← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 198

Sashe 21

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsuka Nabila tai kana tace “Aikin banza wannan da gani ruwan munafukai ne da ita shiyasa sam tamu batazo d’aya ba... Nidai na fad’a miki idan ina waje kema kiyi banza da ita kafin na tunb’uke miki hak’orin gaba....”

Girgiza kai kurum Marliya tai tana dariya kana ta fice a kitchen d’in ta bar Nabilah da masifarta...

***

Wajajen biyar na yamma Khalid ya sauk’a a Kaduna dashikema bai fito da wuri ba saida ya tsaya ya kammala wasu abubuwan....

A parlor ya tadda Siyama da Yesmin first cousin d’insa d’iyar Yayan Ammi dake karatu a Cyprus, rabonsa da ita zaikai shekara biyu ko fiyeda haka idan bai mance ba...

Siyama na hangosa murmusinta ya k’aru kana tace “Speaking of the devil... Kinga gashi nan sauk’arsa kenan....”

Baice mata komai ba sai uwar harara da ya danna mata

Cikeda zumud’i Yesmin ta ajiye glass of lemonade dake hannunta ta juyo tana dubansa fuska fal fari’a.....

SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_

*20*

*©Sameena Aleeyou...✍🏽*

“Ya Khalid sannu da zuwa, ya hanya...?” Yesmin ta fad’i cikin kashe murya....

Kallon kirki bata ishi Khalid ba yace da ita “Kina lafia...?” A tak’aice...

Nanma saida ta kuma murmusawa had’ida juya idanu kana tace “Lafia lou, it’s been a while...” Bai bari takai ayaba yace “As you can see I just got home, I’m pretty tired... would you please keep your greetings maybe for later....” Ya k’arashe yana d’aga mata giransa sama alamun Yes a gajjiye yake...

Nan fah jikin Yesmin yayi sanyi ta juyo suka had’a idanu da Siyama, sosai Siyama taji kunyar abinda Khalid yayiwa yarinyar nan Yesmin tasan za’a rina hakan kallon su Ammi kurum take idan taji suna mafarkin had’a Yesmin da Khalid, basusan Khalid wane irin baud’edd’en mutum bane shiyasa...

Har ya isa staircase Siyama ta d’an bud’e murya tace “Eyya shalelen Daddy sannu da hanya ko nazo na baka massage ne...?”

Rolling idanunsa yayi yana mai dubanta a kaikaice kana yace “Spare me your false sympathy Siyaam...” Daga haka bai kuma cewa komai ba sai sa kai da yai yayi haurawansa sama...

Duban Yesmin Siyama tai fuska d’aukeda murushin yak’e kana tace “Ehen mai ma nake ce miki....?”

Girgiza kai Yesmin tai kana tace “Cousin anya Khalid zai soni kuwa...? Kiga fah abinda yayi...”

Murmushin Siyama ta kumayi kana tace “Kar ki damu cousin idan dai Khalid ne ya wuce haka, but I believe you can change him....”

Sauk’e deep breath Yesmin tai kana tace “But are you sure he doesn’t have a girlfriend...?”

Murmusawa Siyama ta kumayi kana tace “Wa... Wannan...?” Ta kuma d’an murmusawa kana tace “Dukda fad’a da muke yawan yi Khalid bai tab’a b’oyemin komai ba na rayuwarsa... Idan da ace yanada I’ll be the first person to know.. My brother is single... Shifah wannan baida lokacin ‘yanmatan ma pride d’insa bazai bari ya nemi budurwa ba shiyasa nace miki idan kinyi hak’uri you can win him over...”

Kurb’an lemonade Yesmin tai tana jinjina kalaman Siyama...

A b’angaren Khalid kuwa Haurawa sama da yayi yaji dama bai shigo sashen Ammi ba gaba da’aya, Aunty Hidaya ya hango mahaifiyar Yesmin Yaya ga mahaifiyarsa....

Cikin sauri yasa kai zai juya saidai tuni Aunty Hidaya ta hangoshi, bud’e murya tai cikeda far’a kana tace “A’a Son suk’ar yaushe....?”

K’ak’aro murmushi yayi yace “I just arrived Aunt.... Mun sameku lafia....?”

Aunty Hidaya ta kuma murmusawa kana tace “Lafiya lau Saifullahi... Ya aiki...?”

Murmushi Khalid yayi don ita kad’ai ke ce masa Saifullahi kana yace “Lafiya Aunt... Aunt Ammi fah...?”

Aunty Hidaya tace “Ta shige d’aki but tana fitowa... inaga bathroom ta shiga....”

Jinjina kai yayi kana ya mik’e a d’an gajjiye yace “Ok Aunt idan ta fito a ce mata na dawo... zan wuce d’aki na d’an kwanta before magrib...”

Dakatar dashi Aunty Hidaya tai da fad’in “Kaga k’anwar taka a k’asa koh... Jiya ta dawo daga sch ta gama gaba d’aya sauran karb’an result, she was so excited sanda taji zanzo don ko hutawa batai ba tace zata biyoni Kaduna....” Ta k’arashe cikeda gwad’a d’iyarta Yesmin....

Tak’aitaccen murmushi yayi kana yace “Aunt I’m exhausted, see you later....”

Yana ida fad’in haka ya fice cikin sauri ba tareda ya bari ta kuma janyo wani zancen ba....

Kallo tabi bayansa dashi k’asar zuciyarta tana furta lallai akwai aiki da wannan baud’edd’en yaron....

****

Yana zuwa d’aki wanka yayi ya rage kayan jikinsa zuwa masu sauk’i kana ya mik’e kan gadonsa... Wayarsa ya janyo ya shiga duban lambar da ya d’aukesa lokaci a garin Kano kafin ya samu don neman lambar ne ma ya dad’a zaunar dashi....

Kallon lambar yake yana murmushi lokaci guda ya shiga tura sak’o yana mai ambatawa cikin zuciyarsa

_Karkiyi tunanin Khalid ya mance... No never, you must pay for what you did..._

****

Nabila ta kuma duban Addarta Zulfah a karo na biyu kana tace “Addah donma bakiga how Mamy scolded me bane ranan da nazo na jima, is like Mamy gani take Aunty Bara’atu is nothing but a bad influence to her children, gani take wajenta nake koyo duk wani rashinji... Yanzu ma bance mata ga yanda zaje ba kawai tasan dai zan shiga sch registration ne dashike an koma....”

Zulfah ta sauk’e nannauyan ajiyan zuciya kana ta kamo hannayen Nabilah tace “Kiyi hak’uri Sis ni na janyo miki....”

Girgiza kai kurum Nabilah tai kana tace “A’a you don’t have to apologize, I’m your sister, when ever you need me.... I got your back....”

Rungumeta Zulfah tai cikeda farin ciki suka ci gaba da firansu....

Daga yanda Aunty B ke tsaye jinjina kai tai k’wayan idanunta suna kuma kad’awa, ‘yar uwarta Mariya bazata tab’a daina kallonta a matsayin mutuniyar banza ba, tun suna k’ana haka ta d’auketa har sukayi aure, har izuwa lokacinda iyayensu suka rasu suka barsu..... Hannu tasa ta goge hawaye guda da ya gangaro mata bata iya shiga d’akin ba sai juyawa da tayi da baya....

“Ya Kausar..? Kinje kin dubota...?” Zulfah ta tambaya damuwa kwance saman fuskarta....

Girgiza kai Nabilah tai kana tace “Banje ba tukuna amma In sha Allah daga nan zan biya...”

“Yaya Hafiz fah.... Yana zuwa gida...?”

Saida Nabilah ta aika mata wata kallo kana tace “Toh ni ina ruwana dashi da har zan fahimci yana zuwa ko bai zuwa....”

Zulfah bata kuma cewa komai ba tinda ta fahimci tambayar Hafiz ya sanya ran ‘yar uwar tata b’aci....

Mik’ewa Zulfah tai ta bud’e drawer ta zaro wasu ‘yan kud’ade kana ta mik’awa Nabilah tace “Gashi ki sai mata tsara idan zakije and please hug her for me... Kema ga wannan ki sai maku wani abin keda Marliya....”

Kallonta Nabilah tai ta kalli kud’ad’en kana tace “Addah save your money, now that you’ve to face another life zai maki amfani, nida Marliya bamu buk’atan komai, zandai karb’i na Kausar na sai maita...”

Girgiza kai Zulfah tai kana tace “Karki damu na karb’i alawee na ne na wannan watan, I’m still saving some, sannan babu abinda Aunty B bata min kinji koh so ki kwantar da hankalinki.... Inaso na kira Mamy but banso ta fahimci komai cikin muryata... Can you please hug her for me...” Ta k’arashe idanunta na rau rau....

Hannayenta Nabila ta rik’e cikeda tausayawa kana tace “Komai zai wuce Addah... Kar ki mance masu iya magana sunce INDA RAI DA RABO... Watarana zaki bud’e idanu ki tarar komai ya wuce, rayuwa ta zamto sabuwa mai dad’i, all your nightmares zasu gushe kinji koh... Never lose faith...”

Jinjina kai Zulfah tai kana tace “Allah yasa k’anwata...”

Nabila ta sakar mata sassanyar murmushi....

Sun jima suna tattaunawa kafin Nabilah ta d’auki jakarta da ‘yar folder d’inta ta makaranta tai masu sallama....

Tana tsaye tana neman adaidaita sak’o makamancin na jiya ya shigo mata daga lambar da bata sani ba...

Karancewa tai had’ida jan tsuka ta danna delete, bata kuma bi takai ba ta tari adaidaitan ta ta nufi gidan Hajiya.....

Saida ta tsaya bakin babban kwalta tai sayayyan kayan mak’ulashe na yara wa Kausar kafin ta nufi gidan...

Akayi sa’a bata tadda Hajiya ba, da alama harta yaran Hajiyan ma basa nan, Raihanah kawai ta tadda zaune bakin barandar Hajiya suna wasa itada Kausar...

Sosai Nabila taji dad’in ganinsu haka, tayi tsaye tana dubansu fuska fal fari’a....

Kausar ince ta fara hangota ta shiga d’aga hannaye sama tana dariya alamun ta ganeta....

A guje Nabila ta tafi ta d’aga yarinyar sama tana cillawa Raiha na dariyarsu...

D’an gefe dasu Nabilah ta zauna Raihana na mata sannu da zuwa...

Fuska a sake Nabila ta amsa kana tace “Yau ku kad’ai ne a gidan...?”

Jinjina kai Raiha tai kana tace “Sun fita gaba d’aya d’iyar k’awar Hajiya ta haihu yau ake suna....”

Nabila ta jinjina kai don taji dad’in hakan zata samu ta tambayi Raihana kalan goyon da ake baiwa d’iyar ‘yar uwarta.....

“Raiha ki fad’imin gaskiya please Ya rayuwar Kausar yake hannun Hajiya da iyalanta....?”

Take idanun Raihana sukai rau rau, lokaci guda tasa bayan hannunta ta goge hawayen kana tace “Addah Nabila ko ban fad’a miki ba kinsan irin rayuwar tsanar Addah Zulfah da sukai yayi tasiri ga rayuwar innocent Kausar... Addah Nabila banso Kausar tayi irin girman da nayi.... Inso taji dad’i ta rayu da mahaifiya tasan soyayya da shak’uwa irinta mahaifiya wanda ni na rasa tsawon rayuwata....” Ta k’arashe hawaye na gangaro mata...

Nabilar ma k’walla ne suka ciko idanunta, tai k’ok’arin dannewa don k’arfafa gwiwan Raihana kana ta kamo hannayen Raihana ta rik’e cikin nata lokaci guda take furta “Komai zai wuce Raiha, komai zai zama labari.... Hak’urinki bazai tab’a tafiya kawai ba, zaki cimma wani mataki na rayuwa da yardar Allah.... Believe me INDA RAI DA RABO.....” Ta k’arashe tana k’ak’aro murmushin k’arfafa gwiwa....

Jinjina kai Raihana tayi had’ida sakin murmushi kana tace “Haka ne Addah Nabilah wataran komai zai zama labari...”

Nabila ta sakar mata murmushi kana ta mik’a mata ledar hannunta tace “Ga wannan sai ki adana mata please...”

Cikedajin dad’i Raihana ta amsa tana mai godiyawa Nabilar domin ita duk wanda zai k’aunaci Kausar ya gama mata komai, har cikin ranta takejin yarinyar...
Chapter 21 · 0% Book details