← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 198

Sashe 75

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gajeren tsaki Ammi tayi had’ida girgiza kai kad’an don ta fara gajjiya da fad’an Kubura da Yesmin kan namijin da sam basa gabansa....Ta dubi Kubura tace “B’ace min daga nan, idan bakida aiki kije ki taya Tabawa....”
Ta maidoda dubantaga Nabilah tace “Ke! Kinajina banason salon iskanci da bariki, tun muna shaida juna ki tattari k’afafuwanki Ki bari gidan nan, sannan ki fita daga rayuwan d’ahnah for good don shi ba mijinki bane kin jini koh, kinsan hausawa suna cewa idan kunne yaji toh fah jiki ya tsira, Don haka ki rufa ma kanki asiri kibi ta k’ofan da kika shigo ki fice tun kafin a fiddaki ta wata k’ofar....”
D’agowa Nabilah tai ta dubeta kana ta kuma sadda kanta tace “Kiyi hak’uri Ammi bazan tafi ba har sai nayi magana da Daddy....”

Yesmin ta dubeta shaye da mamaki kana tace “Eh lallai... Kinji koh Ammi, kinga irin salon nata koh.... Kawai ki bani dama na fidda maki ita right this minute....”

Murmushi Ammi tai tana mai duban k’arfin hali irinta Nabilah kana tace “Baza’ai haka ba Yesmin... K’yaleta badai tace Daddy take son gani ba.... Let her come inside and wait...”
Yesmin ta dubi Ammi zatai magana... Ammi ta kashe mata idanu guda....
Lokaci guda Ammi ta sakarwa Nabilah murmushi kana tace “Ki shigo parlor ki jira Daddyn anjima kad’an zai fito daga sashensa, shigo ki zauna, Yesmin tell Kubura to serve her drink...”
Yesmin tai tsaye tana duban mamaki wa Ammi yanda ta janyo Nabilah ta zaunarta saman kujera.... Harda kunna mata tv kana tace ta saki jikinta anjima kad’an mijinta zai sauk’o....

Cikin sauri Yesmin tabi bayan Ammi, a staircase ta tari Ammi tana fad’in “Haba Haba Ammi ya zakiyi haka, ya zaki bar wannan ‘yar iskar yarinyar ta shigo cikin parlornki har ta zauna, maiyasa baki bani go ahead na fiddata ba, ita har ta isa tace Daddy tazo gani...? Ammi kuma fah kinsan I can’t stand the sight of her....”

Banda harara Ammi bata b’alla mata komai, janyo hannunta tayi suka shige d’aki kana tace “Ashe ke banza ce shashasha, banda abinki ce maki akai bansan mai nake bane, wannan shine damarmu da zamuyi amfani da ita mu rabata da Khalid har abada, na tabbata idan har muka nunawa Khalid cewa wannan yarinyar har gida take bin manyan alhazawa tunda gashi ta biyo mahaifinshi tsaf zai yarda cikakkiyar k’aruwa ce, kinga shikenan Khalid ya rabu da ita har abada, zai dawo ya bamu hak’uri ya kuma amince da zab’inmu....”
Yesmin ta zaro idanu tana duban Ammi cikeda mamaki kana ta tintsire da dariya tace “Amma Ammi ban tab’a yarda da hausar nan cewa abinda babba ya hango yaro ko ya hau rimi bazai hanga ba irinta yau, shikenan kuwa Ammi, Wllhi kin kawo shawari, Bara na kirawo Cousin ta baro duk abinda take tazo ayi a gabanta....

**

Tsaye Baffah yai yana dubanshi yanda ya kishingid’a saman kujera idanunsa a lumshe, tausayin abokin nasa ya cikasa, tunani yake ya sanar dashi ne koko kada ya sanar dashi, da alama Nabilar batason yasan taje gidansu, toh idan wani abin yaje ya faru fah tinda yasan ‘yan uwan Khalid da iyayensa sam basa son Nabilah hasalima she’s the reason Khalid yake cikin condition d’in da ya tsinci kansa ciki.... Toh ko dai ya fad’iwa Khalid d’in ne, maybe everything will come to an end.... Da wannan tunanin ya k’araso cikin parlorn, daga can kujeran gefen Khalid d’in ya zauna had’ida k’ura masa idanu....
Khalid ya k’yallara idanu guda yana duban Baffah, gajeren tsaki yayi kana ya gyara kwanciyarsa ya kwanta sosai cikin kujera yana mai furta “Don’t give me that look...”

Baffah ya fuzar da iska yace “Khalid you need to end this for crying out loud... Jibi fah ka duba kaga duk yanda ka wani rame, kaman ba Khalid Mainasara da na sani ba... Haba Dude just put an to this already...”

D’ago Khalid yayi yanai masa wani irin duba kana yace “Wait... Ka gaji da gani na a nan ne... Idan ka gaji da ganina ne just go straight and tell to my face, ba wai ka tsaya kana karanto min lectures d’inka da already na sani ba ka gane.... I’m fed up with you already...” Ya k’arashe yana mai mik’ewa tsaye zai nufi d’aki...
Baffah ya bud’e murya yace “Do you really want to ruin your life just because of a girl...?”

Cak Khalid ya tsaya kana ya karkato yana duban Baffah... Gajeren murmushin takaici yayi kana yace “Did you just say ruin my life..? Idan baka sani ba... It’s official, my life is actually a complete mess... So ka daina cewa zan ruining rayuwana...” Yasa kai yana mai ci gaba da tafiya..

Baffah ya kuma bud’e murya yace “Kasan cewa tazo Kaduna... Probably tana gidanku....”

Wannan karon sosai Khalid ya juyo yana dubansa, saida ya d’auki dak’ik’a guda kana yace “What do you mean...?”

Baffah ya mik’e tsaye kana yace “I mean Nabilah....”

Kallonsa Khalid yake sosai kana yace “Nabilah kuma... Mai zai kawota gidanmu for what...?”

Baffah ya d’an ciza leb’ensa yace “Khalid I’m sorry... But I told her everything... The situation you’re in right now... Inaga shiyasa tazo maybe to confront your parents....”

Girgiza kai kurum Khalid yake idanunsa suka kad’a sukai jazir ji yake tamkar ya dunk’ula hannu yayita kaiwa Baffah duka... Cikin tsananin b’acin rai ya tako gaban Baffah, yana huci yake furta “How many times do I have to tell you, I hate people intruding into my life.... Why Baffah... Maiyasa zaka sanar da ita... Akan mai...? What if they did something to her...? You know perfectly well basa sonta, they’re capable of anything...”

Baffah na b’alla masa harara yake furta “Because I cant stand seeing you like this.... I don’t want you to go astray, I don’t want you to ruin your life..”

“Just shut up..!!” Khalid ya katsesa kafin yaci gaba da furta “I don’t need your concern.... Kuma na gama zama a nan...” Yana ida fad’in haka ya nufi d’aki kaman zai tashi sama Baffah na biye dashi na kiran sunansa inaa ko sauraronsa Khalid bai tsayayi ba, tuni ya soma parking stuff d’insa....

***

Laila ta dubi Siyama a karo na biyu kana tace “Look princess I’m not saying you should leave him for good, kawai zaki rabu dashi ne na d’an wani lokaci to teach him a lesson and to let him see your worth.... Sometimes dole mu bar abinda mukeso don mu karb’awa kanmu’yanci, kan mai zakije ki zauna cikin talakawa da talauci don kawai Sameer na son zama cikin talakawa, babu dangin iya balle na uba, ya bar gidansu gidan arziki ya koma zama cikin tsiya, idan ba mugunta ba mai hakan ke nufi... Look princess men are so selfish wasu lokutan, ki baro gidanku da aikinki da gatanki da komai ki koma zaman k’unci Wai duk kan soyayya, soyayyar da rana tsaka zaki iya ganinsa da wata macen tinda shi k’ofa uku ya rage masa bayan ke, yes he has the right ya auro Uku bayan ke... while ke kuma on the other hand bakida wannan damar, ya kashe maki kariya ya hanaki aiki... Nan gaba ya auro mai zuwa office da zuba kwalliya ki dawo ‘yar kallo cikin gidanki.... Toh wllhi kiyi ma kanki fad’a tun wuri kafin lokaci ya k’ure maki....”

Sauk’e nannauyan ajiyan zuciya Siyama tai kana tace “Yes princess you’re absolutely right.... Ya kamata na karb’i’yancina daga wajen Sameer I can’t let him control me.... Bazan bar soyayyan da nake masa yaci galaba akaina ba.... I’ve to fight my battles....” Ta k’arashe tana mai hura hanci had’ida duban wani gefe guda....

Laila ta saki murmushi a hankali kana ta kurb’i drink... Tuni Siyama ta suri handbag d’inta sukai sallama da Laila...

****

Tsananin mamakin abinda kunnuwarsa ke sauraro masa daga cikin gidan ne ya hanasa shigewa cikin gidan, banda ele da kacaniyan mutane had’ida wak’okin ‘yan bori baka jiyo komai... Hafiz yai tsaye yana sauraron ikon Allah yanda kasan bayan gari haka gidan ya koma..... Yana nan tsaye mutanen unguwa da fitowarsu kenan daga masallaci suka k’araso sukai masa sallama, da k’yar ya iya amsa sallaman nasu... D’aya daga cikin mutanen ya bud’e murya yace “Alhamdulillahi Allah ya kawoka, wato a gaskiya mun damu matuk’a da abindake wakana cikin gidanka, tun jiya abu yak’i ci yak’i cinyewa... Don munso kiran jam’ian hizba tun a jiyan amma wasu daga cikin committee na unguwa sukace mai gidan baya nan a bari nan da zuwa kwanaki uku idan har bai dawo ba sai a zattar da hukunci don bai kamata a apka masa gida kai tsaye ba dukda irin abubuwan dake faruwa cikin gidan....”

Hafiz da har lokacin yawun bakinsa a k’afe yake, da k’yar ya lalumo kalamai saman harshensa yace “Malam Sambo wani abu ne ke faruwa cikin gidan nawa....?”

Mutuminda ya kirada Malam Sambo bai kaiga basa amsa ba d’aya mutumin gajeren cikinsu yace “Kai kurma ne... Shin baka jiyo sautin kalangu da ‘yandaudu dake tashi cikin gidan... Kaga sam bazamu lamunci wannan abu ba, tarbiyan yaranmu muke jiyewa don haka dole ka tashi ka bar unguwar nan matuk’ar iyalinka zata maida gidanka gidan baje kolin shaid’anu... Haba ace an yini an kwana zubur ana abu guda tun jiya, babu dare babu rana babu sararawa balle sanin lokacin sallah, toh sam bazai yuwu ba mu bamu saba ganin irin wannan d’abi’a a unguwar nan ba, bazai yuwu a kawo mana gidan bori a unguwa ‘yan daudu da lalatattu suke mana safara ba, ya zama dole mu d’au mataki....”

D’ayan ya jinjina kai yace “Wannan hakane, unguwar nan an mana shaida mai kyau bazamuso rana tsaka wani ko wata ya kawo mana mishkila ba... Kuma tinda ka jima a unguwar hakan bata tab’a faruwa ba sai yanzu...”

Hafiz ya lumshe idanunsa a hankali hawaye masu d’umi suka zubo masa.... K’unci sun taru sun masa yawa a zuciyarsa.... Suna nan tsaye shida mutan unguwa wasu mazan suka fito daga cikin gidansa rungumeda ‘yanmata...
D’aya Dattijon ya furta “Subhanallahi... Ka gani koh, kaga irin musiban dake faruwa tun jiya a gidanka.... Toh ya zama wajibi ka d’auki mataki kokuma mu mu d’auka....” Daga haka tafiya sukai suka barsa nan tsaye yana mai bin’yandaudun da zasu shige cikin gidansa da kallo...
Chapter 75 · 0% Book details