Sashe 10
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nabila ta dafe k’uncinta tana duban Mamy da Zulfah dake faman surfa mata fad’a kan rashin kunyar data kuma b’ullo dashi a ‘yan kwanakin... Kuka Nabilah keyi tana fad’in “Wllhi Mamy Allah baku kyautawa, ita fah Addah tsoron Yaya Hafiz take sai ta tsaya yana mata cin kashi da cin mutunci, Mamy bakiji abinda ya gama fad’iwa Abbah ai na lab’e bakin k’ofa naji komai, wllhi Mamy wulak’ancin da yayiwa Addah kare bazaici ba, ko shine autan maza sai taci gaba da zama dashi.. Idan Abbah yace zata bar masa gida babu gidansu Aunty B ne babu gidajen danginki ne Mamy, ina aka tab’a aure da cin zarafi.....”.
Zulfah ta katseta cikin daka tsawa “Babu ruwanki da rayuwar auren da nake sannan Ya Hafiz ba sa’anki bane da zaki masa rashin kunya da rashin mutunci, idan kullum muzguna mun yake babu ruwanki ban buk’atan damuwarki cikin rayuwar aurena kinjini koh....” Ta k’arashe hawaye na gangaro mata...
Su duka biyun hawaye suke daga ita har Nabilan da bata daina hawayen takaici ba....
Zulfah taci gaba da fad’in “Allah na gani bai mance dani ba, sannan shi ya k’addara min wannan aure, kuma bana fata na zamto sanadiyan tashin hankalin Abbah... Inda rai da rabon wata rana Allah zai ya sarremun lamurana nayi imani zai sauk’ak’a min ta yanda banyi zato ba banyi tsammani ba kinji koh Sister... So please na rok’eki stop meddling, ki daina shiga kinji, wata matsalar kurum zaki kuma haifar mun.....” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya...
Rungumeta Nabila tayi su duka suna hawaye mai ban tausayi, Mamy tasa bayan hannu ta goge hawayen da suka zubo mata kafin ta shiga tsakaninsu ta janyosu suka nufi d’aki Mamy na rungume da kafad’ar ko waccensu....
Nasiha ta kuma yimasu gameda rayuwar duniya da matsayi da kuma ribar hak’uri, gaba d’aya yaran nata ta had’e ta masu nasiha harmada Marliya wacce take autarsu... Bayan magrib Mamy da Aunty Lami suka kuma tausar Zulfah suka umarceta da ta koma d’akinta kafin Abbah ya dawo gida ya taddata...
Aunty Lami ita tayimata rakiya har d’akinta ta kuma bata baki da nasihan hak’urin zama da miji musamman irin nata mijin... Sosai Zulfah taji dad’in shawarwarin Aunty Lami harda tayata daura abinci kafin ta wuce gida da shike ba itace da girki ba Mamy ce....
***
Bai tashi dawowa gidan ba sai wajajen 11:30pm lokacin har ta soma gyangyad’i a parlor wai donma tana kallon shirin fina finanfinan India da ake nunawa a tashan mbc bollywood....
Baiji mamakin ganinta ba don yasan zata dawo... Ya jima yana tsaye yana k’are mata kallon wulak’anci kafin ya daka mata wani uban tsawan datajisa uwa a mafarki...
“Ke!!! Ba cewa nayi kije gida ba sai na nemeki, mai kuma ya dawo dake....?”
Baccin da takeji ya watse itakam halin nasa ya daina bata mamaki saima tsoro...
Gyara kwanciyarta tayi kana tace “Wanda ka kai masa k’ara ne yace na dawo sanin kanka darajarsa kake ci nake zaune gidanka...” Daga haka juyawa tayi ta basa baya
Yayi k’wafa had’ida jinjina kai kafin ya fad’a d’aki, tana jinyo sanda yayiwa k’ofar sakata...
Tayi k’ok’arin danne k’uncinta tana duban sashen da abincinsa ke ajiye, a hankali ta gyara kwanciyarta had’ida lumshe idanu dukda baccin ya k’aurace mata...
A haka rayuwa taci gaba da wakana, a b’angaren su Sameer kuwa ana gobe zai taho Kano kusan kwana Siyama tayi tana zuba masa shagwab’a, gaba d’aya saiji tafiyar ta fice a ransa, ji yayi tamkar ya rubuta resignation letter ya zauna da Partner d’insa amma taimakon al’umma na d’aya daga cikin manyan burikansa na rayuwa....
Washe gari ma da k’yar suka rabu da juna yanda kasan wata uwa duniya zai tafi....
K’uri Sultan ya masu sanda Sameer ya kuma kirawo sunanta “Partner..!”
Juyowa tayi tana dubansa kana tace “Ka mance wani abu...?”
Saida ya d’ibi wasu dak’ik’ai yana dubanta kana ya kashe mata idanu guda kafin yace “I love you....”
Murmusawa tayi sannan tace “I know Partner... Drive safe....!” Ta k’arashe tana cuno masa baki gaba alamun kiss....
Kaman kar ya daina dubanta haka yakeji, shi kuwa Sultan dake zaune gaban motan idan ransa yayi dubu ya b’aci kai kace akansu aka soma soyayya, saikace wanda zasu shafe watanni ba tareda sunga juna ba sannan ya tabbata daren jiya kwana sukayi suna abu guda.... Cikeda takaici ya ciro wayarsa a aljihu yana shafawa....
Jiki a sanyaye Siyama ta dawo cikin gidan sai tanaji gaba d’aya ya mata girma, tsayuwa tayi gefen madubin console tana duban hotonsu dake cikin k’aramar frame a hankali tayi murmushi tana shafawa kana tace “Allah ya kaimun kai lafiya Partner.....”
Da dare tayima gaba d’aya sai taji babu dad’i, ta bud’e closet d’insu tana tunanin kayan baccin da zata saka, da ace yana nan k’ila da wannan zai zab’a mata, ko kuma wancan... Haka tayita tunani ko wanne ta d’auko sai ta mayar tana tunanin bashine Partner zai zab’a mata ta saka ba, gaba d’aya sai taji sabon tashin hankalin rashinsa na taso mata... haka nan a kitchen ma ta gama galantoyinta tana tunanin mai zataci, da ace Partenr na nan da ya dafa masu abinci mai sauk’i idan basuyi order ba....
K’walla suka ciko idanun Siyama sanda ta kwanta bisa gadonsu taji gadon ya mata fad’i.... Can k’arshen gado ta tak’ure had’ida rungume pillow hawaye na gangaro mata tsananin kewar mijinta na addabarta, ta mastu gari ya waye ta fice office ko zataji sanyi koda kuwa zata had’u da Khalid ne suyi fad’a...
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*10*
Washe gari daga office koda ta dawo gida wasu ‘yan kayayyakinta ta had’a cikin k’aramar akwati kafin ta d’auki hanyar gidansu...,Kallo guda zaka mata ka fahimci tsan tsan damuwar dake tattareda ita..
Babu kowa a parlorn sai k’aran alarm ta dafuwar oxtail dake tashi daga kitchen, mik’ewa tayi saman sofa ta d’an kishingid’a had’ida lumshe idanunta, tanajin sanda Malam Sallau ya shigo da suitcase d’inta ya ajiye daga bayan parlorn yana mai fad’in “Hajiya ga jakar a nan...”
Ko zarafin amsashi Siyama bata samu ba har lokacin idanunta a lumshe suke, wasu irin tunani marassa kangado masu tada hankali su suka addabeta, yanzu idan Partner ya kasa jure rashinta kusanshi fah? Idan ya fad’a wata rayuwar fah..? Ko kuma idan yace zai k’ara aure fah... Shin waima da wasu irin mutane zaike huld’a....?” Ire iren tunanin dake zuwa zuciyarta kenan har Kubura mai aikin Ammi ta shigo parlorn Siyama bataji shigowarta ba...
Turus Kuburan tayi tana duban Siyama dake kwance saman sofa idanu a lumshe ko takalmin k’afarta bata samu zarafin cirewa ba dashike d’aure yake da belt...
Kubura ta kuma juyawa ta kalli akwati a gefe... D’an k’arasowa ta shigayi cikeda risinawa tana kiran Siyama...
“Aunty..! Aunty..!!!..” Shiru Siyama bata amsa ba...
Saida Kubura ta d’an buga kujeran kad’an tana k’ara fad’in “Aunty....”
Sai sannan Siyama ta bud’e idanunta had’ida d’an yamutsa fuska...
“Aunty lafiya kuwa...?” Kubura ta tambaya...
A kaikaice Siyama ta dubeta fuska babu walwala kana tace “Banson gulmarku ta masu aiki d’auki jakata ki haura min da ita sama d’akina...”
Kubura ta jinjina kai tana fad’in “A’a wai Aunty gani nayi kaman bakida lafiya shiyasa na tambaya....”
Gajeren tsaki Siyama tayi don ta tsani shiga sharo babu shanu irinta ma’aikatan gidan Ammi musamman Kubura, kallon data watsa mata yasa bata kuma cewa komai ba ta ciccib’i jakan tana washe hak’wara don ko babu komai zatake samun na kashewa don Siyama akwai sake hannu shiyasa duk ma’aikatan gidan ke bata girma kama daga masu gadi har ma’aikatan cikin gidan itadai barta da basarwa wanda usulin d’abi’artace miskilace ta gaske ba kasafai take shiga hark’an mutane ba shiyasa ko k’awaye basufi a k’irga ba wanda takedasu, tanada zafin rai abu k’ank’ani ke b’ata mata rai hakan yasa duk wanda yasanta yake shan maganin zama da ita... Da yawan mutane sukan d’auketa mace mai gadara da isa da ji da kai wasu kuwa kan d’auki hakan da cewa goyon data samu ne na sangarci daga gidansu... Idan kaji hayaniyar Siyama toh fah ka tabbata Khalid ne ya tab’ata shiyasa mahaifinta ya d’auki muk’ami mai girma a kampaninsa ya damk’a mata....
Ammy dake zarya cikin makeken d’akinta tana waya nan ta hangi Kubura da jaka nik’inik’i tana haurowa zata shige d’akin Siyama... A’a mamaki ya kama Ammy cikin sauri ta katse wayar da take kana ta tsare Kubura da fad’in “Ke ke yaya wannan fah...? Daga ina....?”
Kubura na haki take fad’in “Ammy Aunty Siyama ce tazo tana parlorn k’asa tana kwance, Ammy inaji dai babu lafiya ne don baki ganta ba gaskiya.....”
“Ke ya isheni bani hanya na wuce....” Ammy ta katseta sanda take sauk’owa daga bene cikin tsananin tashin hankali....
Kwance ta hangi Siyama har lokacin.... Cikin sauri Ammy ta k’arasa gareta.....
****
Kallon juna sukayi a karo na biyu kafin suka kuma tafe hannaye suna shewa irinta aminan asali, Hajiya taci gaba da juya super wax d’in dake hannunta kana tace “Ke Lami bakida kyau kin rantse sai kin mallaki tsohuwar nan...”
Aunty Lami ta kuma juya idanu kana tace “Ai idan sunsan wata basu san wata ba, nid’in nan dai da a baya aka ambata da juya mujiya merere wanere sai an dawo ana bina tako ina... Sai na zamto almiski duk yanda na shiga na bar k’amshina....”
Hajiya rik’e da hab’a take duban Aunty Lami kana suka kuma saka shewa, Hajiyar Hafiz tace ya labarin aminyar sirri....?”
A tare suka kwashe da dariya kana Aunty Lami tace “Zancen kike nema bara kiga na tashi na tafi kafin Abbah ya dawo daga kasuwa don yau zai komo d’akina gwara naje na masa shiri tinda ita wancan bataga kwanciyar hankalin ba ma ballanta ta tsaya kulada miji....” Ta k’arashe maganar tana tura zanin cikin bak’ar leda....
Hajiya ta mik’e tana gyara d’aurin zani take fad’in “Ai ni babban abinda kemin dad’i shine yanda Mamani ke matuk’ar k’aunar Hafiz sam bata ganin laifinsa idan kuwa baki mance ba a baya itace dai tak’i jinin d’ana ta d’auki son duniya ta d’aura kan Ma’aruf yaronda sam ashe ba mai zama bane k’ashinsa ya jima da daddagewa cikin k’asa....”
Zulfah ta katseta cikin daka tsawa “Babu ruwanki da rayuwar auren da nake sannan Ya Hafiz ba sa’anki bane da zaki masa rashin kunya da rashin mutunci, idan kullum muzguna mun yake babu ruwanki ban buk’atan damuwarki cikin rayuwar aurena kinjini koh....” Ta k’arashe hawaye na gangaro mata...
Su duka biyun hawaye suke daga ita har Nabilan da bata daina hawayen takaici ba....
Zulfah taci gaba da fad’in “Allah na gani bai mance dani ba, sannan shi ya k’addara min wannan aure, kuma bana fata na zamto sanadiyan tashin hankalin Abbah... Inda rai da rabon wata rana Allah zai ya sarremun lamurana nayi imani zai sauk’ak’a min ta yanda banyi zato ba banyi tsammani ba kinji koh Sister... So please na rok’eki stop meddling, ki daina shiga kinji, wata matsalar kurum zaki kuma haifar mun.....” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya...
Rungumeta Nabila tayi su duka suna hawaye mai ban tausayi, Mamy tasa bayan hannu ta goge hawayen da suka zubo mata kafin ta shiga tsakaninsu ta janyosu suka nufi d’aki Mamy na rungume da kafad’ar ko waccensu....
Nasiha ta kuma yimasu gameda rayuwar duniya da matsayi da kuma ribar hak’uri, gaba d’aya yaran nata ta had’e ta masu nasiha harmada Marliya wacce take autarsu... Bayan magrib Mamy da Aunty Lami suka kuma tausar Zulfah suka umarceta da ta koma d’akinta kafin Abbah ya dawo gida ya taddata...
Aunty Lami ita tayimata rakiya har d’akinta ta kuma bata baki da nasihan hak’urin zama da miji musamman irin nata mijin... Sosai Zulfah taji dad’in shawarwarin Aunty Lami harda tayata daura abinci kafin ta wuce gida da shike ba itace da girki ba Mamy ce....
***
Bai tashi dawowa gidan ba sai wajajen 11:30pm lokacin har ta soma gyangyad’i a parlor wai donma tana kallon shirin fina finanfinan India da ake nunawa a tashan mbc bollywood....
Baiji mamakin ganinta ba don yasan zata dawo... Ya jima yana tsaye yana k’are mata kallon wulak’anci kafin ya daka mata wani uban tsawan datajisa uwa a mafarki...
“Ke!!! Ba cewa nayi kije gida ba sai na nemeki, mai kuma ya dawo dake....?”
Baccin da takeji ya watse itakam halin nasa ya daina bata mamaki saima tsoro...
Gyara kwanciyarta tayi kana tace “Wanda ka kai masa k’ara ne yace na dawo sanin kanka darajarsa kake ci nake zaune gidanka...” Daga haka juyawa tayi ta basa baya
Yayi k’wafa had’ida jinjina kai kafin ya fad’a d’aki, tana jinyo sanda yayiwa k’ofar sakata...
Tayi k’ok’arin danne k’uncinta tana duban sashen da abincinsa ke ajiye, a hankali ta gyara kwanciyarta had’ida lumshe idanu dukda baccin ya k’aurace mata...
A haka rayuwa taci gaba da wakana, a b’angaren su Sameer kuwa ana gobe zai taho Kano kusan kwana Siyama tayi tana zuba masa shagwab’a, gaba d’aya saiji tafiyar ta fice a ransa, ji yayi tamkar ya rubuta resignation letter ya zauna da Partner d’insa amma taimakon al’umma na d’aya daga cikin manyan burikansa na rayuwa....
Washe gari ma da k’yar suka rabu da juna yanda kasan wata uwa duniya zai tafi....
K’uri Sultan ya masu sanda Sameer ya kuma kirawo sunanta “Partner..!”
Juyowa tayi tana dubansa kana tace “Ka mance wani abu...?”
Saida ya d’ibi wasu dak’ik’ai yana dubanta kana ya kashe mata idanu guda kafin yace “I love you....”
Murmusawa tayi sannan tace “I know Partner... Drive safe....!” Ta k’arashe tana cuno masa baki gaba alamun kiss....
Kaman kar ya daina dubanta haka yakeji, shi kuwa Sultan dake zaune gaban motan idan ransa yayi dubu ya b’aci kai kace akansu aka soma soyayya, saikace wanda zasu shafe watanni ba tareda sunga juna ba sannan ya tabbata daren jiya kwana sukayi suna abu guda.... Cikeda takaici ya ciro wayarsa a aljihu yana shafawa....
Jiki a sanyaye Siyama ta dawo cikin gidan sai tanaji gaba d’aya ya mata girma, tsayuwa tayi gefen madubin console tana duban hotonsu dake cikin k’aramar frame a hankali tayi murmushi tana shafawa kana tace “Allah ya kaimun kai lafiya Partner.....”
Da dare tayima gaba d’aya sai taji babu dad’i, ta bud’e closet d’insu tana tunanin kayan baccin da zata saka, da ace yana nan k’ila da wannan zai zab’a mata, ko kuma wancan... Haka tayita tunani ko wanne ta d’auko sai ta mayar tana tunanin bashine Partner zai zab’a mata ta saka ba, gaba d’aya sai taji sabon tashin hankalin rashinsa na taso mata... haka nan a kitchen ma ta gama galantoyinta tana tunanin mai zataci, da ace Partenr na nan da ya dafa masu abinci mai sauk’i idan basuyi order ba....
K’walla suka ciko idanun Siyama sanda ta kwanta bisa gadonsu taji gadon ya mata fad’i.... Can k’arshen gado ta tak’ure had’ida rungume pillow hawaye na gangaro mata tsananin kewar mijinta na addabarta, ta mastu gari ya waye ta fice office ko zataji sanyi koda kuwa zata had’u da Khalid ne suyi fad’a...
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*10*
Washe gari daga office koda ta dawo gida wasu ‘yan kayayyakinta ta had’a cikin k’aramar akwati kafin ta d’auki hanyar gidansu...,Kallo guda zaka mata ka fahimci tsan tsan damuwar dake tattareda ita..
Babu kowa a parlorn sai k’aran alarm ta dafuwar oxtail dake tashi daga kitchen, mik’ewa tayi saman sofa ta d’an kishingid’a had’ida lumshe idanunta, tanajin sanda Malam Sallau ya shigo da suitcase d’inta ya ajiye daga bayan parlorn yana mai fad’in “Hajiya ga jakar a nan...”
Ko zarafin amsashi Siyama bata samu ba har lokacin idanunta a lumshe suke, wasu irin tunani marassa kangado masu tada hankali su suka addabeta, yanzu idan Partner ya kasa jure rashinta kusanshi fah? Idan ya fad’a wata rayuwar fah..? Ko kuma idan yace zai k’ara aure fah... Shin waima da wasu irin mutane zaike huld’a....?” Ire iren tunanin dake zuwa zuciyarta kenan har Kubura mai aikin Ammi ta shigo parlorn Siyama bataji shigowarta ba...
Turus Kuburan tayi tana duban Siyama dake kwance saman sofa idanu a lumshe ko takalmin k’afarta bata samu zarafin cirewa ba dashike d’aure yake da belt...
Kubura ta kuma juyawa ta kalli akwati a gefe... D’an k’arasowa ta shigayi cikeda risinawa tana kiran Siyama...
“Aunty..! Aunty..!!!..” Shiru Siyama bata amsa ba...
Saida Kubura ta d’an buga kujeran kad’an tana k’ara fad’in “Aunty....”
Sai sannan Siyama ta bud’e idanunta had’ida d’an yamutsa fuska...
“Aunty lafiya kuwa...?” Kubura ta tambaya...
A kaikaice Siyama ta dubeta fuska babu walwala kana tace “Banson gulmarku ta masu aiki d’auki jakata ki haura min da ita sama d’akina...”
Kubura ta jinjina kai tana fad’in “A’a wai Aunty gani nayi kaman bakida lafiya shiyasa na tambaya....”
Gajeren tsaki Siyama tayi don ta tsani shiga sharo babu shanu irinta ma’aikatan gidan Ammi musamman Kubura, kallon data watsa mata yasa bata kuma cewa komai ba ta ciccib’i jakan tana washe hak’wara don ko babu komai zatake samun na kashewa don Siyama akwai sake hannu shiyasa duk ma’aikatan gidan ke bata girma kama daga masu gadi har ma’aikatan cikin gidan itadai barta da basarwa wanda usulin d’abi’artace miskilace ta gaske ba kasafai take shiga hark’an mutane ba shiyasa ko k’awaye basufi a k’irga ba wanda takedasu, tanada zafin rai abu k’ank’ani ke b’ata mata rai hakan yasa duk wanda yasanta yake shan maganin zama da ita... Da yawan mutane sukan d’auketa mace mai gadara da isa da ji da kai wasu kuwa kan d’auki hakan da cewa goyon data samu ne na sangarci daga gidansu... Idan kaji hayaniyar Siyama toh fah ka tabbata Khalid ne ya tab’ata shiyasa mahaifinta ya d’auki muk’ami mai girma a kampaninsa ya damk’a mata....
Ammy dake zarya cikin makeken d’akinta tana waya nan ta hangi Kubura da jaka nik’inik’i tana haurowa zata shige d’akin Siyama... A’a mamaki ya kama Ammy cikin sauri ta katse wayar da take kana ta tsare Kubura da fad’in “Ke ke yaya wannan fah...? Daga ina....?”
Kubura na haki take fad’in “Ammy Aunty Siyama ce tazo tana parlorn k’asa tana kwance, Ammy inaji dai babu lafiya ne don baki ganta ba gaskiya.....”
“Ke ya isheni bani hanya na wuce....” Ammy ta katseta sanda take sauk’owa daga bene cikin tsananin tashin hankali....
Kwance ta hangi Siyama har lokacin.... Cikin sauri Ammy ta k’arasa gareta.....
****
Kallon juna sukayi a karo na biyu kafin suka kuma tafe hannaye suna shewa irinta aminan asali, Hajiya taci gaba da juya super wax d’in dake hannunta kana tace “Ke Lami bakida kyau kin rantse sai kin mallaki tsohuwar nan...”
Aunty Lami ta kuma juya idanu kana tace “Ai idan sunsan wata basu san wata ba, nid’in nan dai da a baya aka ambata da juya mujiya merere wanere sai an dawo ana bina tako ina... Sai na zamto almiski duk yanda na shiga na bar k’amshina....”
Hajiya rik’e da hab’a take duban Aunty Lami kana suka kuma saka shewa, Hajiyar Hafiz tace ya labarin aminyar sirri....?”
A tare suka kwashe da dariya kana Aunty Lami tace “Zancen kike nema bara kiga na tashi na tafi kafin Abbah ya dawo daga kasuwa don yau zai komo d’akina gwara naje na masa shiri tinda ita wancan bataga kwanciyar hankalin ba ma ballanta ta tsaya kulada miji....” Ta k’arashe maganar tana tura zanin cikin bak’ar leda....
Hajiya ta mik’e tana gyara d’aurin zani take fad’in “Ai ni babban abinda kemin dad’i shine yanda Mamani ke matuk’ar k’aunar Hafiz sam bata ganin laifinsa idan kuwa baki mance ba a baya itace dai tak’i jinin d’ana ta d’auki son duniya ta d’aura kan Ma’aruf yaronda sam ashe ba mai zama bane k’ashinsa ya jima da daddagewa cikin k’asa....”