Sashe 95
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baisan sanda shima a harzuk’e jijyoyinsa sunyi sama yake furta “Abinda suka jik’a suka baiwa Siyama ta kasa rabuwa da Sameer nima shi suka jik’a suka bani.... Cos yarinyar da kuka tsana kuke jifarta da sharri turned out to be Siyama’s sister in-law... Nabilah ba kowa bace face k’anwar Sameer wanda suke uwa d’aya uba d’aya..!!!” Yayi maganan yana mai takowa dab gaban Siyama
Ba Siyama datayi mutuwar tsaye ba harta Ammi neman yawun bakinta tai ta rasa balle tai tunanin kalamai ka iya zuwa kan harshen ta....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*73*
Girgiza kai Siyama take cikin rashin yarda da abinda kunnuwanta ke jiyo mata, lokaci guda ta kamo hannayen Khalid tana mai furta “Khalid tell me this isn’t true.... Wasa kakemin koh, babu abinda ya had’a Sameer da wad’annan mutanen.... Tell me you’re just joking...”
Fincikar hannayensa yai kana yace “Since when muka soma wannan wasar dake abinda kikaji gaskiya ne Nabilah k’anwar mijinki ne....!”
“What was that...?” Muryar Daddy ya katsesu..... Lokaci guda Ammi dake faman girgiza kai itama cikin rashin yarda ta shiga furta “Karka sauraresa, shak’iyancin Khalid ne kawai ya motsa don an hanasa auran yarinyar shine bari ya dangantata da Sameer, yo ina Sameer ina zuri’ar yarinyar can dangin mayu.... Kai ko a halitta Sameer yayi kama da wad’ancan mutanen ne.... Wllhi k’arya yake tsantsan Daddyn Siyaaam kar ka yarda dashi.....”
Siyama dake tsananin kuka kuma janyo hannayen Khalid tai tana jijjigawa da iyakan k’arfinta take fad’in “Khalid tell me is isn’t true... Ka fad’a min k’arya kake...!!!!” Ta k’arashe cikin tsananin d’aga murya....
Daddy ne ya k’araso ya janye hannayen Siyama daga na Khalid yana mai k’ok’arin kwantarwa Siyamar hankali....
Cikin kuka Siyama ke furta “Daddy Wllhi k’arya ne, of all people those people can’t be my husband’s family.... Daddy not my Sameer....” Ta k’arashe cikin shesshek’ar kuka....
Duban Khalid dake faman watsama Siyama muguwar kallo Daddy yai kana yace “Khalid..!”
D’ago kai Khalid yai ya dube mahaifin nasa had’ida furta “Na’am Daddy..” lokaci guda yaci gaba da furta “Ka sameni a parlor na...”
Babu musu Khalid ya jinjina kai kana yabi bayan Daddyn yana mai watsawa Siyama da Ammi ke tausanta harara....
Daga can gefen k’afan mahaifin nasa ya zauna had’ida risinawa kana yace “Daddy barkada gida, ina yini....”
Amsa masa mahaifin nasa yai kana yai gyaran murya ya soma fad’in “Khalid maike faruwa...? Shin abinda naji kana fad’i gaskiya ne cewa yarinyar can k’anwar mijin Siyama ne....?”
Jinjina masa kai Khalid yai had’ida gyara zamansa kana yace “Daddy abinda kaji gaskiya ne, Nabila k’anwar Sameer ne, recently Sameer ya sami biological parents d’insa, and it happens to be Nabilah k’anwarsa ce Daddy... Wato Daddy akwai abubuwa da dama da suke faruwa a gidan nan wanda sam basa dacewa tin daga kan yanda ake gudanar da al’amran gidan nan... Daddy ba wai ina fad’in gazawarku bane a matsayinku na wad’anda hakkin kula da tarbiyan gidan nan ya rataya a wuyarsu bane most especially you Daddy... Amma maganar gaskiya fah Daddy kuskuren tin daga sama ne, ya samo asali ne daga wajenka, ka baiwa Ammi wani irin power a gidan nan wanda sai abinda taga dama akeyi, Daddy I’m not saying baiwa matarka dama da freedom kuskure bane, but Daddy everything has a limit, ina ganin a matsayinka na shugaba a gida ya kamata ka zama kaikeda final say matuk’ar bai kaucewa Shari’a ba, Daddy karfa ka mance Allah da kansa ya gargade masu imani cewa su tsare kawunansu da iyalansu daga shiga wuta, shin Daddy mecece makomar gidan nan...? Yanzu ga Siyama a gida itama bata d’auki auren da daraja ba balle mijinta sabida abinda ta taso taga akeyi kenan a gidansu, turbar da mahaifiyarta ta d’aurata bisa kenan... Sam Ammi da Siyama basu d’auki d’an adam da wata daraja ba idanba wanda suke so bane... After what she’s done a gidansu Sameer bansan da wasu idanu zata dubesu matsayin sirakanta ba, Daddy mai ya haifar da haka...? Rashin samun wadataccen tarbiya ne tin daga fari shi ya haifar da haka.... Opinion d’in kowa a gidan nan baida daraja idandai ba daga Siyama ya fito ba, Ammi bata d’aukan maganan kowa ko shawarin kowa saina Siyama, and Daddy kaikuma duk abinda Ammi ta fad’i a gidan nan shikenan daidaine kayi na’am dashi without overlooking it... Daddy please ya kamata a daina irin wannan rayuwar a gidan nan, a duba lamarin Daddy.....” Ya k’arashe cikin tsananin k’ank’an da kai da kuma murya....
Shiru ya gifta tsakaninsu tamkar mahaifin nasa bazaice komai ba, saima d’aura hab’arsa da yayi saman hannayensa guda biyu da ya dunk’ule waje guda....
Muryar Ammi ce ya katse shirun da ya ratsa cikin parlorn...
“Toh wllhi ba k’anwar Sameer ba, yau idan uwar Sameer ce wannan yarinyar babu abinda ya shalleni, wllhi bazaka aureta ba muddin ina numfashi, yo sai mai... Allah ya kiyayeni na had’a jini da matsiyata, kuma shima Sameer d’in sai ya sakar min d’iyata, wllhi bazata zauna dashi ba, naji dad’i da rabo bai tsaga tsakaninsu ba, rabuwa ya zama dole, gwara da Allah ya bayyana mana....” Bata ida maganar nata ba Siyama ta shigo tana kuka tana fad’in “Ammi wllhi bazan rabu da mijina ba.... Gaskiya ni bazan iya rabuwa da Sameer ba don wllhi ina sonshi ina k’aunarshi har kwanan gobe, Sameer is nothing like his family, tsautsayi ne da k’addara yasa suka zama danginsa, kuma ma ai su Mummy ne iyayensa shida wad’ancan mayun jini ne kawai ya had’su, but his real family are here.... So Ammi don’t think of separating us... Nida Sameer are magnets babu wanda ya isa ya rabamu not even his so called new family, yanzu zan tafi ba sai anjima ba, yanzu zan koma to win my husband back don ya zama dole na rabasa da wad’ancan annoban....!” Tana ida fad’in haka ta fice fuuuu Ammi na k’walla mata kira ko saurarenta bata tsayayi ba...
Ammi ta maidoda dubantaga Daddy tana fad’in “Daddyn Siyaam kaga fah tafiya zatayi, kayiwa Allah ka dakatar da ita kartaje su lashe min ita kaman yanda suka lashe Khalid...” Ganin bai amsata ba ya sanyata janyo Khalid tana fad’in “Tashi tashi wuce maza ka k’wato min car keys d’inta...” Khalid na tirjewa Ammi na turasa, fad’i yake “Ammi kinsan Siyama idan tayi niyyan abu no one can stop her....”
“Ka shige nace kafin na maka baki...”
Duban mahaifiyar tasa kurum yai had’ida girgiza kai kana ya fice yabi bayan Siyama...
Ya maido da dubantaga mijinta wanda ta koma masa tamkar TV kana tace “One of these days d’aya daga cikin yaranka zasu sakamin hawan jini, wani irin musifa ne wannan ace yara duk sun haukace kan dangin mayu, da ina tunanin Khalid ne kawai iftila’in ya auka masa ashe harda Siyamar kanta, yo na Siyama ma ai shine babban tashin hankali tinda an riga anyi aure, Toh wllhi ko ina mutuwa ina tashuwa ne bazan bari Khalid ya auri yarinyar can ba, kuma Siyamar ma ko kotun k’oli zamu tafi wllhi sai Sameer ya sakar min d’iyata don bazan tab’a had’a iri da dangin tsiya ba ehe....”
Tana ida fad’in haka tasa kai ta fice fuuuu tana k’walla kiran yaran nata....
Birki tai a d’ari sakamakon hango Siyama da tai cikin mota Khalid na tsaye gaban motar tana fad’in ko ya kauce mata a hanya ko tabi takansa.....
Ammi ta isa jikin motar a guje tana fad’in “Nafa fad’a maki babu ke babu tsinannen yaron nan ki fito a motar nan Siyama....”
Siyama fad’i take “Ammi idan sama da k’asa zasu had’e Wllhi baki isa ki rabani da Partner ba, kuma wllhi yanzu ba sai anjima ba zan tafi na soma yak’in raba mijina da wad’ancan jarababbun.....”
Khalid fad’i yake “Siyama calm down, ki bari abi komai a sannu, ki sauk’o ayi magana ta nutsuwa babu wanda zai rabaki da mijinki amma hanyar da kika d’auko ba mai b’ullewa bace just calm down first....”
Bai rufe baki ba Siyama ta kuma baiwa mota wuta alamun batada niyan fasa abinda tai niyya... Gani zatabi kan Ammi yasa Khalid saurin janyo mahaifiyarsu gefe dake kururwa Siyama kaw taja mota ta fice a guje k’iris ya rage bata had’ada security mai bud’e mata gate d’inba
Ammi hannu aka take furta “Na shiga uku na lalace ni Farida mi nayima yaran nan suka zab’i wasu tsinannu kwashesu sama da mahaifiyarsu.....” Ta shiga rera kuka bataji bata gani, da k’yar Khalid ya iya janyota ya shigar da ita cikin gida....
***
Akram na risine gabansa ya ida amsa wayar da yake, saida ya d’an b’ata lokaci yana duba abu cikin wayar kana yace “Ina saurarenka...”
D’an gyara zamansa Akram yai kana yace “Mun gana da ita yarinyar jiya, kuma na sanar da ita abinda ke tafe damu, and daga dukkan alamun mun samu goyon bayan K’anwar mahaifiyar tata wacce take zaune gabanta, amma your Excellency wani hanzari ba gudu ba....”
Engr ya gyara zamansa kana yace “Umhum go ahead ina saurarenka...”
Akram ya kuma d’an turowa daga cikin kujeran kansa a k’asa kana yaci gaba da fad’in “Sir, ina ganin zaifi kyau idan baka bayyana mata kanka a halin yanzu ba, ma’ana naci gaba da isar mata sak’onka zuwa nan da d’an wani lokaci sabida tsohon mijinta yanada matsalan tab’in k’wak’walwa kuma Sir a matsayin da kake idan kowa yasan cewa kai kake nemanta wannan tsohon mijin nata can cause a biggest scandal for us, ni kuma hakkinane na kare reputation d’inka and your career in politics kasan abokan hamayya k’iris suke jira Rankashi dad’e...”
Shiru yai yana nazarin maganganun Akram d’in kana yace “Haka ne Akram.... Kayi daidai, hakan yayi... Bansan da mai zan biyaka ba bayan duk abubuwan da kake min.... Hak’ika ka cika d’anuwa na k’warai....”
Ba Siyama datayi mutuwar tsaye ba harta Ammi neman yawun bakinta tai ta rasa balle tai tunanin kalamai ka iya zuwa kan harshen ta....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*73*
Girgiza kai Siyama take cikin rashin yarda da abinda kunnuwanta ke jiyo mata, lokaci guda ta kamo hannayen Khalid tana mai furta “Khalid tell me this isn’t true.... Wasa kakemin koh, babu abinda ya had’a Sameer da wad’annan mutanen.... Tell me you’re just joking...”
Fincikar hannayensa yai kana yace “Since when muka soma wannan wasar dake abinda kikaji gaskiya ne Nabilah k’anwar mijinki ne....!”
“What was that...?” Muryar Daddy ya katsesu..... Lokaci guda Ammi dake faman girgiza kai itama cikin rashin yarda ta shiga furta “Karka sauraresa, shak’iyancin Khalid ne kawai ya motsa don an hanasa auran yarinyar shine bari ya dangantata da Sameer, yo ina Sameer ina zuri’ar yarinyar can dangin mayu.... Kai ko a halitta Sameer yayi kama da wad’ancan mutanen ne.... Wllhi k’arya yake tsantsan Daddyn Siyaaam kar ka yarda dashi.....”
Siyama dake tsananin kuka kuma janyo hannayen Khalid tai tana jijjigawa da iyakan k’arfinta take fad’in “Khalid tell me is isn’t true... Ka fad’a min k’arya kake...!!!!” Ta k’arashe cikin tsananin d’aga murya....
Daddy ne ya k’araso ya janye hannayen Siyama daga na Khalid yana mai k’ok’arin kwantarwa Siyamar hankali....
Cikin kuka Siyama ke furta “Daddy Wllhi k’arya ne, of all people those people can’t be my husband’s family.... Daddy not my Sameer....” Ta k’arashe cikin shesshek’ar kuka....
Duban Khalid dake faman watsama Siyama muguwar kallo Daddy yai kana yace “Khalid..!”
D’ago kai Khalid yai ya dube mahaifin nasa had’ida furta “Na’am Daddy..” lokaci guda yaci gaba da furta “Ka sameni a parlor na...”
Babu musu Khalid ya jinjina kai kana yabi bayan Daddyn yana mai watsawa Siyama da Ammi ke tausanta harara....
Daga can gefen k’afan mahaifin nasa ya zauna had’ida risinawa kana yace “Daddy barkada gida, ina yini....”
Amsa masa mahaifin nasa yai kana yai gyaran murya ya soma fad’in “Khalid maike faruwa...? Shin abinda naji kana fad’i gaskiya ne cewa yarinyar can k’anwar mijin Siyama ne....?”
Jinjina masa kai Khalid yai had’ida gyara zamansa kana yace “Daddy abinda kaji gaskiya ne, Nabila k’anwar Sameer ne, recently Sameer ya sami biological parents d’insa, and it happens to be Nabilah k’anwarsa ce Daddy... Wato Daddy akwai abubuwa da dama da suke faruwa a gidan nan wanda sam basa dacewa tin daga kan yanda ake gudanar da al’amran gidan nan... Daddy ba wai ina fad’in gazawarku bane a matsayinku na wad’anda hakkin kula da tarbiyan gidan nan ya rataya a wuyarsu bane most especially you Daddy... Amma maganar gaskiya fah Daddy kuskuren tin daga sama ne, ya samo asali ne daga wajenka, ka baiwa Ammi wani irin power a gidan nan wanda sai abinda taga dama akeyi, Daddy I’m not saying baiwa matarka dama da freedom kuskure bane, but Daddy everything has a limit, ina ganin a matsayinka na shugaba a gida ya kamata ka zama kaikeda final say matuk’ar bai kaucewa Shari’a ba, Daddy karfa ka mance Allah da kansa ya gargade masu imani cewa su tsare kawunansu da iyalansu daga shiga wuta, shin Daddy mecece makomar gidan nan...? Yanzu ga Siyama a gida itama bata d’auki auren da daraja ba balle mijinta sabida abinda ta taso taga akeyi kenan a gidansu, turbar da mahaifiyarta ta d’aurata bisa kenan... Sam Ammi da Siyama basu d’auki d’an adam da wata daraja ba idanba wanda suke so bane... After what she’s done a gidansu Sameer bansan da wasu idanu zata dubesu matsayin sirakanta ba, Daddy mai ya haifar da haka...? Rashin samun wadataccen tarbiya ne tin daga fari shi ya haifar da haka.... Opinion d’in kowa a gidan nan baida daraja idandai ba daga Siyama ya fito ba, Ammi bata d’aukan maganan kowa ko shawarin kowa saina Siyama, and Daddy kaikuma duk abinda Ammi ta fad’i a gidan nan shikenan daidaine kayi na’am dashi without overlooking it... Daddy please ya kamata a daina irin wannan rayuwar a gidan nan, a duba lamarin Daddy.....” Ya k’arashe cikin tsananin k’ank’an da kai da kuma murya....
Shiru ya gifta tsakaninsu tamkar mahaifin nasa bazaice komai ba, saima d’aura hab’arsa da yayi saman hannayensa guda biyu da ya dunk’ule waje guda....
Muryar Ammi ce ya katse shirun da ya ratsa cikin parlorn...
“Toh wllhi ba k’anwar Sameer ba, yau idan uwar Sameer ce wannan yarinyar babu abinda ya shalleni, wllhi bazaka aureta ba muddin ina numfashi, yo sai mai... Allah ya kiyayeni na had’a jini da matsiyata, kuma shima Sameer d’in sai ya sakar min d’iyata, wllhi bazata zauna dashi ba, naji dad’i da rabo bai tsaga tsakaninsu ba, rabuwa ya zama dole, gwara da Allah ya bayyana mana....” Bata ida maganar nata ba Siyama ta shigo tana kuka tana fad’in “Ammi wllhi bazan rabu da mijina ba.... Gaskiya ni bazan iya rabuwa da Sameer ba don wllhi ina sonshi ina k’aunarshi har kwanan gobe, Sameer is nothing like his family, tsautsayi ne da k’addara yasa suka zama danginsa, kuma ma ai su Mummy ne iyayensa shida wad’ancan mayun jini ne kawai ya had’su, but his real family are here.... So Ammi don’t think of separating us... Nida Sameer are magnets babu wanda ya isa ya rabamu not even his so called new family, yanzu zan tafi ba sai anjima ba, yanzu zan koma to win my husband back don ya zama dole na rabasa da wad’ancan annoban....!” Tana ida fad’in haka ta fice fuuuu Ammi na k’walla mata kira ko saurarenta bata tsayayi ba...
Ammi ta maidoda dubantaga Daddy tana fad’in “Daddyn Siyaam kaga fah tafiya zatayi, kayiwa Allah ka dakatar da ita kartaje su lashe min ita kaman yanda suka lashe Khalid...” Ganin bai amsata ba ya sanyata janyo Khalid tana fad’in “Tashi tashi wuce maza ka k’wato min car keys d’inta...” Khalid na tirjewa Ammi na turasa, fad’i yake “Ammi kinsan Siyama idan tayi niyyan abu no one can stop her....”
“Ka shige nace kafin na maka baki...”
Duban mahaifiyar tasa kurum yai had’ida girgiza kai kana ya fice yabi bayan Siyama...
Ya maido da dubantaga mijinta wanda ta koma masa tamkar TV kana tace “One of these days d’aya daga cikin yaranka zasu sakamin hawan jini, wani irin musifa ne wannan ace yara duk sun haukace kan dangin mayu, da ina tunanin Khalid ne kawai iftila’in ya auka masa ashe harda Siyamar kanta, yo na Siyama ma ai shine babban tashin hankali tinda an riga anyi aure, Toh wllhi ko ina mutuwa ina tashuwa ne bazan bari Khalid ya auri yarinyar can ba, kuma Siyamar ma ko kotun k’oli zamu tafi wllhi sai Sameer ya sakar min d’iyata don bazan tab’a had’a iri da dangin tsiya ba ehe....”
Tana ida fad’in haka tasa kai ta fice fuuuu tana k’walla kiran yaran nata....
Birki tai a d’ari sakamakon hango Siyama da tai cikin mota Khalid na tsaye gaban motar tana fad’in ko ya kauce mata a hanya ko tabi takansa.....
Ammi ta isa jikin motar a guje tana fad’in “Nafa fad’a maki babu ke babu tsinannen yaron nan ki fito a motar nan Siyama....”
Siyama fad’i take “Ammi idan sama da k’asa zasu had’e Wllhi baki isa ki rabani da Partner ba, kuma wllhi yanzu ba sai anjima ba zan tafi na soma yak’in raba mijina da wad’ancan jarababbun.....”
Khalid fad’i yake “Siyama calm down, ki bari abi komai a sannu, ki sauk’o ayi magana ta nutsuwa babu wanda zai rabaki da mijinki amma hanyar da kika d’auko ba mai b’ullewa bace just calm down first....”
Bai rufe baki ba Siyama ta kuma baiwa mota wuta alamun batada niyan fasa abinda tai niyya... Gani zatabi kan Ammi yasa Khalid saurin janyo mahaifiyarsu gefe dake kururwa Siyama kaw taja mota ta fice a guje k’iris ya rage bata had’ada security mai bud’e mata gate d’inba
Ammi hannu aka take furta “Na shiga uku na lalace ni Farida mi nayima yaran nan suka zab’i wasu tsinannu kwashesu sama da mahaifiyarsu.....” Ta shiga rera kuka bataji bata gani, da k’yar Khalid ya iya janyota ya shigar da ita cikin gida....
***
Akram na risine gabansa ya ida amsa wayar da yake, saida ya d’an b’ata lokaci yana duba abu cikin wayar kana yace “Ina saurarenka...”
D’an gyara zamansa Akram yai kana yace “Mun gana da ita yarinyar jiya, kuma na sanar da ita abinda ke tafe damu, and daga dukkan alamun mun samu goyon bayan K’anwar mahaifiyar tata wacce take zaune gabanta, amma your Excellency wani hanzari ba gudu ba....”
Engr ya gyara zamansa kana yace “Umhum go ahead ina saurarenka...”
Akram ya kuma d’an turowa daga cikin kujeran kansa a k’asa kana yaci gaba da fad’in “Sir, ina ganin zaifi kyau idan baka bayyana mata kanka a halin yanzu ba, ma’ana naci gaba da isar mata sak’onka zuwa nan da d’an wani lokaci sabida tsohon mijinta yanada matsalan tab’in k’wak’walwa kuma Sir a matsayin da kake idan kowa yasan cewa kai kake nemanta wannan tsohon mijin nata can cause a biggest scandal for us, ni kuma hakkinane na kare reputation d’inka and your career in politics kasan abokan hamayya k’iris suke jira Rankashi dad’e...”
Shiru yai yana nazarin maganganun Akram d’in kana yace “Haka ne Akram.... Kayi daidai, hakan yayi... Bansan da mai zan biyaka ba bayan duk abubuwan da kake min.... Hak’ika ka cika d’anuwa na k’warai....”