Sashe 92
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sameer yana tafe sashen Mamani ya tsaya yana hangen k’ofar sashen Aunty Lami tamkar mai son tuna wani abin... Haka kurum kaman wanda aka umarcesa ya nufi sashen nata sallama saman bakinsa....
Aunty Lami dake k’uryar d’aki tana waya da Haule, Haule na labarta mata kalan rashin darajan da Magajiya tazo har cikin gidanta tai mata nan ta sinkayo muryarsa mai cikeda k’warjini yana sallama... Gaban Lami ya yanke ya fad’i tamkar wacce aka aje mata guduma... Gaba d’aya saima ta daburce ta shiga amsa masa sallamar nasa cikin in ina.... Daga d’aya b’angaren Haule da itama ta sauraro sallamar tasa wanda ko shakka babu itama fad’uwar gaban ya haifar mata, cikin sauri taceda Lami “Dama ta sameki ki gama mana shi duk mu huta da fargaba da fad’uwar gaba...” Bata jira cewar Lami d’in ba ta datse kiran....Da k’yar tai k’ok’arin saita kanta kana tai masa izinin shigowa.....
Aunty Lami harda karkad’e masa kujera tana fad’in “Lale lale Uban masu gida, shigo abinka....”
Murmushi saman fuskar Sameer ya shigo kana ya soma gaidata bayan ya daidaita bisa kujera mai d’aukan mutum biyu wato two seater... Gaba d’aya Lami ya kasa zaune ta kasa tsaye dikda d’ingishi da take sakamon fad’owa da tai jikin window sanda take lek’ensu Abbah da Mamy....
Kankace mai ta cika gaban Sameer da kayan ciye ciye da shaye shaye tana fad’in “D’an gidana kaci abinci please... Ko kana son wani abinne yanzun na had’a maka....”
A hankali ya d’an murmusa kana yace “Karki damu Aunty aima a k’oshe nake, dama cewa nayi bara na shigo na dubaki don jiya Mamy ke cemin bakiji dad’i ba kin samu buguwa a k’afarki....”
Aunty Lami ta kuma mik’ar da k’afar tana mai tamke idanu alamun zogi kana tace “Wllhi am Uban masu gida... Kaga waccan k’yauran kitchen d’in shine fah na buga dashi, ka ganshin nan ya jima a haka nan, toh Abbanku bai samun zama balle a gyara ga gidan sai ‘yanmata saima ka rasa waye zaka aika....”
Sameer ya d’an karanceta a hankali kana yace “Karki damu Aunty zan turo mai gyara anjima kad’an a duba in sha Allah... Allah ya baki lafiya....”
Ta amsada “Haba Uban masu gida, ayi haka... Kai na kuwa gode fah... Allah dai shi saka da Alkhairi.... Ohni Lami yau ga Ma’aruf d’in ya dawo garemu har mun soma ganin alfanunsa... Allah mun gode maka da ka bayyana mana shi....” Ta k’arashe tana mai kamo bakin zani tana share hawaye tamkar gaskiya....
Sameer shiru yai tamkar mai nazari don baiga abin godiya da kuka a nan ba, kana ya d’anyi gyaran murya yace “Babu komai Aunty, ki kwantar da hankalinki na dawo gareku in sha Allah kuma bazan sake b’acewa ba...” Yayi maganar yana mai dubanta with a straight face....
Aunty Lami da bugun k’irjinta ya k’aru a hankali ta saki zanin da take share hawaye dashi tana duban cikin idanun Sameer da baya fad’i mata komai sai tsan tsan tsoro da fargaba ga k’warjininsa da ya hanata sukuni tin shigowarsa.... Kakkaurar miyau ta had’iya da k’yar kana ta saki murmushin yak’e tace “Haka ne Uban masu gida... Toh ko ruwan kasha mana...”
Mik’ewa yayi hannayensa sakale cikin aljihun wandonsa kana ya d’aura sassanyar murmushi saman kyakkywar fuskarsa yace “Na gode Aunty ban jima da shan ruwa ba next time in sha Allah...”
Aunty Lami ta bisa da kallo har ya fice tanaji cikin ranta tamkar yayi tuntub’e wajen ya fad’i gawa kowa ya huta, ta maidoda dubantaga ga contaminated drink d’in data kawo masa wanda ko kallo bai ishesa ba, tai k’wafa ta d’auka ta nufi kitchen dashi ta juye cikin sink, cikin ranta take ayyana cewa next time bazai tsallake ba idan ya tsallake wannan, tai murmushi sakamakon tuno abinda yafiso tun yana yaro wanda dashi zasuyi amfani su gama dashi kana tai k’wafa a fili ta furta “Muje zuwa Ma’aruf da sannu zaka fad’a tarkonmu...”
***
Jinge kansa yake jikin car seat d’in idanunsa a lumshe yana mai ci gaba da kad’a ‘yan yatsun hannunsa jikin steering wheel d’in motar.... Yusuf da duk tsawon lokacin karantarsa yake gyara zamansa ya d’anyi kana yace “We’ve been waiting here fo edges idan kanawa Allah muyi abu guda d’aya don wllhi na gaji....”
Da wutsiyar idanu Akram ya dubesa kana yace “Toh idan naje mai zance mata, kaina na kawo kokuwa Ogana nakema sharan fage...?”
Yusuf ya fuzar da iska a hankali had’ida tab’e baki kana yace “Rashin bin shawarinka ya janyo maka, saida na fad’a maka tun farko be frank with him, ka sanar dashi komai....”
Baikai aya ba Akram ya katsesa da fad’in “In sanar dashi mi... Cewa munyi tarayya wajen son mace guda kokuwa mai kakeso na sanar dashi...? Ni kama san abinda yafi damuna.... Wllhi ban sani ba if I can do this.... I’m not sure...” Ya k’arashe yana mai taunar lip d’insa na k’asa a hankali...
Yusuf yaci gaba da karantarsa a nitse kana yace “Alright here’s what you should do, amma shawarice....”
Akram ya dubesa da gefen ido kana yace “Ina saurarenka.....”
K’asaitacciyar murmushi Akram yayi bayan Yusuf ya gama basa shawarin hukuncin da zai yanke, wanda kuma sosai yayi na’am da shawarin abokin nasa da wannan matsaya suka nufi gidan Aunty Bara’atu kaman yanda Atika ta kwatanta masu.....
Kallon Atika da Aunty Bara’atu kurum take tana mamakin yanda suka tasata gaba sai tayi ado don zata fita zance... D’an turo baki gaba tai kana tace “Wllhi Aunty da dai kin daina biye Atika matsala ce bai ganta ba, ni ko zamanin da nake budurwa ma ai ban fita zance ba balle yanzu da nake bazawara....Kuma harda wani ado Aunty aima sai yace sonsa nake....”
Hararan da Aunty B ta narka mata ya sanyata yin shiru....
Atika ta k’unshe dariyarta sanda take ajiye had’edd’iyar doguwar riga ‘yar dubai mai launin ruwan hoda Wato peach saman gado, harara Zulfah ta rakata dashi had’idayin k’wafa na zan kamaki ne...
Atika ta kuma darawa kana tace “Aunty wannan ‘yar gidan naki saifa kinyi da gaske don wllhi ko a office haka nake fama da ita, duk wanda yace yana sonta sun b’ata kenan, harta Manager yanzu bata masa murmushin da take masa da, shi wannan abokin Yusuf d’in ma na tabbata don dai kin saka baki ne bansan ko gidan Hafiz takeso mu koma ba....” Nan ma harara Zulfah ta narka mata kana Aunty B ta tari zancen da fad’in “Ai Hafiz saidai yaga Katin gayyata da izinin Allah.. Mai ake da jinin Haule jinin tsiya....”
Zulfah ta marairaice fuska tace “Kai Aunty Hajiya fah tayi nadama...”
Muguwar kallo Aunty B ta kuma watsa mata kana tace “Idan Hajiya Haule zata shekara tana cewa ta tuba tayi nadama bazan tab’a yarda ba... Ke idanma ta tuban ba komawa gidan d’anta zakiyi ba kin gama zaman aure dashi....”
Atika ta mik’e tana amsa wayarta da ake bugawa... Ko ba’ace ba kasan bak’on nasu ne ya iso, nan Yusuf ke sanar da ita gasu sun iso... Aunty B tasa Zulai ta bud’e masu parlor k’ofan gaba...
Zulfa’u kaw gaba d’aya sai jinta take wani iri haka nan ga bugu da k’irjinta keyi, yau ita Zulfa’u ce zata fita wajen wani da sunan yazo neman aurenta, da gaske dai Ya Hafiz ba mijinta bane... Toh mai zatace, ya ma ake firan.. Abu ne da bata sanshi ba tun tasowarta tinda Hafiz ma rana tsaka akace an bata shi.... Tana tsaka da tunanin muryar Aunty Bara’atu ya katseta “Ki k’arasa shirinki a hankali Zulai ta kai masu abin tab’awa....”
Gabanta ya kuma bada sautin rasss... A hankali ta jinjina kai kana tace “Toh Aunty....”
D’aukar doguwar rigar tai tana k’are mata kallo kana ta zirata, ta d’ago tana duban kanta jikin mirror sosai ya mata kyau ya zauna a jikinta, zallan powder ta shafa shima don Atika ta tak’ura mata saiko d’an man baki data shafa, ta d’au mayafin rigar ta rufa akan sumarta wanda yake a tsefe ta tufkeshi a tsakiya mai yalwan cika dukda bai faye tsawo ba...
Atika tai tsaye tana dubanta kana tace “K’awata kin fito, babu wanda zai tunanin kin tab’a aure balle haihuwa... Masha Allah son kowa k’in wanda bai samu ba....”
‘Y’ar gajeriyar murmushi tai kana “Kedai kyaji dashi... Ni wllhi don dai kun tak’ura min ne amma harga Allah banyi shirin soma wani relationship yanzu ba....Not now gaskiya....” Ta k’arashe tana mai zama saman gado gijif..
Atika ta dara kana tace “Ni wllhi badani kike, Akram fah had’edd’en gaye ne na gaban goshin Governor to be d’inmu... Ni dama tinda Yusuf yace min program d’inki na kashesa nace za’a iso wajen.... Nidai Wllhi karki badamu ehe ki bari kawai musha biki, amma fah ina tausayin manager don Wllhi shima da gaske yake sonki....”
Hararanta Zulfah ta kumayi kana tace “Kedai kyaji dashi....”
Suna a haka Aunty Bara’atu ta turo k’ofan d’akin ta shigo ta dubi Atika tace “Haka akeyi kun k’yale bayin Allah sunata zaune... Ki lek’a ku gaisa kafin na taso k’eyar k’awar taki...”
Atika ta mik’e ta d’au mayafi tana mai darawa kana tace “An gama Auntynmu...”
***
A parlor Sameer ya bar Shamsu da Khalid suna firan ball ya shiga amsa kiran Mummynsa....
Koda suka gaisa Hajiya Fatahiyya sai cewa tai “Sameer, Son are you sure you’re alright... Daga muryarka inaji kaman wani abu na damunka... What’s wrong son.... please tell me...”
Fuzar da iska yai a hankali don yasan Mummy ta masa farin sanin da bazai iya b’oye mata damuwarsa ba.... Katse shirun nasa tai da fad’in “Is everything alright with your family...?”
Aunty Lami dake k’uryar d’aki tana waya da Haule, Haule na labarta mata kalan rashin darajan da Magajiya tazo har cikin gidanta tai mata nan ta sinkayo muryarsa mai cikeda k’warjini yana sallama... Gaban Lami ya yanke ya fad’i tamkar wacce aka aje mata guduma... Gaba d’aya saima ta daburce ta shiga amsa masa sallamar nasa cikin in ina.... Daga d’aya b’angaren Haule da itama ta sauraro sallamar tasa wanda ko shakka babu itama fad’uwar gaban ya haifar mata, cikin sauri taceda Lami “Dama ta sameki ki gama mana shi duk mu huta da fargaba da fad’uwar gaba...” Bata jira cewar Lami d’in ba ta datse kiran....Da k’yar tai k’ok’arin saita kanta kana tai masa izinin shigowa.....
Aunty Lami harda karkad’e masa kujera tana fad’in “Lale lale Uban masu gida, shigo abinka....”
Murmushi saman fuskar Sameer ya shigo kana ya soma gaidata bayan ya daidaita bisa kujera mai d’aukan mutum biyu wato two seater... Gaba d’aya Lami ya kasa zaune ta kasa tsaye dikda d’ingishi da take sakamon fad’owa da tai jikin window sanda take lek’ensu Abbah da Mamy....
Kankace mai ta cika gaban Sameer da kayan ciye ciye da shaye shaye tana fad’in “D’an gidana kaci abinci please... Ko kana son wani abinne yanzun na had’a maka....”
A hankali ya d’an murmusa kana yace “Karki damu Aunty aima a k’oshe nake, dama cewa nayi bara na shigo na dubaki don jiya Mamy ke cemin bakiji dad’i ba kin samu buguwa a k’afarki....”
Aunty Lami ta kuma mik’ar da k’afar tana mai tamke idanu alamun zogi kana tace “Wllhi am Uban masu gida... Kaga waccan k’yauran kitchen d’in shine fah na buga dashi, ka ganshin nan ya jima a haka nan, toh Abbanku bai samun zama balle a gyara ga gidan sai ‘yanmata saima ka rasa waye zaka aika....”
Sameer ya d’an karanceta a hankali kana yace “Karki damu Aunty zan turo mai gyara anjima kad’an a duba in sha Allah... Allah ya baki lafiya....”
Ta amsada “Haba Uban masu gida, ayi haka... Kai na kuwa gode fah... Allah dai shi saka da Alkhairi.... Ohni Lami yau ga Ma’aruf d’in ya dawo garemu har mun soma ganin alfanunsa... Allah mun gode maka da ka bayyana mana shi....” Ta k’arashe tana mai kamo bakin zani tana share hawaye tamkar gaskiya....
Sameer shiru yai tamkar mai nazari don baiga abin godiya da kuka a nan ba, kana ya d’anyi gyaran murya yace “Babu komai Aunty, ki kwantar da hankalinki na dawo gareku in sha Allah kuma bazan sake b’acewa ba...” Yayi maganar yana mai dubanta with a straight face....
Aunty Lami da bugun k’irjinta ya k’aru a hankali ta saki zanin da take share hawaye dashi tana duban cikin idanun Sameer da baya fad’i mata komai sai tsan tsan tsoro da fargaba ga k’warjininsa da ya hanata sukuni tin shigowarsa.... Kakkaurar miyau ta had’iya da k’yar kana ta saki murmushin yak’e tace “Haka ne Uban masu gida... Toh ko ruwan kasha mana...”
Mik’ewa yayi hannayensa sakale cikin aljihun wandonsa kana ya d’aura sassanyar murmushi saman kyakkywar fuskarsa yace “Na gode Aunty ban jima da shan ruwa ba next time in sha Allah...”
Aunty Lami ta bisa da kallo har ya fice tanaji cikin ranta tamkar yayi tuntub’e wajen ya fad’i gawa kowa ya huta, ta maidoda dubantaga ga contaminated drink d’in data kawo masa wanda ko kallo bai ishesa ba, tai k’wafa ta d’auka ta nufi kitchen dashi ta juye cikin sink, cikin ranta take ayyana cewa next time bazai tsallake ba idan ya tsallake wannan, tai murmushi sakamakon tuno abinda yafiso tun yana yaro wanda dashi zasuyi amfani su gama dashi kana tai k’wafa a fili ta furta “Muje zuwa Ma’aruf da sannu zaka fad’a tarkonmu...”
***
Jinge kansa yake jikin car seat d’in idanunsa a lumshe yana mai ci gaba da kad’a ‘yan yatsun hannunsa jikin steering wheel d’in motar.... Yusuf da duk tsawon lokacin karantarsa yake gyara zamansa ya d’anyi kana yace “We’ve been waiting here fo edges idan kanawa Allah muyi abu guda d’aya don wllhi na gaji....”
Da wutsiyar idanu Akram ya dubesa kana yace “Toh idan naje mai zance mata, kaina na kawo kokuwa Ogana nakema sharan fage...?”
Yusuf ya fuzar da iska a hankali had’ida tab’e baki kana yace “Rashin bin shawarinka ya janyo maka, saida na fad’a maka tun farko be frank with him, ka sanar dashi komai....”
Baikai aya ba Akram ya katsesa da fad’in “In sanar dashi mi... Cewa munyi tarayya wajen son mace guda kokuwa mai kakeso na sanar dashi...? Ni kama san abinda yafi damuna.... Wllhi ban sani ba if I can do this.... I’m not sure...” Ya k’arashe yana mai taunar lip d’insa na k’asa a hankali...
Yusuf yaci gaba da karantarsa a nitse kana yace “Alright here’s what you should do, amma shawarice....”
Akram ya dubesa da gefen ido kana yace “Ina saurarenka.....”
K’asaitacciyar murmushi Akram yayi bayan Yusuf ya gama basa shawarin hukuncin da zai yanke, wanda kuma sosai yayi na’am da shawarin abokin nasa da wannan matsaya suka nufi gidan Aunty Bara’atu kaman yanda Atika ta kwatanta masu.....
Kallon Atika da Aunty Bara’atu kurum take tana mamakin yanda suka tasata gaba sai tayi ado don zata fita zance... D’an turo baki gaba tai kana tace “Wllhi Aunty da dai kin daina biye Atika matsala ce bai ganta ba, ni ko zamanin da nake budurwa ma ai ban fita zance ba balle yanzu da nake bazawara....Kuma harda wani ado Aunty aima sai yace sonsa nake....”
Hararan da Aunty B ta narka mata ya sanyata yin shiru....
Atika ta k’unshe dariyarta sanda take ajiye had’edd’iyar doguwar riga ‘yar dubai mai launin ruwan hoda Wato peach saman gado, harara Zulfah ta rakata dashi had’idayin k’wafa na zan kamaki ne...
Atika ta kuma darawa kana tace “Aunty wannan ‘yar gidan naki saifa kinyi da gaske don wllhi ko a office haka nake fama da ita, duk wanda yace yana sonta sun b’ata kenan, harta Manager yanzu bata masa murmushin da take masa da, shi wannan abokin Yusuf d’in ma na tabbata don dai kin saka baki ne bansan ko gidan Hafiz takeso mu koma ba....” Nan ma harara Zulfah ta narka mata kana Aunty B ta tari zancen da fad’in “Ai Hafiz saidai yaga Katin gayyata da izinin Allah.. Mai ake da jinin Haule jinin tsiya....”
Zulfah ta marairaice fuska tace “Kai Aunty Hajiya fah tayi nadama...”
Muguwar kallo Aunty B ta kuma watsa mata kana tace “Idan Hajiya Haule zata shekara tana cewa ta tuba tayi nadama bazan tab’a yarda ba... Ke idanma ta tuban ba komawa gidan d’anta zakiyi ba kin gama zaman aure dashi....”
Atika ta mik’e tana amsa wayarta da ake bugawa... Ko ba’ace ba kasan bak’on nasu ne ya iso, nan Yusuf ke sanar da ita gasu sun iso... Aunty B tasa Zulai ta bud’e masu parlor k’ofan gaba...
Zulfa’u kaw gaba d’aya sai jinta take wani iri haka nan ga bugu da k’irjinta keyi, yau ita Zulfa’u ce zata fita wajen wani da sunan yazo neman aurenta, da gaske dai Ya Hafiz ba mijinta bane... Toh mai zatace, ya ma ake firan.. Abu ne da bata sanshi ba tun tasowarta tinda Hafiz ma rana tsaka akace an bata shi.... Tana tsaka da tunanin muryar Aunty Bara’atu ya katseta “Ki k’arasa shirinki a hankali Zulai ta kai masu abin tab’awa....”
Gabanta ya kuma bada sautin rasss... A hankali ta jinjina kai kana tace “Toh Aunty....”
D’aukar doguwar rigar tai tana k’are mata kallo kana ta zirata, ta d’ago tana duban kanta jikin mirror sosai ya mata kyau ya zauna a jikinta, zallan powder ta shafa shima don Atika ta tak’ura mata saiko d’an man baki data shafa, ta d’au mayafin rigar ta rufa akan sumarta wanda yake a tsefe ta tufkeshi a tsakiya mai yalwan cika dukda bai faye tsawo ba...
Atika tai tsaye tana dubanta kana tace “K’awata kin fito, babu wanda zai tunanin kin tab’a aure balle haihuwa... Masha Allah son kowa k’in wanda bai samu ba....”
‘Y’ar gajeriyar murmushi tai kana “Kedai kyaji dashi... Ni wllhi don dai kun tak’ura min ne amma harga Allah banyi shirin soma wani relationship yanzu ba....Not now gaskiya....” Ta k’arashe tana mai zama saman gado gijif..
Atika ta dara kana tace “Ni wllhi badani kike, Akram fah had’edd’en gaye ne na gaban goshin Governor to be d’inmu... Ni dama tinda Yusuf yace min program d’inki na kashesa nace za’a iso wajen.... Nidai Wllhi karki badamu ehe ki bari kawai musha biki, amma fah ina tausayin manager don Wllhi shima da gaske yake sonki....”
Hararanta Zulfah ta kumayi kana tace “Kedai kyaji dashi....”
Suna a haka Aunty Bara’atu ta turo k’ofan d’akin ta shigo ta dubi Atika tace “Haka akeyi kun k’yale bayin Allah sunata zaune... Ki lek’a ku gaisa kafin na taso k’eyar k’awar taki...”
Atika ta mik’e ta d’au mayafi tana mai darawa kana tace “An gama Auntynmu...”
***
A parlor Sameer ya bar Shamsu da Khalid suna firan ball ya shiga amsa kiran Mummynsa....
Koda suka gaisa Hajiya Fatahiyya sai cewa tai “Sameer, Son are you sure you’re alright... Daga muryarka inaji kaman wani abu na damunka... What’s wrong son.... please tell me...”
Fuzar da iska yai a hankali don yasan Mummy ta masa farin sanin da bazai iya b’oye mata damuwarsa ba.... Katse shirun nasa tai da fad’in “Is everything alright with your family...?”