Sashe 43
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nabilah tai k’wafa kana ta bud’e flask d’in, tuwon shinkafa ce fara sol d’auri d’auri a leda, leda guda ta d’auka ta kwance ta saka cikin plate d’in zata kuma d’auko wata ledar yace da ita “Ya isa haka idan kuma ba tayani ci zakiyi ba...”
Takai masa mugun kallo had’ida d’auke idanu tana mai gyara zaman rigarta duk gaba d’aya a tsarge take ga Mamani ta gama yarfata...
Gaba d’aya a tak’ure take, ta soma k’ok’arin mik’a hannu zata janyo d’aya flask d’in yai saurin mik’a hannunsa ya tura mata kusanta, ba tareda dubeshi ba ta shiga kiciniyar bud’ewa...
Khalid ya mik’o hannu zai bud’e tai saurin janye hannunta...
K’uri ya mata yanda tai tsananin b’ata fuska, ya tab’e baki alamun ko inkula kana yace da ita “Na fasa taimakon ki bud’e da kanki kafin na kira Mamani nace mata rowa kike min...”
Ta kalle shi a kufule kana ta janye idanunta tana tab’a marfin taji ya bud’u alamun ya bud’e kenan....
Lafiyayyar miyar taushe ne wanda yaji bushesshen kifi da naman Sa... K’amshin ya daki hancin Khalid sanda taci gaba da serving d’insa bawai don ranta naso ba...
Tana gama serving d’insa ta soma k’ok’arin mik’ewa amma saiji tai ta kasa tashi sabida kallon da yake binta dashi, tai k’wafa cikin zuciyarta don ko magana ta kasa masa...
Khalid ya janyo plate d’in kaman zai soma cin abincin, itakoh sai satan kallonsa take ganin kaman hankalinsa ya koma kan plate ya sanyata mik’ewa a hankali, daidai sanda Mamani ta fito hannunta rik’eda takardan foster Clark...
“Ungo jeki had’o masa abin sha, kya bashi abinci haka babu ruwan zak’i ce maki akai shi ya saba cin abinci haka ne babu ruwan zak’i...?”
“Mamani fah baice maki zaisha ba don Allah ki k’yaleni na tafi aiki fah nake...” Tai maganar kaman zata runtuma kuka...
Shiko Khalid yana cin tuwon yana satan kallonsu ko tofawa baiyi ba...
“Aiki a’a kecema agogo, nace kece ma agogo... Shige ki had’o masa aikin naki ya jiraki...”
Nabilah ta gallawa Khalid da ya maida hankalinsa kan abincin da yakeci harara tai k’wafa a hankali... “Mamani da gaske baisha ki tambayeshi kiji....”
“Ke banson rashin kunyar banza a ina yace miki bayasha... Kai Haladu wai bakasha abin zak’in d’akin tsohuwa ba...?”
Khalid da bawai yama fahimci meye abinda ake shirin bashin ba amma duk dai salon kada Nabilah ta tafi yace “Idan an bani zansha Mamani....”
“Toh kaji d’an gari.... Maza shige ki had’a masa d’auki k’ank’ara a firiji (Fridge)...” Mamani ta fad’i tana zama kujeran data tashi...
Kaman zatai kuka haka ta shige kitchen, Hajiya Mamani taci gaba dajan Khalid da hira, idan tace Haladu shiko sai ya gyara mata yace Khalid ne, k’arashe ya fahimci Mamani ba daina ce masa Haladu zatai ba, sosai yaci abinci saida yaji mamakin kansa shida ba gwanin son tuwo ba amma tass ya cinye wanda Nabilah ta zuba masa...
Nabilah ta shigo d’aukeda k’aramar tray da jug had’ida cup bisa, wannan karon ta warware d’ankwalin kanta ta d’an rufe jikinta dashike yanada d’an girma...
Ta dire tray d’in gabansa, zata tashi Mamani ta kuma umartanta cewa ta zuba masa...
Badon taso ba ta d’au cup d’in ta shiga tsiyaya lemun, citta ta samu a kitchen d’in ta d’an markad’a ta tace ta had’e da lemon tsami kad’an sai d’an fosterclarck d’in data zuba kad’an sai sugar nan koh ya bada flavor mai dad’i tamkar lemonade...
Salon kar Mamani ta barta ta tafi yace ya gama cin abincin da an tattare wajen...
Nanma Mamani ta umarci Nabilah data tattare wajen....
Nabilah data cika fam k’iris ya rage bata fashe ba ta d’ago tana watsa masa mugun kallo kaman zatai kuka...
Murmushi ya sakar mata a hankali had’ida kashe mata idanu guda yana mai ci gaba da sipping drink d’insa...
Fuuu ta wuce da kwanukan kaman zata tashi sama...
Mamani tace “Maza ki fasa kwanukan na uwarkice babu asarana ciki ehe...”
Ko amsata Nabilah batai ba ta shige abinta, ai komawa sashen Mamani da bata iyayiba kenan, ko kitchen wajen Mamy bata biya ba ta fad’a d’aki tana maida numfashi...
Kaman wacce aka zabura tai saurin k’arasawa drawer d’in data aje teddy bear d’in da bata ta ciro tana duba...
“Who are you... Maiyasa kake bibiyan kowa a family na... Mai kake nema....?” Tamkar mai magana da mutum haka take maganar... Ta jima tana duban Teddy d’in tamkar mai jiran amsa daga gareshi saiji tai wayarta na faman ruri... Ta d’an firgita kana ta aje teddy d’in zata nufi wayar nan teddy d’in wanda idan yai babban motsi ke fad’in wasu kalmomi ya kuma fad’i mata kalaman _I love you_
Kallo tabi teddy d’in dashi kana ta nufi wayarta dake k’aran alamun shigowar sak’o...
Ta rausayar da idanu had’ida fuzar da iska kana ta d’aga wayar tana k’ok’arin karance sak’on...
_I’m waiting for you outside.._
Saida ta karance kusan sau uku kafin ta zauna saman gado tana tunanin martanin da zata maida masa bayan haushin da suka k’unsa mata shida Mamani...
_Mantuwa kai ko abincin ne bai isheka ba_ Ta rubuta ta tura masa..
Murmushi Khalid yai kana ya shiga tura mata reply kaman haka _Idan baki fito ba zan shigo har yanda kike na sameki kinsan zan iya... So you’ve 2minutes to decide, is either ki fito ko na shigo na sameki... Just 2 minutes.._
Rausayar da idanu tai kana takaima teddy d’in harara tace “Bazan fita ba saidai kai duk abinda kaga dama...”
Marliya dake tsaye bakin k’ofa tsoro da mamaki suka kamata ganin Nabilah ta saka teddy gaba tana tsigalesa...
“Addah Naby lafia..?”
Marliya ta tambaya tana dubanta...
Nabila ta d’an shafi goshinta tace “Lafiya mana mai kika gani...”
Marliya ta k’arashe shigowa d’akin kana tace “Yo niko naga komai, kin saka gunki gaba kina masa masifa, waima ba cewa kikai ma Kausar zaki kai ba.. Addah Naby anya lafiya kike...? Marliya ta k’arashe tsoro kwance saman fuskarta..
Janyo hannunta Nabilah tai sanda wayarta ta d’auki ruri kana tace “I’ll explain to you later, bani hijab d’inki kiga na fita yanzu zan dawo, karma Mamy ta sani dan Allah...” Ta k’arashe tana kwab’e hijab d’in daka kan Marliya ta zira ta fice cikin sauri...
Marliya ta bita da kallon mamaki tafito parlor a sanyaye....
A b’angaren Mamani kuwa sai k’irga kud’ad’en da Khalid ya bata take tana zirawa k’ark’ashin kwalla tana shimai albarka yanda kasan bata tab’a ganin tsaban kud’i ba ko sallama taji anayi zata tura k’ofa da sandarta sannan ta zaune akai kafin ta amsa sallamar...
***
Jingine jikin motarsa ta taddashi ya bada baya waya manne kunnensa na hagu abinka da lefty.....
Tai tsaye tana k’arema kwantattun sumarsa da a kullum cikin shek’i suke kallo, yanda ya bada bayan nan tamkar ta suri dutse ta runtuma ma k’eyarsa haka taji, tayi tsaye tana tunanin Khalid ya juyo yana dubanta, kaman wanda akacemasa juyo...
Kallo guda ya mata ya d’auke kansa yana ci gaba da amsa wayarsa, wani takaicin ya kuma lullub’e Nabilah, tasa kai zata juya cikin gida sabida tsananin takaici saijiyo muryarsa tai yana fad’in “Ina zaki...?”
Ta tsaya cak ba tareda ta juyo ba.. Badon Teddy d’insa dake duk’unk’une cikin hijab d’inta ba da tuni ta juya cikin gida hasalima da ko fitowa bazatai ba kawai dai don tana son maida mashi kayanshi ne...
A hankali ta juyo ta taddashi yanda yake tsaye....
Khalid ya murmusa a hankali had’ida zira hannaye cikin aljihu ganin yanda Nabilah tasha mur...
“Thanks for the food... it was delicious...” Ya fad’i idnunsa akanta....
Tinda ya soma magana idanunta ke k’asa tana duban k’fafunsa da Mamani ta zage mata nata k’afafun akansu, ta kuma duban nata k’afafun sai taji kaman yanzu Mamani ke zage mata nata k’afafun tai saurin maida yatsun k’afafunta cikin takalami, hankalin Khalid ya karkata kan abinda take duba yatsun k’afafunsa...
Murmushi ya kusa kufce masa, lokaci guda yake furta “Sun maki kyau ne..?”
Tai Saurin d’agowa a d’an razane tamkar wacce aka mintsila, lokaci guda ta had’e fuska tace “Allah ya sawak’e...”
Khalid ya murmusa a hankali kana ya tab’e baki yana mai furta “You know there’re some certain things that we can’t simply hide...”
D’agowa tai had’ida d’an masa wani duba “And there’re some certain people that we can’t simply stand them...”
“Are you sure about that...?” Ya tambaya cikin kashe murya....
Bata kuma tsayuwa basa amsa ba ta mik’a masa teddy d’insa tana fad’in “Ga abinka nan banso, just stop stalking me please..”
Khalid ya shiga kad’a d’an makulin hannunsa yana dubanta murmushi kwance saman fuskarsa....
Tai tsaye tana jiran taji ya amsa abinsa dashike kauda kanta gefe tai... Bata ankara ba sai k’aran tashin motarsa ta jiyo kafin tai wani aune ya bad’eta da k’ura ya bar wajen....
Tai saurin matsawa baya don kar ya had’eda ita baki sake tabi bayan motar tasa da kallo zuciyarta na k’una, amma wannan shi a sahun rainin hankalinma ajin k’arshe yake, kaman ta fashe da kuka haka ta shak’e wuyan teddy d’in ta nufi cikin gida ga ‘yansa idon unguwar zaune benci benci bakin kantina...
Hango Aunty Lami da tai ta sauk’a a adaidaita kuma wannan karon ma Hajiyar Ya Hafiz na cikin keken ya sanyata d’an lab’ewa cikin sauri ta lalumi wayarta ta shiga neman layin Aunty B da shike ta sanar da Aunty B d’in komai gameda zarginda takewa Aunty Lami kuma Aunty B tace she should keep her updated gameda komai don tasha alwashin tayata zak’ulo gaskiyar al’amari, idan har da gaske su Lami su suka sanadiyan gushewar farin cikin ‘yar uwarta sai yanda k’arfinta ya k’are wajen d’aukan fansa ga ‘yar uwarta....
***
Sameer ya kuma dubanta da mamaki kana yace “Are you serious zaki baro aikinki a Kaduna ki dawo ki zauna dani a nan...?”
Siyama ta kuma janyo hannunsa guda ta shige ciki tana mai furta “Of course Partner, na amince zan biyo aurena na kula da kai...”
Sameer ya tura yatsun hannunshi guda cikin nata yayinda ya mata matashi da b’angaren kafad’arsa guda kana yace “Baki tunanin Uncle bazaiso hakan ba...?”
Takai masa mugun kallo had’ida d’auke idanu tana mai gyara zaman rigarta duk gaba d’aya a tsarge take ga Mamani ta gama yarfata...
Gaba d’aya a tak’ure take, ta soma k’ok’arin mik’a hannu zata janyo d’aya flask d’in yai saurin mik’a hannunsa ya tura mata kusanta, ba tareda dubeshi ba ta shiga kiciniyar bud’ewa...
Khalid ya mik’o hannu zai bud’e tai saurin janye hannunta...
K’uri ya mata yanda tai tsananin b’ata fuska, ya tab’e baki alamun ko inkula kana yace da ita “Na fasa taimakon ki bud’e da kanki kafin na kira Mamani nace mata rowa kike min...”
Ta kalle shi a kufule kana ta janye idanunta tana tab’a marfin taji ya bud’u alamun ya bud’e kenan....
Lafiyayyar miyar taushe ne wanda yaji bushesshen kifi da naman Sa... K’amshin ya daki hancin Khalid sanda taci gaba da serving d’insa bawai don ranta naso ba...
Tana gama serving d’insa ta soma k’ok’arin mik’ewa amma saiji tai ta kasa tashi sabida kallon da yake binta dashi, tai k’wafa cikin zuciyarta don ko magana ta kasa masa...
Khalid ya janyo plate d’in kaman zai soma cin abincin, itakoh sai satan kallonsa take ganin kaman hankalinsa ya koma kan plate ya sanyata mik’ewa a hankali, daidai sanda Mamani ta fito hannunta rik’eda takardan foster Clark...
“Ungo jeki had’o masa abin sha, kya bashi abinci haka babu ruwan zak’i ce maki akai shi ya saba cin abinci haka ne babu ruwan zak’i...?”
“Mamani fah baice maki zaisha ba don Allah ki k’yaleni na tafi aiki fah nake...” Tai maganar kaman zata runtuma kuka...
Shiko Khalid yana cin tuwon yana satan kallonsu ko tofawa baiyi ba...
“Aiki a’a kecema agogo, nace kece ma agogo... Shige ki had’o masa aikin naki ya jiraki...”
Nabilah ta gallawa Khalid da ya maida hankalinsa kan abincin da yakeci harara tai k’wafa a hankali... “Mamani da gaske baisha ki tambayeshi kiji....”
“Ke banson rashin kunyar banza a ina yace miki bayasha... Kai Haladu wai bakasha abin zak’in d’akin tsohuwa ba...?”
Khalid da bawai yama fahimci meye abinda ake shirin bashin ba amma duk dai salon kada Nabilah ta tafi yace “Idan an bani zansha Mamani....”
“Toh kaji d’an gari.... Maza shige ki had’a masa d’auki k’ank’ara a firiji (Fridge)...” Mamani ta fad’i tana zama kujeran data tashi...
Kaman zatai kuka haka ta shige kitchen, Hajiya Mamani taci gaba dajan Khalid da hira, idan tace Haladu shiko sai ya gyara mata yace Khalid ne, k’arashe ya fahimci Mamani ba daina ce masa Haladu zatai ba, sosai yaci abinci saida yaji mamakin kansa shida ba gwanin son tuwo ba amma tass ya cinye wanda Nabilah ta zuba masa...
Nabilah ta shigo d’aukeda k’aramar tray da jug had’ida cup bisa, wannan karon ta warware d’ankwalin kanta ta d’an rufe jikinta dashike yanada d’an girma...
Ta dire tray d’in gabansa, zata tashi Mamani ta kuma umartanta cewa ta zuba masa...
Badon taso ba ta d’au cup d’in ta shiga tsiyaya lemun, citta ta samu a kitchen d’in ta d’an markad’a ta tace ta had’e da lemon tsami kad’an sai d’an fosterclarck d’in data zuba kad’an sai sugar nan koh ya bada flavor mai dad’i tamkar lemonade...
Salon kar Mamani ta barta ta tafi yace ya gama cin abincin da an tattare wajen...
Nanma Mamani ta umarci Nabilah data tattare wajen....
Nabilah data cika fam k’iris ya rage bata fashe ba ta d’ago tana watsa masa mugun kallo kaman zatai kuka...
Murmushi ya sakar mata a hankali had’ida kashe mata idanu guda yana mai ci gaba da sipping drink d’insa...
Fuuu ta wuce da kwanukan kaman zata tashi sama...
Mamani tace “Maza ki fasa kwanukan na uwarkice babu asarana ciki ehe...”
Ko amsata Nabilah batai ba ta shige abinta, ai komawa sashen Mamani da bata iyayiba kenan, ko kitchen wajen Mamy bata biya ba ta fad’a d’aki tana maida numfashi...
Kaman wacce aka zabura tai saurin k’arasawa drawer d’in data aje teddy bear d’in da bata ta ciro tana duba...
“Who are you... Maiyasa kake bibiyan kowa a family na... Mai kake nema....?” Tamkar mai magana da mutum haka take maganar... Ta jima tana duban Teddy d’in tamkar mai jiran amsa daga gareshi saiji tai wayarta na faman ruri... Ta d’an firgita kana ta aje teddy d’in zata nufi wayar nan teddy d’in wanda idan yai babban motsi ke fad’in wasu kalmomi ya kuma fad’i mata kalaman _I love you_
Kallo tabi teddy d’in dashi kana ta nufi wayarta dake k’aran alamun shigowar sak’o...
Ta rausayar da idanu had’ida fuzar da iska kana ta d’aga wayar tana k’ok’arin karance sak’on...
_I’m waiting for you outside.._
Saida ta karance kusan sau uku kafin ta zauna saman gado tana tunanin martanin da zata maida masa bayan haushin da suka k’unsa mata shida Mamani...
_Mantuwa kai ko abincin ne bai isheka ba_ Ta rubuta ta tura masa..
Murmushi Khalid yai kana ya shiga tura mata reply kaman haka _Idan baki fito ba zan shigo har yanda kike na sameki kinsan zan iya... So you’ve 2minutes to decide, is either ki fito ko na shigo na sameki... Just 2 minutes.._
Rausayar da idanu tai kana takaima teddy d’in harara tace “Bazan fita ba saidai kai duk abinda kaga dama...”
Marliya dake tsaye bakin k’ofa tsoro da mamaki suka kamata ganin Nabilah ta saka teddy gaba tana tsigalesa...
“Addah Naby lafia..?”
Marliya ta tambaya tana dubanta...
Nabila ta d’an shafi goshinta tace “Lafiya mana mai kika gani...”
Marliya ta k’arashe shigowa d’akin kana tace “Yo niko naga komai, kin saka gunki gaba kina masa masifa, waima ba cewa kikai ma Kausar zaki kai ba.. Addah Naby anya lafiya kike...? Marliya ta k’arashe tsoro kwance saman fuskarta..
Janyo hannunta Nabilah tai sanda wayarta ta d’auki ruri kana tace “I’ll explain to you later, bani hijab d’inki kiga na fita yanzu zan dawo, karma Mamy ta sani dan Allah...” Ta k’arashe tana kwab’e hijab d’in daka kan Marliya ta zira ta fice cikin sauri...
Marliya ta bita da kallon mamaki tafito parlor a sanyaye....
A b’angaren Mamani kuwa sai k’irga kud’ad’en da Khalid ya bata take tana zirawa k’ark’ashin kwalla tana shimai albarka yanda kasan bata tab’a ganin tsaban kud’i ba ko sallama taji anayi zata tura k’ofa da sandarta sannan ta zaune akai kafin ta amsa sallamar...
***
Jingine jikin motarsa ta taddashi ya bada baya waya manne kunnensa na hagu abinka da lefty.....
Tai tsaye tana k’arema kwantattun sumarsa da a kullum cikin shek’i suke kallo, yanda ya bada bayan nan tamkar ta suri dutse ta runtuma ma k’eyarsa haka taji, tayi tsaye tana tunanin Khalid ya juyo yana dubanta, kaman wanda akacemasa juyo...
Kallo guda ya mata ya d’auke kansa yana ci gaba da amsa wayarsa, wani takaicin ya kuma lullub’e Nabilah, tasa kai zata juya cikin gida sabida tsananin takaici saijiyo muryarsa tai yana fad’in “Ina zaki...?”
Ta tsaya cak ba tareda ta juyo ba.. Badon Teddy d’insa dake duk’unk’une cikin hijab d’inta ba da tuni ta juya cikin gida hasalima da ko fitowa bazatai ba kawai dai don tana son maida mashi kayanshi ne...
A hankali ta juyo ta taddashi yanda yake tsaye....
Khalid ya murmusa a hankali had’ida zira hannaye cikin aljihu ganin yanda Nabilah tasha mur...
“Thanks for the food... it was delicious...” Ya fad’i idnunsa akanta....
Tinda ya soma magana idanunta ke k’asa tana duban k’fafunsa da Mamani ta zage mata nata k’afafun akansu, ta kuma duban nata k’afafun sai taji kaman yanzu Mamani ke zage mata nata k’afafun tai saurin maida yatsun k’afafunta cikin takalami, hankalin Khalid ya karkata kan abinda take duba yatsun k’afafunsa...
Murmushi ya kusa kufce masa, lokaci guda yake furta “Sun maki kyau ne..?”
Tai Saurin d’agowa a d’an razane tamkar wacce aka mintsila, lokaci guda ta had’e fuska tace “Allah ya sawak’e...”
Khalid ya murmusa a hankali kana ya tab’e baki yana mai furta “You know there’re some certain things that we can’t simply hide...”
D’agowa tai had’ida d’an masa wani duba “And there’re some certain people that we can’t simply stand them...”
“Are you sure about that...?” Ya tambaya cikin kashe murya....
Bata kuma tsayuwa basa amsa ba ta mik’a masa teddy d’insa tana fad’in “Ga abinka nan banso, just stop stalking me please..”
Khalid ya shiga kad’a d’an makulin hannunsa yana dubanta murmushi kwance saman fuskarsa....
Tai tsaye tana jiran taji ya amsa abinsa dashike kauda kanta gefe tai... Bata ankara ba sai k’aran tashin motarsa ta jiyo kafin tai wani aune ya bad’eta da k’ura ya bar wajen....
Tai saurin matsawa baya don kar ya had’eda ita baki sake tabi bayan motar tasa da kallo zuciyarta na k’una, amma wannan shi a sahun rainin hankalinma ajin k’arshe yake, kaman ta fashe da kuka haka ta shak’e wuyan teddy d’in ta nufi cikin gida ga ‘yansa idon unguwar zaune benci benci bakin kantina...
Hango Aunty Lami da tai ta sauk’a a adaidaita kuma wannan karon ma Hajiyar Ya Hafiz na cikin keken ya sanyata d’an lab’ewa cikin sauri ta lalumi wayarta ta shiga neman layin Aunty B da shike ta sanar da Aunty B d’in komai gameda zarginda takewa Aunty Lami kuma Aunty B tace she should keep her updated gameda komai don tasha alwashin tayata zak’ulo gaskiyar al’amari, idan har da gaske su Lami su suka sanadiyan gushewar farin cikin ‘yar uwarta sai yanda k’arfinta ya k’are wajen d’aukan fansa ga ‘yar uwarta....
***
Sameer ya kuma dubanta da mamaki kana yace “Are you serious zaki baro aikinki a Kaduna ki dawo ki zauna dani a nan...?”
Siyama ta kuma janyo hannunsa guda ta shige ciki tana mai furta “Of course Partner, na amince zan biyo aurena na kula da kai...”
Sameer ya tura yatsun hannunshi guda cikin nata yayinda ya mata matashi da b’angaren kafad’arsa guda kana yace “Baki tunanin Uncle bazaiso hakan ba...?”