Sashe 55
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sosai Mummy tasha jinin jikinta ganin yanayin Sameer d’in, gaba d’aya ta kasa sakin jiki dashi kaman ba Sameer d’inta ba... Ita gani tayima gaba d’aya ya canza, Sameer matashi mai yalwan fari’a da son jama’a duk ya koma wani iri, da wuya kaga murmushinsa a yanzu, haka nan magana idan ba ta zame masa dole ba bai yinta, da ace batai ma d’an nata farin sani ba sai tace canzasa akai, gaba d’aya tinda yazo zata iya k’irga maganan da ya shiga tsakaninsu....
Misalin k’arfe takwas na dare bayan an ida sallahn lisha ya shigo sashen Mummy, tuni ta fad’ad’a murmushinta dukda a b’angaren Sameer d’in ba haka bane....
“Son an shigo...” Tai maganar tana mai daidaita zamanta saman kujera...
Daga can kujeran gefe ya zauna ba tareda ya iya amsata ba sai jinjina mata kai da yai alamun eh...
Kafin Mummy ta kuma samun zarafin magana Sameer yace “Daddy fah...? I thought ya dawo gari....?” Yai maganar a tak’aice...
Mummy ta d’an dubeshi cikeda kulawa kana tace “Ya d’aga dawowarsa sai next week... Sameer wai dan Allah meke damunka... Talk to me Son...” Ta k’arashe murya cikeda damuwa...
D’ago rinannun idanunsa yai yana dubanta lokaci guda yanajin wani irin zafi da k’una cikin k’irjinsa, yana son Mummy sosai, soyayya irin wacce d’ah keyiwa mahaifiyarsa amma ace ba itace mahaifiyarsa ba bayan tsawon rayuwarsa kan hakan ya taso, ta tabbata Mummy ba itace mahaifiyarsa ba, shekaru talatin da d’oriya ita ya tashi ya gani matsayin mahaifiya a gareshi, sannan tai masa rik’o irin wanda bazai tab’a kawowa cewa ba itace ta haifeshi ba, gwanda Daddy ma wasu lokutan bai d’aukan al’amaransa da mahimmacin kaman yanda Mummy keyi....
K’uri ta masa tana jiran mai zaice ga k’irjinta dake tsananin bugawa ganin sam babu wasa a tattareda fuskarsa...
Muryarsa ta sinkayo yana fad’in “Mummy I’m going to ask you for the last time.... Mummy tell me, how am I related to you....?”
K’uri Hajiya Fatahiyya ta masa idanunta na k’ok’arin kawo ruwa kaman yanda na Sameer d’in suka ciko da ruwa....
A hankali Mummy ta taso ta dawo kujeran da Sameer ke zaune, kanta a k’asa tana goge hawayen da suka gangaro mata, a hankali ta kuma d’agowa tana dubanshi shid’inma ita yake duba....
“Sameer my Son..... Na sani duk daren dad’ewa rana irin wannan zata riskeni, ranan da zan bud’e baki na fad’a maka cewa banice na haifeka ba...!” Suk’e ajiyan zuciya Hajiya Fatahiyya tai kana taci gaba da fad’in “Amma ka sani badason raina zan sanar dakai labarinka ba saidon dole, sirrin dake rufe shekaru da dama ya tono kansa, zan sanar dakai komai amma sai kamin alk’awari zakacigaba da kasancewa d’ah a gareni....!” Ta k’arashe cikin murya irinta mai kuka wanda yasa Sameer sanda kansa k’asa zuciyarsa na tsananin masa rauni... Ya jima a haka yana jiyo sautin jan numfashin Mummy irinta mai kuka wanda hakan ke tsananin sosa masa zuciya kana yaci gaba da sauraro muryarta tana ci gaba da fad’in “Shekaru talatin baya ka zamto d’ah a garemu nida Daddynka.... A wancan lokacin ahekarunmu kusan biyar da aure nida Daddynka amma Allah bai bamu haihuwa ba, asalina mutuniyar Dutsimma ce ta jihar Katsina kaman yanda ka sani Dad d’inka mutumin asalin garin Gombe ne.... A wancan lokacin dangin mijina sunyita kwad’aitar masa cewa ya sake aure ko zai samu haihuwa amma baiyi hakan ba ko nace Allah bai k’addara ba, kullum ina cikin kuka da damuwa na rashin haihuwa alhali shi Dad d’inka sam bai nuna damuwansa akan rashin haihuwata saidaima yaita k’arfafa min gwiwa yana sanar dani idan da rabo zamu samu gaba, sannan duk abinda kaga Allah ya hana bawansa yasan dalilinsa nayin hakan, da kalaman Dad d’inka masu tausasa zuciya nakan samu natsuwa, dukda cewa sam ban tsira hannun danginsa ba wajen gori habaici da maganganun marassa dad’inji... Ana haka kwatsam watarana mahaifinka ya samu aiki garin Dutse ta jihar Jigawa, wannan shine dalilin da yasa na sami sauk’i daga tsangwaman dangin miji, muka tattara muka dawo garin Dutse da zama ba tareda mijina yayiwa danginsa sallama ba domin kuwa tinda yak’i bin shawarinsu cewa ya sake aure duk sai suka juya masa baya, babu mai shiga hidimarmu sannan babu mai gayyatarmu hidimarsa, sosai abin yayiwa Dad d’inka zafi, mahaifansa duk sun rasu balle ya masu sallama saiko dangi wad’anda suke ‘yan uba......” Hajiya Fatahiyya ta d’anja fasali kafin taci gaba da fad’in “A shekararmu ta biyu a garin Dutse kazo cikin rayuwarmu, wanda ka kasance fitilar da ya haskaka mana rayuwa, mafarin farin cikinmu snnan mabud’in alkhairanmu....” K’walla suka ci gaba da gangarowa Hajiya Fatahiyya sanda taci gaba da fad’in “Dumba....!” Sai ta kuma jan fasali tana duban Sameer d’in wanda shima ita yake duba....
Mummy ta sadda kanta k’asa a hankali tana goge hawayenta kana taci gaba da fad’in “Wata rana Dumba tazo dakai rik’e a hannunta... Kanata kuka kana ambaton Mamynka, lallashin duniya Dumba tai maka kak’iyin shiru, niko ina daga window ina hango dramarku da Dumba, tausayin k’aramin yaron ya kamani sosai, na shiga d’aki yanda nake ajiyan biscuit da alawa na sadaka ma yara don d’abi’atace tuntuni tausayin yara k’anana da kyautata masu, na d’auko maka biscuit guda na bud’e na baka, tuni ka amsa kana ci ka saki hannun Dumba ka kamo hannuna ka kwanta cikin jikina kana cin biscuit d’inka har bacci yayi gaba dakai kana kwance cikin jikina, Dumba ta sami daman tashi ta gudanar da ayyukanta domin fir kukanka ya hanata sakat....”
Cikin rawar murya Sameer ya katse Mummy da fad’in “Wacece Dumba...? Meye alak’ata da ita...?” Yai maganar hawaye na gangaro masa...
Sauk’e ajiyan zuciya Mummy tai kana taci gaba da fad’in “Zakaji komai In sha Allah Sameer...” Lokaci guda taci gaba da fad’in “Na d’aukeka na kaika bisa gado na bayan kayi baccin, na zauna daga gefe ina kallon kyakkyawar fuskarka data cika da tsoro alamun wani babban al’amari ya matuk’ar firgitaka dukda k’aranci na shekarunka...
Sanda Dumba ta ida ayyukanta nan take ce min zata d’aukeka ku tafi... Gaba d’aya Dumba ban gane mata ba a wannan ranan don da alama cikin tashin hankali take itama...
Na tsareta da idanu kana na jeho mata tambaya... Dumba shin ina kika samo yaro...?
Dumba ta shiga rarraba idanu kana tace “Hajiya rainonsa aka kawo min...”
Na dubeta sosai kana nace anya Dumba ki sanar dani gaskiya ina mahaifiyar yaron nan yake kuka irin haka... Idan bakiso na kira miki ‘yansanda tun wuri gwara ki sanar dani gaskiyar lamarin.... Dumba ta shiga rarraba idanu ganin da gaske nike saita sanar dani yanda ta samo yaro ta duk’a har k’asa tana bani hak’uri tana fad’in zan sanar dake gaskiya Hajiya...
Yaron nan rayuwarsa cikin had’ari take, yanzu haka aminai uku sun zaci ya jima a barzahu Hajiya ni kuma bazan iya kashe rai ba....
Naci gaba da dubanta da tsananin mamaki kana nace Dumba ban gane ba... So kike kicemin ked’in kwangilar kisa aka baki...?
Kan Dumba na k’asa hawaye na d’igo mata tace k’warai kuwa Hajiya amma wllhi bazan iya ba don ban tab’a kashe koda k’aramar dabba ba ballanta d’an mutum k’aramin yaro kaman wannan wanda bashida hakkin kowa, na zab’i na barshi a raye ba kaman yanda sukai zato ba... Saidai bansan yaya zanyi dashi ba bansan ina zan b’oyeshi ba nayi tunanin idan ya k’ara girma kad’an na turashi almajiranci ta chan k’asashen Chadi yanda zai b’ace daga duniyarsu har abada....
Tinda Dumba ta soma magana hawaye ke zubo min had’ida tsananin tausayinka....” Mummy ta sauk’e ajiyan zuciya kana taci gaba da fad’in “Sameer ni na buk’aci Dumba ta barmin rik’onka a hannuna, aka kuwayi sa’a da maigidana ya dawo ya taddaka taredani gwanin ban sha’awa yanda ka sake dani kana amsan abincin daga hannuna, yayita mamakin ina na samo yaro nan na zayyane masa komai, shid’inma tausayinka ne tsantsan ya kamashi amma sai yace bazamu bi maganar Dumba haka kurum ba gwara mubi diddigi muji ina ta samo yaron nan don kardai ma sato shi tayi mutum a yau abin tsoro ne, watak’ila dangin yaron nan iyayensa nata nemansa wata k’ila ‘yansanda ke neman Dumba ta shirya wannan labari, nabi shawarin mijina washe gari muka tafi gidan wacce ta samo mana Dumba matsayin ‘yar aiki saidai bamu sami labari mai dad’i ba domin kuwa ita kanta dillanci masu aiki take sannan ta sanar damu ita kanta batasan ina zata samu Dumba ba, nan na soma yarda da maganganun mijina, wata k’ila Dumba mugun nufi ne tattare da ita, neman duniya munyi bamu sami Dumba ba gashi batako sanar damu sunanka ba, nida mijina muka yanke shawarin kiranka da suna Sameer, da fari Dad d’inka yaso a damk’a ka hannun hukuma ko cibiyar kulada marayu amma fir nak’i hakan nace nidai Allah ne ya bani d’ah daga sama, a dole ya amince da buk’atata muka rik’eka matsayin d’anmu, a wannan lokacin Dad d’inka ya sami aiki a jami’ar Amurka muka d’unguma muka nufi gida Gombe donyi masu sallama sunyita mamakin ganin mu da yaro kasancewar mun d’au shekaru ba tareda sunsan yanda muke ba hakan yasa sukai zaton ko haihuwa nayi wasu sukai ta cewa k’ila da ciki na tafi kenan, masu mana murna suka mana masu nuna bak’in cikinsu sukai, nan dai muka sanar masu sallama mukazo yi masu zamu koma k’asar Amurka da zama na wasu lokuta, duk duniyar nan bayan Dumba da bamusan yanda zamu sameta ba saiko aminiyata Farida su kad’aine sukasan cewa bamu ne muka haifeka ba.....!” Mummy ta k’arashe tana matse k’walla da bakin zaninta...
Yayinda Sameer kansa ke k’asa hawaye naci gaba da gangaro masa tambayoyi da dama suna neman tarwatsa masa kwanya...
Misalin k’arfe takwas na dare bayan an ida sallahn lisha ya shigo sashen Mummy, tuni ta fad’ad’a murmushinta dukda a b’angaren Sameer d’in ba haka bane....
“Son an shigo...” Tai maganar tana mai daidaita zamanta saman kujera...
Daga can kujeran gefe ya zauna ba tareda ya iya amsata ba sai jinjina mata kai da yai alamun eh...
Kafin Mummy ta kuma samun zarafin magana Sameer yace “Daddy fah...? I thought ya dawo gari....?” Yai maganar a tak’aice...
Mummy ta d’an dubeshi cikeda kulawa kana tace “Ya d’aga dawowarsa sai next week... Sameer wai dan Allah meke damunka... Talk to me Son...” Ta k’arashe murya cikeda damuwa...
D’ago rinannun idanunsa yai yana dubanta lokaci guda yanajin wani irin zafi da k’una cikin k’irjinsa, yana son Mummy sosai, soyayya irin wacce d’ah keyiwa mahaifiyarsa amma ace ba itace mahaifiyarsa ba bayan tsawon rayuwarsa kan hakan ya taso, ta tabbata Mummy ba itace mahaifiyarsa ba, shekaru talatin da d’oriya ita ya tashi ya gani matsayin mahaifiya a gareshi, sannan tai masa rik’o irin wanda bazai tab’a kawowa cewa ba itace ta haifeshi ba, gwanda Daddy ma wasu lokutan bai d’aukan al’amaransa da mahimmacin kaman yanda Mummy keyi....
K’uri ta masa tana jiran mai zaice ga k’irjinta dake tsananin bugawa ganin sam babu wasa a tattareda fuskarsa...
Muryarsa ta sinkayo yana fad’in “Mummy I’m going to ask you for the last time.... Mummy tell me, how am I related to you....?”
K’uri Hajiya Fatahiyya ta masa idanunta na k’ok’arin kawo ruwa kaman yanda na Sameer d’in suka ciko da ruwa....
A hankali Mummy ta taso ta dawo kujeran da Sameer ke zaune, kanta a k’asa tana goge hawayen da suka gangaro mata, a hankali ta kuma d’agowa tana dubanshi shid’inma ita yake duba....
“Sameer my Son..... Na sani duk daren dad’ewa rana irin wannan zata riskeni, ranan da zan bud’e baki na fad’a maka cewa banice na haifeka ba...!” Suk’e ajiyan zuciya Hajiya Fatahiyya tai kana taci gaba da fad’in “Amma ka sani badason raina zan sanar dakai labarinka ba saidon dole, sirrin dake rufe shekaru da dama ya tono kansa, zan sanar dakai komai amma sai kamin alk’awari zakacigaba da kasancewa d’ah a gareni....!” Ta k’arashe cikin murya irinta mai kuka wanda yasa Sameer sanda kansa k’asa zuciyarsa na tsananin masa rauni... Ya jima a haka yana jiyo sautin jan numfashin Mummy irinta mai kuka wanda hakan ke tsananin sosa masa zuciya kana yaci gaba da sauraro muryarta tana ci gaba da fad’in “Shekaru talatin baya ka zamto d’ah a garemu nida Daddynka.... A wancan lokacin ahekarunmu kusan biyar da aure nida Daddynka amma Allah bai bamu haihuwa ba, asalina mutuniyar Dutsimma ce ta jihar Katsina kaman yanda ka sani Dad d’inka mutumin asalin garin Gombe ne.... A wancan lokacin dangin mijina sunyita kwad’aitar masa cewa ya sake aure ko zai samu haihuwa amma baiyi hakan ba ko nace Allah bai k’addara ba, kullum ina cikin kuka da damuwa na rashin haihuwa alhali shi Dad d’inka sam bai nuna damuwansa akan rashin haihuwata saidaima yaita k’arfafa min gwiwa yana sanar dani idan da rabo zamu samu gaba, sannan duk abinda kaga Allah ya hana bawansa yasan dalilinsa nayin hakan, da kalaman Dad d’inka masu tausasa zuciya nakan samu natsuwa, dukda cewa sam ban tsira hannun danginsa ba wajen gori habaici da maganganun marassa dad’inji... Ana haka kwatsam watarana mahaifinka ya samu aiki garin Dutse ta jihar Jigawa, wannan shine dalilin da yasa na sami sauk’i daga tsangwaman dangin miji, muka tattara muka dawo garin Dutse da zama ba tareda mijina yayiwa danginsa sallama ba domin kuwa tinda yak’i bin shawarinsu cewa ya sake aure duk sai suka juya masa baya, babu mai shiga hidimarmu sannan babu mai gayyatarmu hidimarsa, sosai abin yayiwa Dad d’inka zafi, mahaifansa duk sun rasu balle ya masu sallama saiko dangi wad’anda suke ‘yan uba......” Hajiya Fatahiyya ta d’anja fasali kafin taci gaba da fad’in “A shekararmu ta biyu a garin Dutse kazo cikin rayuwarmu, wanda ka kasance fitilar da ya haskaka mana rayuwa, mafarin farin cikinmu snnan mabud’in alkhairanmu....” K’walla suka ci gaba da gangarowa Hajiya Fatahiyya sanda taci gaba da fad’in “Dumba....!” Sai ta kuma jan fasali tana duban Sameer d’in wanda shima ita yake duba....
Mummy ta sadda kanta k’asa a hankali tana goge hawayenta kana taci gaba da fad’in “Wata rana Dumba tazo dakai rik’e a hannunta... Kanata kuka kana ambaton Mamynka, lallashin duniya Dumba tai maka kak’iyin shiru, niko ina daga window ina hango dramarku da Dumba, tausayin k’aramin yaron ya kamani sosai, na shiga d’aki yanda nake ajiyan biscuit da alawa na sadaka ma yara don d’abi’atace tuntuni tausayin yara k’anana da kyautata masu, na d’auko maka biscuit guda na bud’e na baka, tuni ka amsa kana ci ka saki hannun Dumba ka kamo hannuna ka kwanta cikin jikina kana cin biscuit d’inka har bacci yayi gaba dakai kana kwance cikin jikina, Dumba ta sami daman tashi ta gudanar da ayyukanta domin fir kukanka ya hanata sakat....”
Cikin rawar murya Sameer ya katse Mummy da fad’in “Wacece Dumba...? Meye alak’ata da ita...?” Yai maganar hawaye na gangaro masa...
Sauk’e ajiyan zuciya Mummy tai kana taci gaba da fad’in “Zakaji komai In sha Allah Sameer...” Lokaci guda taci gaba da fad’in “Na d’aukeka na kaika bisa gado na bayan kayi baccin, na zauna daga gefe ina kallon kyakkyawar fuskarka data cika da tsoro alamun wani babban al’amari ya matuk’ar firgitaka dukda k’aranci na shekarunka...
Sanda Dumba ta ida ayyukanta nan take ce min zata d’aukeka ku tafi... Gaba d’aya Dumba ban gane mata ba a wannan ranan don da alama cikin tashin hankali take itama...
Na tsareta da idanu kana na jeho mata tambaya... Dumba shin ina kika samo yaro...?
Dumba ta shiga rarraba idanu kana tace “Hajiya rainonsa aka kawo min...”
Na dubeta sosai kana nace anya Dumba ki sanar dani gaskiya ina mahaifiyar yaron nan yake kuka irin haka... Idan bakiso na kira miki ‘yansanda tun wuri gwara ki sanar dani gaskiyar lamarin.... Dumba ta shiga rarraba idanu ganin da gaske nike saita sanar dani yanda ta samo yaro ta duk’a har k’asa tana bani hak’uri tana fad’in zan sanar dake gaskiya Hajiya...
Yaron nan rayuwarsa cikin had’ari take, yanzu haka aminai uku sun zaci ya jima a barzahu Hajiya ni kuma bazan iya kashe rai ba....
Naci gaba da dubanta da tsananin mamaki kana nace Dumba ban gane ba... So kike kicemin ked’in kwangilar kisa aka baki...?
Kan Dumba na k’asa hawaye na d’igo mata tace k’warai kuwa Hajiya amma wllhi bazan iya ba don ban tab’a kashe koda k’aramar dabba ba ballanta d’an mutum k’aramin yaro kaman wannan wanda bashida hakkin kowa, na zab’i na barshi a raye ba kaman yanda sukai zato ba... Saidai bansan yaya zanyi dashi ba bansan ina zan b’oyeshi ba nayi tunanin idan ya k’ara girma kad’an na turashi almajiranci ta chan k’asashen Chadi yanda zai b’ace daga duniyarsu har abada....
Tinda Dumba ta soma magana hawaye ke zubo min had’ida tsananin tausayinka....” Mummy ta sauk’e ajiyan zuciya kana taci gaba da fad’in “Sameer ni na buk’aci Dumba ta barmin rik’onka a hannuna, aka kuwayi sa’a da maigidana ya dawo ya taddaka taredani gwanin ban sha’awa yanda ka sake dani kana amsan abincin daga hannuna, yayita mamakin ina na samo yaro nan na zayyane masa komai, shid’inma tausayinka ne tsantsan ya kamashi amma sai yace bazamu bi maganar Dumba haka kurum ba gwara mubi diddigi muji ina ta samo yaron nan don kardai ma sato shi tayi mutum a yau abin tsoro ne, watak’ila dangin yaron nan iyayensa nata nemansa wata k’ila ‘yansanda ke neman Dumba ta shirya wannan labari, nabi shawarin mijina washe gari muka tafi gidan wacce ta samo mana Dumba matsayin ‘yar aiki saidai bamu sami labari mai dad’i ba domin kuwa ita kanta dillanci masu aiki take sannan ta sanar damu ita kanta batasan ina zata samu Dumba ba, nan na soma yarda da maganganun mijina, wata k’ila Dumba mugun nufi ne tattare da ita, neman duniya munyi bamu sami Dumba ba gashi batako sanar damu sunanka ba, nida mijina muka yanke shawarin kiranka da suna Sameer, da fari Dad d’inka yaso a damk’a ka hannun hukuma ko cibiyar kulada marayu amma fir nak’i hakan nace nidai Allah ne ya bani d’ah daga sama, a dole ya amince da buk’atata muka rik’eka matsayin d’anmu, a wannan lokacin Dad d’inka ya sami aiki a jami’ar Amurka muka d’unguma muka nufi gida Gombe donyi masu sallama sunyita mamakin ganin mu da yaro kasancewar mun d’au shekaru ba tareda sunsan yanda muke ba hakan yasa sukai zaton ko haihuwa nayi wasu sukai ta cewa k’ila da ciki na tafi kenan, masu mana murna suka mana masu nuna bak’in cikinsu sukai, nan dai muka sanar masu sallama mukazo yi masu zamu koma k’asar Amurka da zama na wasu lokuta, duk duniyar nan bayan Dumba da bamusan yanda zamu sameta ba saiko aminiyata Farida su kad’aine sukasan cewa bamu ne muka haifeka ba.....!” Mummy ta k’arashe tana matse k’walla da bakin zaninta...
Yayinda Sameer kansa ke k’asa hawaye naci gaba da gangaro masa tambayoyi da dama suna neman tarwatsa masa kwanya...