← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 101 OF 198

Sashe 101

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Abbah yace “Naji wannan, matarka kuma fah...? Kasan da zuwanta baka sanar damu ba....?”
Sameer ya ware idanunsa a hankali “Abbah matata kuma...? Kana nufin Siyama tazo gida....?”
Daga d’aya b’angaren Abbah yace “Baka san da zuwan nata ba kenan....?”
Sam baiso iyayensa su fahimci wane irin zama suke da Siyama, k’ok’arin saita kansa yai kana yace “Oh...Har ta iso kenan... Kuyi hak’uri Abbah ban kawo maku ita da kaina ba amma gani a hanya in sha Allah....” Daga haka sallama sukai da Abban yana mai duban Mamy da tai jigum tana jiran ya ida wayar....
Mamy tace “Asibiti yake koh....?”
Jinjina mata kai kurum Abbah yai kana yace “Mariya akwai abinda na fahimta a rayuwar auren yaron nan.... Kaman auren nasa cike yake da tarin matsaloli....”
Ajiyan zuciya Mamy ta sauk’e a hankali “Nima nayi tunanin hakan tin sanda nai ido biyu da iyalin nasa, kuma bai kawo mana ita duk tsawon lokacin nan ba... Nayi tunanin na tambayesa sai kuma naga ba hurumina bane...”
Jinjina kai Abbah yai a hankali kana yace “Wannan hakan matsalarsu tasu ne, ina fata su zamto masu warware matsalolinsu da kawunansu basai wani yaji ba...”
Ta jinjina kai ba tareda ta furta komai ba sai nazarin abin da take....

***

Tsare Akram tai sosai da manyan idanunta tanai masa kallon tuhuma,lokaci guda kuma ta saki murmushi ta mik’e ta nufo yanda yake.... Gefe dashi ta zauna tana wani karkad’a jiki murmushi bai bar saman fuskarta ba....
“Akram I’m a business woman, sanin kanka ne ban dogara da dukiyar da mijina keda ita ba, inada tawa dukiyar.... Kuma ina mai tabbatar maka I can make you what your boss fails to make you.... Idanma baka son wannan I can offer you something more than that.....” Ta k’arashe tana kashe murya had’ida kashe masa idanu guda....
Mik’ewa tsaye yai yana mai murmusawa da gefen bakinsa kana yace “Duk ba sai kinyi wad’annan ba Hajiya, never bazan tab’a cin amanan Excellency irin haka ba, but rest assure auren da mijinki yake nema bazai tab’a yuwa ba.... Here is my plan....” Ziryan ziryan ya zayyano mata yanda abin zai kasance.....

Ta saki murmushin jin dad’i kana tace “Who’s she... who’s the girl, sanar dani...”
Nanma murmushin yai da gefen bakinsa kana yace “Sanin ko wacece ita to you is not necessary, just trust me, auren bazai tabbata ba....”

Mik’e k’afa guda tai tana mai ci gaba da kad’a k’afar tata take furta “And I’m ever ready to support you financially, duk wani abinda ake buk’ata daga lefe zuwa sadaki zan baka kai har gidan da zaka ajeta ni nan zan baka....”

Nanma dai murmushin yai kana yace “Karki damu Hajiya I’ve everything under control, idan bazaki damu ba ni zan wuce....” Ya k’arashe yana mai mik’ewa tsaye....
Muhibbah ta kuma sakin shu’umar murmushi kana tace “Naji dad’i da muka kasance on the same page.... And let me remind you this, ka tabbata ka cika alk’awarinka idan ba haka ba, you’ll both lose her daga kai har boss d’in naka... Coz when it comes to my husband I can be very dangerous.....” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta...
Shid’inma murmushin yake kafin ya d’an tako gabanta kad’an, murmushin bai gushe saman fuskarsa ba hannayensa sakale cikin aljihun wandonsa na jampa yake furta “You don’t want to have me as an enemy, coz I can expose your little secret... I know exactly the kind of business you run.... So idan baki so mijinki yasan musabbabin yawon k’asashen da matarsa keyi da sunan business trips, kada ki kuskura ki shiga hurumin Zulfa’u...”

Zaro idanu waje tai tana dubansa da tsananin mamaki, ta had’iyi miyau da k’yar don batai tsammanin Akram zai iya sanin wannan sirri nata da ko danginta basu sani ba...
Bai daina murmushin ba ya furta “Just a piece of advice, do not double cross me...” Daga haka sa kai yai ya fice daga parlorn cikin sauri.....

Muhibbah ta sauk’e huci mai zafi ga kanta da ya d’auki chaji lokaci guda... Cikin sauri ta haura sama ta nufi drawer d’inta ta d’auko k’wayar had’ida tsura masa idanu... Lokaci guda ta shiga b’allewa tamkar zararriya haka ta shiga afawa a baki, saida ta afawa kusan hud’u lokaci guda kafin ta zube saman gado had’ida lumshe idanunta....

***

Daga bakin k’ofa yaja ya tsaya ganin har Sawwama ta dawo gidan, hularsa a karkace ya hard’e hannaye k’irji had’ida jinginuwa jikin k’ofar yana k’are mata kallo, kana ganinshi kasan yau a Hafiz d’insa ya fito....
Sawwama dake faman goge kayan kallo sam bataji motsin shigowarsa ba har saida ta mik’e zata nufi d’aki nan ta ganshi k’ik’am tsaye akanta ya kafeta da idanunsa masu sumar da ita....
Sosai ya mata kyau don tayi kewarsa sosai, tai saurin mik’ewa ta nufesa tana mai furta “Hafizina bansan kana tafe ba da na girka maka wani abin.... Muje ka kwanta ka huta yanzu zan shiga kitchen na dafo maka abinci mai sauk’i, kar ka damu Magajiya ta had’oni da duk wani abin buk’ata....” Kasa k’arashe maganan nata tai jin ko motsasa daga yanda yake ta kasa... Ta d’ago tana dubansa da mamaki, ta d’an saki murmushi kad’an....
“Lafiya dai Hafizina...?”

“Uwarki ne ba lafiya...”
Kalmar data sinkaya kenan daga bakin Hafiz, gabanta ya yanke ya fad’i... Sai yanzu ta tuna babu wani shirin asiri data dawo dashi gidan.....
Ta saki murmushin yak’e “Haba Hafizina na riga na baka hak’uri, nasan muna son junanmu.... Mu baiwa maras d’a kunya muci gaba da zaman aurenmu, nai maka alk’awarin duk wasu abubuwa marassa kyau da nake a baya na dainasu daga yanzu, zan kula dakai yanda baka tsammani Hafizina....” Ta k’arashe tana marairaicewa.....
Tamkar wanda ya tina wani abin ya murmusa da gefen bakinsa, ta gefenta ya rab’a ya shige cikin d’ajin yana wani faman k’obarewa.....
Sawwama ta bisa da kallo dikda cewa tasha jinin jikinta da ganin yanayin Hafiz d’in.......

***
Chapter 101 · 0% Book details