’awa Sameer hannu domin yin masabaha...
Mama tace “Ahtoh naga abin naka bana k’are bane ai....”
Sameer dake danne dariyarsa yace “Yanda kikace hakan za’ai Mama...”
“Toh ai ba masallaci ya kamata kukai ba makarantar ‘yanmata ya kamata kukai tallan nawa...” Shamsu yace yana mai zama gefen Sameer...
D’an darawa sukai gaba d’aya kana Mama ta mik’e tana tambayan Sameer mai za’a kawo masa...
Cikeda ladabi yace “A’a Mama nikam a k’oshe nake na gode....”
Mama tace “Aiko dai kaji mai Iyali, wanine dai sai anyita fama dashi....”
Shamsu ya tari zancen nata da fad’in “Nima ruwan tea d’in nan kawai ya isheni Mamana...”
“Kadaiji dashi..” Mama tace sanda take bari masu parlorn...
D’an shaking hannu suka kumayi suna dariyar draman Mama kana Shamsu yace “Doc,ya akai ne... Kwana biyu ko k’yallinka ba’a gani, ko zumud’in angoncin ne ya soma b’oyeka....” Yai maganar cikeda zolaya...
Gajeren tsaki Sameer yai had’ida b’alla masa harara kana yace “Aure ko damuwa....”
Shamsu ya d’an dara kad’an “Yaushe aure ya koma damuwa, ince gashi kaida Mama kun hanani sakat.... Ni gwarama da kazo coz dama inatason mu had’u naji what are your plans...”
Fuzar da iska Sameer yai a hankali had’ida fitowa daga cikin kujeran kad’an, saida ya shafi fuskarsa da tafukan hannayensa kana yace “Wannan kuma saidai ka tambayisu Abbah don ni kaina ban sani ba....”
Dariya mai bayyana hak’wara Shamsu keyi yana mai furta “Sameer kenan, gaba d’aya sai ka juye min Sameer d’in dana sani sanda muke sch kafin ka auri Partner....”
Nanma dai d’an duban nasa kawai Sameer yai wannan karon harda tab’e baki kad’an “Kaidai baka tab’a d’aukan abu serious, na kawo maka matsalata kana dariya...”
“Toh kuka kakeso nayi.., Kai ba d’an gata bane, su Mummy Sun aura maka Siyama yanzu gashi su Abbah zasu aura maka Sahariyya... Ni amin Auren mana idan inada gatan....” Har yanzu dai dariyar bata bar saman fuskar Shamsu ba....
Mik’ewa tsaye Sameer yai yana zira hannaye cikin aljihu...
Shamsu dake sipping tea ya d’ago yana dubansa kana yace “Ina kuma zakaje naga dai shigowarka kenan...”
Cak ya tsaya ba tareda ya juyo ya dubeta ba, ganin yaja ya tsaya yasa Sahariyya ci gaba da fad’in “Kaga fah ko ruwan da aka kawo maka baka sha ba, dan Allah ka tsaya ko ruwan ka d’an sha...” Tai saurin k’arasawa ta shiga k’ok’arin bud’e drinks d’in tana zubawa a cup...
Yanda tai maganar cikeda girmamawa ya hana Sameer gwaleta, karkatowa yai kad’an yana duban yanda take serving drink d’in har rawa jikinta keyi.... Ta d’ago kai sukai ido hud’u nan taga dai har lokacin fuskarsa tamau, ta maida kanta k’asa tana mai furta “Ina yini...”
Saida ya kwashe wasu sakanni kaman mai nazarin wani abin sai kuma yace “Lafiya..” A tak’aice...
“Yaya ka zauna dan Allah...” Ta fad’i cikin kashe murya, wani duban ya mata ya sanyata had’iye sauran kalaman nata, duk duniya Sahariyya bata tab’a cin karo da wanda takejin bala’in shakkarsa kaman Sameer ba, ikon Allah wai ita Sahariyya kejin shakku da tsoro had’ida fargaban wani bil’adam kaman haka, a iyakacin saninta tsabagen k’aurin suna da tai na rashin kunya da rashin mutunci yasa duk saurayin da yazo wajenta idan halinta bai koresa ba toh kuwa jama’an unguwa sai sun koresa, amma yau ita ke jin azabebben fad’uwan gaba da tsananin shakkun wani mutum haka... Ta had’i miyau da k’yar, har lokacin tana nan duk’a gabansa dikda cewa k’afar tata bai ida warkewa ba amma ko zafin tsugunon da tai bataji....
Sameer ya d’an gyara tsayuwarsa kad’an yana karantarta kana yace “Yaya jikin naki...?”
Nan fah Sahariyya taji maganar tasa tamkar wacce aka jefota, dad’i ya cika zuciyarta ashe har ya damu da ita haka.... Cikeda jin dad’i ta amsa masa da cewa “Da sauk’i Yaya aima saura kad’an ne, gobe muke komawa wajen mai d’aurin dama...”
Jinjina kansa yai har lokacin tsaye gabanta yake hannayensa dafe da kunkumimnsa, saida ya d’an gyara tsayuwarsa kana yace “Menene asalin abinda ya sameki, me ya janyo faruwar ciwon...?”
D’agowa tai tana dubansa wani irin dad’i na mamaye illahirin zuciyarta, a hankali ta furta “K’addara ce Yaya...”
Sameer ya jinjina kai kana ya maimaita “K’addara... Kin yarda da k’addara...?”
Wannan karon a d’an zabure ta d’ago tana dubansa, lokaci guda ta saki murmushi wanda yafi kamada yak’e kana tace “Na yarda da k’addara Yaya...”
“Good..” Ya furta a hankali yana mai jinjina kai yayinda Sahariyya ta shagala sosai da annashuwa, sinkayo muryarsa tai yana fad’in “Idan kin yarda da k’addara kaman yanda kika fad’i maiyasa kika biyewa mahaifiyarki kuke aibanta k’anwarki Raihaan don kawai bata kasance d’iyaga mahaifiyarki ba..?”
Wannan karon azabebben fad’uwan gaba taji ya sauk’a mata, ta tuna farin zuwansa gidan tun Kafin susan cewa shine Ma’aruf, nan fah Sahariyya ta shiga muzurai tana neman abin fad’i lokaci guda ta soma kame kame da inda inda... Sameer ya girgiza kai a hankali yana mai aika mata wani kallo lokaci guda ya sakale hannayensa cikin aljihun wandonsa kana yaci gaba da fad’in “Wacce kika k’ona da ganganci itace ta yarda da k’addara amma bake ba, nasan kinsan wa nake nufi.... Anyways Allah ya baki lafiya, ni zan wuce suna kirana a asibiti.... Idan Baba Alhaji yazo sai ki fad’a mishi nazo ban sameshi ba....” Daga haka bai jira cewarta ba yasa kai ya fice...
Sahariyya dake dab’e wajen tamkar wacce aka dasa kasa motsa koda d’an yatsarta tai, dik a tunaninta Sameer damuwarsa akanta yake nuna mata ashe ba haka bane, magana yaso yab’a mata kuma ba akan kowa ba sai kan shegiyar k’anwar nan nata... Wani irin zogi da rad’ad’i taji zuciyarta na mata, idanunta suka kad’a sukai jazir hawayen da basu shirya fitowa ba suka shiga zarya a kumatunta, wani irin tsanar Raihanah takeji kaman ta shak’eta ta mutu, fuskar Raihanah take hangowa tana mai furtawa a fili “Na tsaneki na tsaneki shegiya stinanniya munafuka algunguma mayya..!” Idanunta na zuban hawaye masu rad’ad’i take maganar cikin tsananin karaji...
A haka Haule ta shigo ta taddata, ganinta a duk’e tana hawaye ya sanya Haule k’arasawa da sauri ta shiga jijjigata tana fad’in “Ke Sahariyya... Lafiya... Meke faruwa.. Ina Ma’aruf d’in....?”
Sahariyya na hawaye take fad’in “Hajiya dik laifin munafukar Raihanar nan ne, annamimiya mai halin munafukan farko, nunawa take itace mutumiyar arziki keda ‘ya’yanki faragurbi... Munafuka wayasan kalan salon munafuncin da take masa can gidan Mamanin... Ni wllhi Hajiya kisa Baba Alhaji ya dawo da ita gida, Allah kad’ai yasan mai take masa acan mai shegen son mazan bala’i....” Ta k’arashe tana goge hawayen da suka wanke mata fuska...
Murmusawa kad’an Haule tai kana tace “Banda abinki mai Ma’aruf zai da wannan banzar yarinyar tausayice kawai take basa, kinsan shi ya mata aiki lokacinda ta k’one kuma Allah yayisa mai tausayi da tausasawa bacin haka ke ko a hanya yayi kama da wanda zai tarayya da Raihanah ne ai Ma’aruf saike naki ne, domin kaw an gama magana ki kwantar da hankalinki yanzu zan kira mahaifiyarsa mujin batun lefe a ina anka tsaya... Karma wannan ya tada miki hankali, ci gaba da shirye shiryenki, ki kirawo Fa’iza yau kuje ku cire ankonku muma ku ciro mana ankon gida iyanin....”
Kalaman Hajiya ya d’an tausasa zuciyar Sahariyya, ta saki murmushi tana mai furta “Shisa nake sonki Hajiyata...” Hajiya ta rungumeta tana fad’in “Aikinfi min wancan shashashar k’anwar taki wacce bata k’aunar uwarta....” Ta k’arashe tana aikama Naja’atu dake tattara wajen hrara... Giriza kai kurum Najah tai ba tareda cewa komai ba ta fice da parantin dake hannunta....
***
Kasancewar washe gari baida zuwa asibiti da wuri ya sanyashi yada zango gidansu abokinsa Shamsu don sun kwana biyu basu had’u ba, Shamsun ma wata k’aramar kwangila ya samu nan cikin gari da wata company shisa shima d’in bai zauna ba kwana biyun.... A parlor Sameer ya samu Mama suka gaisa tana masa tsiyan shida abokinsa aiki duk ya b’oyesu gwarama shi nada iyali amma abokin nasa bai ije kowa ba sai bautan neman kud’i....
Sameer ya d’an sosa k’eyarsa yana mai furta “Zai aje ne Mama....” Yai maganar yana duban k’ofa yanda Shamsu ke k’arasowa cikin parlorn hannunsa rik’eda mug alamun bai jima da tashi ba...
Mama ta dubi Shamsun baki a tab’e kana tace “Allah yasa yaji gori ya aje d’in, mutum gansameme kullum saidai ya tashi ya ishi mutane da tsifface tsiffacen baison cin wannan da safe baison cin wancan, idan kaji gori kai aure muma ma huta da wannan tsirin naka... K’aton kawai...” Ta k’arashe tana yab’a masa muguwar kallo...
Sameer kaw sai sakin murmushi yake yana duban yanda abonkin nasa ya had’e gira sosai....
“Mama fah safiyar da saura dan Allah a k’yaleni haka nan, kofa karin kumallo banyi ba...”
“Tafi can ka rufewa mutane baki, Kaga Sameer ka d’auki hotonsa ka raba a masallatai ko Allah zaisa a dace...”
“Mama neman kai kike dani...?” Shamsu yace yana mai mik’awa Sameer hannu domin yin masabaha...
Mama tace “Ahtoh naga abin naka bana k’are bane ai....”
Sameer dake danne dariyarsa yace “Yanda kikace hakan za’ai Mama...”
“Toh ai ba masallaci ya kamata kukai ba makarantar ‘yanmata ya kamata kukai tallan nawa...” Shamsu yace yana mai zama gefen Sameer...
D’an darawa sukai gaba d’aya kana Mama ta mik’e tana tambayan Sameer mai za’a kawo masa...
Cikeda ladabi yace “A’a Mama nikam a k’oshe nake na gode....”
Mama tace “Aiko dai kaji mai Iyali, wanine dai sai anyita fama dashi....”
Shamsu ya tari zancen nata da fad’in “Nima ruwan tea d’in nan kawai ya isheni Mamana...”
“Kadaiji dashi..” Mama tace sanda take bari masu parlorn...
D’an shaking hannu suka kumayi suna dariyar draman Mama kana Shamsu yace “Doc,ya akai ne... Kwana biyu ko k’yallinka ba’a gani, ko zumud’in angoncin ne ya soma b’oyeka....” Yai maganar cikeda zolaya...
Gajeren tsaki Sameer yai had’ida b’alla masa harara kana yace “Aure ko damuwa....”
Shamsu ya d’an dara kad’an “Yaushe aure ya koma damuwa, ince gashi kaida Mama kun hanani sakat.... Ni gwarama da kazo coz dama inatason mu had’u naji what are your plans...”
Fuzar da iska Sameer yai a hankali had’ida fitowa daga cikin kujeran kad’an, saida ya shafi fuskarsa da tafukan hannayensa kana yace “Wannan kuma saidai ka tambayisu Abbah don ni kaina ban sani ba....”
Dariya mai bayyana hak’wara Shamsu keyi yana mai furta “Sameer kenan, gaba d’aya sai ka juye min Sameer d’in dana sani sanda muke sch kafin ka auri Partner....”
Nanma dai d’an duban nasa kawai Sameer yai wannan karon harda tab’e baki kad’an “Kaidai baka tab’a d’aukan abu serious, na kawo maka matsalata kana dariya...”
“Toh kuka kakeso nayi.., Kai ba d’an gata bane, su Mummy Sun aura maka Siyama yanzu gashi su Abbah zasu aura maka Sahariyya... Ni amin Auren mana idan inada gatan....” Har yanzu dai dariyar bata bar saman fuskar Shamsu ba....
Mik’ewa tsaye Sameer yai yana zira hannaye cikin aljihu...
Shamsu dake sipping tea ya d’ago yana dubansa kana yace “Ina kuma zakaje naga dai shigowarka kenan...”