Sashe 81
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru Sameer ya d’anyi kana yace “Wannan tsakaninku ne Hafiz, ba hurumina bane.... Allah ya baka lafiya...”
Hafiz ya jinjina kai a hankali yana mai rintse idanunsa wasu irin hawaye masu d’umi suka kuma zubo masa.... Jikkunansu sukai sanyi gaba d’aya, Baba Alhaji ya fice cikeda borin kunya yayinda Hajiya ta samu ta silale itama ta nufi can gidan Hafiz d’in dubo Sawwama don taji har wani tunanin Zulfah Hafiz ya soma, abinda bata fata ko bayan ranta ace Hafiz ya maidoda Zulfah d’akinta....
***
Akram ya dubi Yusuf a karo na biyu kana yace “Kanaga banyi mata hanzari ba....?”
Yusuf ya kuma karyan raken dake rik’e hannunsa na dama kana yace “Kasanfa hausawa na cewa A bari ya huce shike kawo rabon wani.... Mutumina this is the right time, na tabbata tuni manema sun soma kawo mata hari so gwara kawai ka making move.... Mu k’arasa Atika tai mana iso....”
Akram ya zuba duka hannayensa biyu saman steering wheel kana ya sauk’e ajiyan zuciya kad’an yace “Amma bazataga mun biyota wajen aikinta mun tak’urata ba....?”
Gajeren tsaki Yusuf yai kana yace “Wataran fah kayan haushi ne dakai, idan bazakai amfani da damar daka samu ba kada ka kuma zuwa kanamin zancen wata Zulfa’u ka gane koh... Na fad’a maka ni nan na sanar da Atika ta shirya mana yanda za’ai muga Zulfah lokacin break d’insu, idan kuma baka shirya ganinta bane toh sai naji...”Ya k’arashe yana mai karyan rakensa....
Harara Akram ya watsa masa kana ya kunna motar, Yusuf yaja marfin mota ya rufe kana suka d’auki hanyar station d’in su Zulfah....
Suna tafe ne wayar salulansa dake aje gefe ta d’auki ruri, ya d’an rage speed kana yakai dubansaga screen d’in wayar, ba kowa bane illa boss d’insa Engr Mutallab.... Yai saurin d’agawa cikeda girmamawa, take Engr d’in ke sanar dashi ya bar duk abinda yake yazo Office ya sameshi...
Akram yace “Alright your excellency gani nan zuwa....” Ya k’arashe yana mai karya steering motar, lokaci guda yake furta “Change of plans... Babu gani Zulfa’u yau...”
Yusuf ya tab’e baki kad’an kana yace “Aidai da ka sanar dashi ka tafi neman aurene bazai katse ka ba....”
Akram ya jefo masa harara gajeriya kana yace “Sallah ne kawai bazan katse ba idan his excellency yanada buk’atan ganina... Komai a bayansa yake...”
Yusuf ya kuma tab’e baki yace “Naga alama ai... Kaga barin kira Atika na sanar da ita bazamu samu zuwa yau ba....”
Atika dake faman rarraba idanu a a cafeteria d’in, tana hango ta yanda zataga su Yusuf shiru bata gansu ba, sai faman waige waige take gashi dai sun ida cin lunch d’insu.... Girgiza kai Zulfah tai kana tace “Wai wanine kike jira...? Idan ba jiran wani kike ba kiwa Allah ki tashi mu koma office...”
Hannunta Atika ta rik’e ta kuma zaunarta tana fad’in “D’an k’aramin lokaci kedai....”
Zulfah ta girgiza kai kurum tana mai juya idanu had’ida jan gajeren tsaki... Daidai nan wayar Atika ta d’auki ruri, Yusuf ne mai kiran nata.... Tai saurin matsawa gefe tana tambayarsa mai ya hanasu zuwa har yanzu....
Nan Yusuf ke sanar da ita something came up dole suka canza plan....
Atika da tuni ta shak’i haushi cewa tai “Ni na fad’a maka wannan abokin naka is not serious, da alama Zulfah ba class d’insa bane don harta ogoginmu na nan station suna nuna kulawa akanta, idan baiyi da gaske ba zaiji a salansa....”
Yusuf yace “Ya zakice haka, ogansa ne ya kirasa kedai kici gaba da mana sharan fada kawai please kinji... Yauwa na gode k’anwata...”
Gajeren tsaki tai kana ta dawo taceda Zulfah su koma Office... Zulfah dai dubanta kawai tai kana ta tattari belongings d’inta suka nufi office... Suna tafe Zulfah ke tambayar Atikan ko lafiya take.... Atika tace lafiya lou wani saurayinta ne yace zaizo toh kuma sai yace mata uziri ya rik’esa...
Zulfah batace komai ba sai jinjina kai da tai...
Atika ta d’an dubeta kana tace “Waini Zulfa’u meye shirinki...?”
Zulfah ta d’an dubeta kana tace “Ban gane ba... Shirina kaman yaya...?”
Atika ta murmusa tace “Ina nufin kinada burin aure nan kusa..? don naga da yawan staff d’inmu idanunsu na kanki ne....”
D’an dubanta Zulfah tai kana ta dubi wani gefen, lokaci guda take furta “After what I went through banajin nayi shirin kasancewa da wani namiji kuma...”
Atika tai shiru na tsawon shud’ewan wasu dak’ik’ai kana tace “Does that mean you haven’t moved on from your ex husband... Kina sonshi ne har yanzu....?”
Wani irin duba ta mata kana ta sauk’e ajiyan zuciya tace “Wasu lokuta mukan tsinci kawunanmu cikin al’amra masu wuyan fasaltuwa, so tari Allah yakan jarabci bawansa da abinda yafi rainawa a rayuwa.... Ko a baya ba auren soyayya nayida Ya Hafiz ba... Idan kika tambayeni ban san wata soyayyan d’ah namiji ba face na iyayena da ‘yan uwana saiko d’iyata da na rasa... Hasalima ni Zulfa’u na taso cikin tsanane a tsakanin danginmu, harta mahaifina da Kakata basa k’aunata kan laifin da sam ban aikata, kan laifin b’acewan d’an uwana Ma’aruf.....To them I was nothing but a curse... Bayan mahaifiyata da k’annena guda biyu no one believes in me, sun yarda cewa mai farar k’afa aka haifoni har saida Allah ya wankeni ya kuma dasa k’aunata cikin zukatansu.... Toh kinga ni bansan wata soyayya ba bansan ya ake jinta ba... Idan nace maki ina son Ya Hafiz na maki k’arya don bansanma ya take ba, the only thing I know shine zaiyi wuya kayi rayuwar aure da mutum sannan a cikin rayuwar har Allah ya baku rabo cikinta kace bazakaji komai gameda mutum ba koda kuwa ace b’angare na tausayawa ne.... A halin yanzu babu wani shiri na aure ko soyayya a gabana, burina shine naci gaba da aikina da kuma samun nasara had’ida kwanciyan hankali.... Kin fahimta....”
Shiru Atika tai tana dubanta har takai aya, tausayin rayuwar da Zulfah tai a baya ya cika mata zuciya, ta saki murmushi a hankali kana tace “Toh kisa a ranki cikin masoyanki harda k’awarki Atika... Sannan na yarda dake na yarda cewa ke ba mai farar k’afa bace kuma in sha Allah a tattareda ke akwai babban al’amari wanda kowa harta masu cewa kinada farin k’afa zasu amfana ta dalilinki....”
Zulfah ta murmusa kana tace “Na gode k’awata nima ina k’aunarki tsakaniga Allah...”
Sukai murmushi su duka biyun kana suka nufi cikin studio....
**
Tin daga k’ofar gidan gaban Hajiya ke bugun tara tara.... Jikinta bai ida sanyi ba saida ta shiga cikin gidan taga bad’alan da ake aikatawa ga hayak’in kayan maye had’ida warinsa ya gauraye gidan gaba d’aya, ta shiga toshe hanci tana tari da k’yar....
Can ta hangi Sawwama sai rawan ‘yan bori take tanayi tana kora barasa ga ‘yan daudu na tayata mai gurmi naci gaba da aikinsa...
Hajiya ta d’aura hannaye duka biyu aka tana nishi da k’yar take furta “Na shiga uku... Na shiga uku ni Haule mai zan gani.....?!!”
***
Kana ganin Muhibbah kasan a d’auke take, Najma ta shigo tana mata kukan yunwa, wani uban tsawa data dararawa yarinyar saida ya sanyata sakin fitsari a wando... Yarinyar ta shiga jada baya jikinta na rawa... Yamutsa fuska Muhibbah take ganin fitsarin da yarinyar ta saki tana mai furta “Oh no no this isn’t happening...” Gashi Engr yasa ta rage ma’aikatan gidan a cewarsa idan tayi niyyan shiryuwa da gaske sai ta fara da kulada iyalanta...
Kira ta shiga dokawa Suwaiba wacce ita kad’ai aka bari harta Cooks d’in gidan Engr ya sallamesu...
Suwaiba ta k’araso a guje tana mai risinawa....
Muhibbah na mata nunida Najma take fad’in “Take care of her... Ta isheni da kuka.... Uban mai kike da har yanzu baki ida lunch d’in ba....?”
Suwaiba tace “Aunty aikin ne sunmin yawa... Kuma ai kaman naji Alhaji yace kece zakike abinci...”
Wani uwar harara data watsawa Suwaiba kana ta isa ta janyo kunnenta guda tace “Na maki kama da mai dafa abinci...? Answer me..!! Na maki kama da mai girki....??”
Suwaiba dake faman tamke fuska alamun taji zafin rik’on cikin sauri take girgiza kai alamun a’a....
Muhibbah ta jinjina kai tace “If you don’t want to get yourself fired toh kiyi duk wasu ayyukan da kikasan ma’aikata keyi gidan nan... Kuma Wllhi saura Engr ya dawo kice masa kece kikai abinci sai nayi d’add’aya dake... Tashi ki bani waje...”
Ta tashi da sauri tana goge hawayen da suka zubo mata... Muhibbah ta kuma kiranta tana mata nuni da Najam tace “Ki gyara wajen nan kafin na dawo....” Tana ida fad’in haka ta haye sama... Najma tai saurin rungumar Suwaiba tana kuka.... Suwaiba ta rungume yarinyar cikeda tausayawa, badon tausayin yaran ba da ganin girman Engr tabbas da tuni ta bar aikin gidan... Matace tamkar ba ‘yar Adam ba ko ma d’iyoyin wasu bazakayi irin wannan rik’on ba balle yaran da ka tsuguna ka haifesu....
Suwaiba ta d’auki yarinyar suka nufi kitchen tare tana mai lallashi had’ida jantada wasa...
Ita kaw Muhibbah tana zuwa d’aki, drawer mai d’aukeda kayan mayenta ta janyo... Ta ciro k’waya guda d’aya ta murmusheshi lokaci guda ta toshe hancinta guda ta shiga shak’a tana mai bubbuga kanta.... Saida taji kanta acan sararin samaniya kafin ta koma gefe tana hango duniyar na juye mata... Tana a haka ta jiyo k’aran shigowar motarsa... Cikin sauri ta mik’e tana k’ok’arin kimtsa kanta dukda cewa k’wayar bai saketa ba, hasalima datasan da wuri zai komo gida da bata sha ba....
Saida ta saita kanta kafin ta sauk’o k’asa....
Akram ne ya soma fitowa rik’eda jakan Engr d’in ya mik’a mata... Tai masa wani duba a yatsine kana tace ya aje a parlor ta k’arada in Engr d’in .... Akram ya bata amsada yana cikin mota...
Tsaye tai tana mamakin mai yakeyi cikin mota, nan dai ta nufi motar...
K’arar radio ta soma jiyowa cikin muryar wata mace mai dad’in sauraro yanda take furta “Toh jama’a masu saurarenmu yauma a nan zamu dasa aya... A shiri na gaba zaku jimu cikin wani sabon shirin... Kuci gaba da kasancewa damu a tasharku kuma zab’inku... A madadin mai kulada shirin da kuma abokiyar aikina tareda ni kaina Zulfa’u Usman Mailafiya muke cewa ku huta lafiya.....”
Muhibbah takai dubantaga mijinta yanda yake kishingid’e jikin car seat idanunsa a lumshe sihirtacciyar murmushi kwance saman fuskarsa....
SameenaAleeyou📚
Hafiz ya jinjina kai a hankali yana mai rintse idanunsa wasu irin hawaye masu d’umi suka kuma zubo masa.... Jikkunansu sukai sanyi gaba d’aya, Baba Alhaji ya fice cikeda borin kunya yayinda Hajiya ta samu ta silale itama ta nufi can gidan Hafiz d’in dubo Sawwama don taji har wani tunanin Zulfah Hafiz ya soma, abinda bata fata ko bayan ranta ace Hafiz ya maidoda Zulfah d’akinta....
***
Akram ya dubi Yusuf a karo na biyu kana yace “Kanaga banyi mata hanzari ba....?”
Yusuf ya kuma karyan raken dake rik’e hannunsa na dama kana yace “Kasanfa hausawa na cewa A bari ya huce shike kawo rabon wani.... Mutumina this is the right time, na tabbata tuni manema sun soma kawo mata hari so gwara kawai ka making move.... Mu k’arasa Atika tai mana iso....”
Akram ya zuba duka hannayensa biyu saman steering wheel kana ya sauk’e ajiyan zuciya kad’an yace “Amma bazataga mun biyota wajen aikinta mun tak’urata ba....?”
Gajeren tsaki Yusuf yai kana yace “Wataran fah kayan haushi ne dakai, idan bazakai amfani da damar daka samu ba kada ka kuma zuwa kanamin zancen wata Zulfa’u ka gane koh... Na fad’a maka ni nan na sanar da Atika ta shirya mana yanda za’ai muga Zulfah lokacin break d’insu, idan kuma baka shirya ganinta bane toh sai naji...”Ya k’arashe yana mai karyan rakensa....
Harara Akram ya watsa masa kana ya kunna motar, Yusuf yaja marfin mota ya rufe kana suka d’auki hanyar station d’in su Zulfah....
Suna tafe ne wayar salulansa dake aje gefe ta d’auki ruri, ya d’an rage speed kana yakai dubansaga screen d’in wayar, ba kowa bane illa boss d’insa Engr Mutallab.... Yai saurin d’agawa cikeda girmamawa, take Engr d’in ke sanar dashi ya bar duk abinda yake yazo Office ya sameshi...
Akram yace “Alright your excellency gani nan zuwa....” Ya k’arashe yana mai karya steering motar, lokaci guda yake furta “Change of plans... Babu gani Zulfa’u yau...”
Yusuf ya tab’e baki kad’an kana yace “Aidai da ka sanar dashi ka tafi neman aurene bazai katse ka ba....”
Akram ya jefo masa harara gajeriya kana yace “Sallah ne kawai bazan katse ba idan his excellency yanada buk’atan ganina... Komai a bayansa yake...”
Yusuf ya kuma tab’e baki yace “Naga alama ai... Kaga barin kira Atika na sanar da ita bazamu samu zuwa yau ba....”
Atika dake faman rarraba idanu a a cafeteria d’in, tana hango ta yanda zataga su Yusuf shiru bata gansu ba, sai faman waige waige take gashi dai sun ida cin lunch d’insu.... Girgiza kai Zulfah tai kana tace “Wai wanine kike jira...? Idan ba jiran wani kike ba kiwa Allah ki tashi mu koma office...”
Hannunta Atika ta rik’e ta kuma zaunarta tana fad’in “D’an k’aramin lokaci kedai....”
Zulfah ta girgiza kai kurum tana mai juya idanu had’ida jan gajeren tsaki... Daidai nan wayar Atika ta d’auki ruri, Yusuf ne mai kiran nata.... Tai saurin matsawa gefe tana tambayarsa mai ya hanasu zuwa har yanzu....
Nan Yusuf ke sanar da ita something came up dole suka canza plan....
Atika da tuni ta shak’i haushi cewa tai “Ni na fad’a maka wannan abokin naka is not serious, da alama Zulfah ba class d’insa bane don harta ogoginmu na nan station suna nuna kulawa akanta, idan baiyi da gaske ba zaiji a salansa....”
Yusuf yace “Ya zakice haka, ogansa ne ya kirasa kedai kici gaba da mana sharan fada kawai please kinji... Yauwa na gode k’anwata...”
Gajeren tsaki tai kana ta dawo taceda Zulfah su koma Office... Zulfah dai dubanta kawai tai kana ta tattari belongings d’inta suka nufi office... Suna tafe Zulfah ke tambayar Atikan ko lafiya take.... Atika tace lafiya lou wani saurayinta ne yace zaizo toh kuma sai yace mata uziri ya rik’esa...
Zulfah batace komai ba sai jinjina kai da tai...
Atika ta d’an dubeta kana tace “Waini Zulfa’u meye shirinki...?”
Zulfah ta d’an dubeta kana tace “Ban gane ba... Shirina kaman yaya...?”
Atika ta murmusa tace “Ina nufin kinada burin aure nan kusa..? don naga da yawan staff d’inmu idanunsu na kanki ne....”
D’an dubanta Zulfah tai kana ta dubi wani gefen, lokaci guda take furta “After what I went through banajin nayi shirin kasancewa da wani namiji kuma...”
Atika tai shiru na tsawon shud’ewan wasu dak’ik’ai kana tace “Does that mean you haven’t moved on from your ex husband... Kina sonshi ne har yanzu....?”
Wani irin duba ta mata kana ta sauk’e ajiyan zuciya tace “Wasu lokuta mukan tsinci kawunanmu cikin al’amra masu wuyan fasaltuwa, so tari Allah yakan jarabci bawansa da abinda yafi rainawa a rayuwa.... Ko a baya ba auren soyayya nayida Ya Hafiz ba... Idan kika tambayeni ban san wata soyayyan d’ah namiji ba face na iyayena da ‘yan uwana saiko d’iyata da na rasa... Hasalima ni Zulfa’u na taso cikin tsanane a tsakanin danginmu, harta mahaifina da Kakata basa k’aunata kan laifin da sam ban aikata, kan laifin b’acewan d’an uwana Ma’aruf.....To them I was nothing but a curse... Bayan mahaifiyata da k’annena guda biyu no one believes in me, sun yarda cewa mai farar k’afa aka haifoni har saida Allah ya wankeni ya kuma dasa k’aunata cikin zukatansu.... Toh kinga ni bansan wata soyayya ba bansan ya ake jinta ba... Idan nace maki ina son Ya Hafiz na maki k’arya don bansanma ya take ba, the only thing I know shine zaiyi wuya kayi rayuwar aure da mutum sannan a cikin rayuwar har Allah ya baku rabo cikinta kace bazakaji komai gameda mutum ba koda kuwa ace b’angare na tausayawa ne.... A halin yanzu babu wani shiri na aure ko soyayya a gabana, burina shine naci gaba da aikina da kuma samun nasara had’ida kwanciyan hankali.... Kin fahimta....”
Shiru Atika tai tana dubanta har takai aya, tausayin rayuwar da Zulfah tai a baya ya cika mata zuciya, ta saki murmushi a hankali kana tace “Toh kisa a ranki cikin masoyanki harda k’awarki Atika... Sannan na yarda dake na yarda cewa ke ba mai farar k’afa bace kuma in sha Allah a tattareda ke akwai babban al’amari wanda kowa harta masu cewa kinada farin k’afa zasu amfana ta dalilinki....”
Zulfah ta murmusa kana tace “Na gode k’awata nima ina k’aunarki tsakaniga Allah...”
Sukai murmushi su duka biyun kana suka nufi cikin studio....
**
Tin daga k’ofar gidan gaban Hajiya ke bugun tara tara.... Jikinta bai ida sanyi ba saida ta shiga cikin gidan taga bad’alan da ake aikatawa ga hayak’in kayan maye had’ida warinsa ya gauraye gidan gaba d’aya, ta shiga toshe hanci tana tari da k’yar....
Can ta hangi Sawwama sai rawan ‘yan bori take tanayi tana kora barasa ga ‘yan daudu na tayata mai gurmi naci gaba da aikinsa...
Hajiya ta d’aura hannaye duka biyu aka tana nishi da k’yar take furta “Na shiga uku... Na shiga uku ni Haule mai zan gani.....?!!”
***
Kana ganin Muhibbah kasan a d’auke take, Najma ta shigo tana mata kukan yunwa, wani uban tsawa data dararawa yarinyar saida ya sanyata sakin fitsari a wando... Yarinyar ta shiga jada baya jikinta na rawa... Yamutsa fuska Muhibbah take ganin fitsarin da yarinyar ta saki tana mai furta “Oh no no this isn’t happening...” Gashi Engr yasa ta rage ma’aikatan gidan a cewarsa idan tayi niyyan shiryuwa da gaske sai ta fara da kulada iyalanta...
Kira ta shiga dokawa Suwaiba wacce ita kad’ai aka bari harta Cooks d’in gidan Engr ya sallamesu...
Suwaiba ta k’araso a guje tana mai risinawa....
Muhibbah na mata nunida Najma take fad’in “Take care of her... Ta isheni da kuka.... Uban mai kike da har yanzu baki ida lunch d’in ba....?”
Suwaiba tace “Aunty aikin ne sunmin yawa... Kuma ai kaman naji Alhaji yace kece zakike abinci...”
Wani uwar harara data watsawa Suwaiba kana ta isa ta janyo kunnenta guda tace “Na maki kama da mai dafa abinci...? Answer me..!! Na maki kama da mai girki....??”
Suwaiba dake faman tamke fuska alamun taji zafin rik’on cikin sauri take girgiza kai alamun a’a....
Muhibbah ta jinjina kai tace “If you don’t want to get yourself fired toh kiyi duk wasu ayyukan da kikasan ma’aikata keyi gidan nan... Kuma Wllhi saura Engr ya dawo kice masa kece kikai abinci sai nayi d’add’aya dake... Tashi ki bani waje...”
Ta tashi da sauri tana goge hawayen da suka zubo mata... Muhibbah ta kuma kiranta tana mata nuni da Najam tace “Ki gyara wajen nan kafin na dawo....” Tana ida fad’in haka ta haye sama... Najma tai saurin rungumar Suwaiba tana kuka.... Suwaiba ta rungume yarinyar cikeda tausayawa, badon tausayin yaran ba da ganin girman Engr tabbas da tuni ta bar aikin gidan... Matace tamkar ba ‘yar Adam ba ko ma d’iyoyin wasu bazakayi irin wannan rik’on ba balle yaran da ka tsuguna ka haifesu....
Suwaiba ta d’auki yarinyar suka nufi kitchen tare tana mai lallashi had’ida jantada wasa...
Ita kaw Muhibbah tana zuwa d’aki, drawer mai d’aukeda kayan mayenta ta janyo... Ta ciro k’waya guda d’aya ta murmusheshi lokaci guda ta toshe hancinta guda ta shiga shak’a tana mai bubbuga kanta.... Saida taji kanta acan sararin samaniya kafin ta koma gefe tana hango duniyar na juye mata... Tana a haka ta jiyo k’aran shigowar motarsa... Cikin sauri ta mik’e tana k’ok’arin kimtsa kanta dukda cewa k’wayar bai saketa ba, hasalima datasan da wuri zai komo gida da bata sha ba....
Saida ta saita kanta kafin ta sauk’o k’asa....
Akram ne ya soma fitowa rik’eda jakan Engr d’in ya mik’a mata... Tai masa wani duba a yatsine kana tace ya aje a parlor ta k’arada in Engr d’in .... Akram ya bata amsada yana cikin mota...
Tsaye tai tana mamakin mai yakeyi cikin mota, nan dai ta nufi motar...
K’arar radio ta soma jiyowa cikin muryar wata mace mai dad’in sauraro yanda take furta “Toh jama’a masu saurarenmu yauma a nan zamu dasa aya... A shiri na gaba zaku jimu cikin wani sabon shirin... Kuci gaba da kasancewa damu a tasharku kuma zab’inku... A madadin mai kulada shirin da kuma abokiyar aikina tareda ni kaina Zulfa’u Usman Mailafiya muke cewa ku huta lafiya.....”
Muhibbah takai dubantaga mijinta yanda yake kishingid’e jikin car seat idanunsa a lumshe sihirtacciyar murmushi kwance saman fuskarsa....
SameenaAleeyou📚