Sashe 68
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aiko yana sako hancin motar cikin gidan yayi arban da taron mutanen nasu, wasu sun shige mota wasu suna tsartsaye cirko cirko a farfajiyan hamshak’in gidan, da yawan mutanen suna mamakin yanda idan za’ai fita ko taron siyasa koma abinda bai shafi siyasa ba yanda duk kaga Engr Mutallab toh fah sai kaga Akram, koda baya nan kuwa sai an jirashi, bai yarda da tuk’in kowa face na Akram, Akram ya zamto tamkar k’ani a gareshi, harta zumunta mai k’arfi saida iyayen Akram suka k’ulla da Mutallab.... Da yawan mutane sunso shiga tsakaninsu saidai Allah bai k’addara hakan ba....
A daidai k’ofar babban parlornsa suka had’u...
Akram na sadda kai k’asa yake fad’in “A min afuwa your excellency....”
Engr ya d’an girgiza kai kurum kana yace “Amma sanin kanka ne African time bashi a tsarina, sannan idan nayi alk’awariwa mutane cewa lokaci kaza zanzo toh ko dak’ik’a guda banson k’arawa.... I suppose kasan duka wad’annan by now.....”
Kai a k’asa Akram yace “I’m very sorry your excellency uziri ne ya rik’eni amma In sha Allah hakan bazata kuma faruwa ba...”
D’an girgiza kai kurum yai kana yace ”A dinga kiyayewa....”
Cikin sauri Akram ya take masa baya yana fad’in “In sha Allah...”
A haka suka nufi mota sauran jama’an na hangosu kowa ya mik’e suka nufi nasu motocin....
Suna tafe Engr Ma’aruf na hankalce da Akram, agogon jikin motar ya kalla ya kuma duba wanda ke d’aure tsintsiyar hannunsa, tabbas lokacin gudanar da shirin ne... Ya kai duban sa ga radio din jikin motar da alama yau dai Akram mancewa yayi qilan, samun kansa yayi da kai hannun sa jikin radio d’in motar ya murd’ata....
Akram ya d’an dubeshi cikeda mamaki sanin cewa maigidan nashi ba ma’abocin sauraren radio bane hasalima a baya ko kunna radio din motar baiyi saiko kira’a....
Jin bai kamo channel d’in ba yasa shi d’an duban Akram....
Cikin sauri Akram ya rage speed kana ya d’an dubi maigidan nasa, ya gane tashar Radio ‘Yanci yake nema, baiyi zaci Ubangidan nasa har ya zama attached to shirin ba, ya saki murmushi a hankali kana ya d’anyi gyaran murya yace “Ai kwana biyu ba’a gudanar da shirin sabida wacce ke gudanarwa anyi mata rasuwa, hasalima uzurin da ya rik’eni ta’aziya mukaje mukai mata....”
Engr Mutallab ya dubesa da mamaki kana yace “Anyi mata rashi....?”
Akram ya jinjina kai a hankali yace “Eh ranka shi dad’e d’iyarta ta rasu yau kwana uku kenan....”
_D’iyarta_ Kalmar da Engr ya nanata cikin zuciyarsa, bai tab’a kawowa tana da aure ba, a hankali ya maida duban sa ga window ba tareda ya kuma cewa komai ba... Akram ya d’an dube sa ba tareda yace komai ba, lokaci guda ya kunna masu k’ira’an Alk’ur’ani mai girma cikin muryar marigayi Sheik Jabir....
***
KADUNA
Yau kwanan sa uku a hotel d’in duk wasu savings d’insa ya k’aryar dole ya nemi kudi ya biya kudin d’aki sannan yaci abinci.... Drawer dake gefen gadon ya janyo ya ciro wallet d’insa ya zari credit card dinsa guda da bai baiwa Daddy ba a cewarsa wannan account d’in tsohuwar account d’insa ne babu kwabon Companyn mahaifinsa a ciki....
K’asa ya sauk’o domin yin payment saidai to his greatest surprise Card d’in was declined.... Mamaki ya cika Khalid bai tsamman Mahaifin sa nada access to wannan account d’in ba... Girgiza kai yayi don yasan wannan bazai wuce aikin Siyama ba....Wato dai shi har yanzu a gidan kallon yaro ake masa.... Fuzar da iska ya d’anyi had’i da shafa sumar sa kafin ya amshi card d’insa, idan bai biya ba k’arshe dai dole ya bar hotel d’in don ba barinsa zasuyi ya zauna a bati ba.... Ba don yaso ba ya shiga neman layin Baffah....
Baffah na parlorn Ammi tare da su Siyama suna tattauna lamarin wayar Khalid ya shigo masa.....
D’agowa Baffah yai yana dubansu bayan ya dubi screen d’in kana yai murmushi yace “Kun ganshi nan na kira....”
Ammi tai saurin cewa “D’aga d’aga muji mai zaice....”
Baffah ya jinjina kai kana ya d’aga wayar
Daga d’aya b’angaren Khalid yace “Kana ina ne...?”
“Gida.... Why..?” Baffah ya fad’i a tak’aice
“Can you come over to the hotel please....?” Khalid ya fad’i tamkar wanda baison maganar...
Baffah ya dubesu su d’inma shi suke duba da shike a speaker ya saka wayar... Siyama ta masa ido kan yaci gaba da magana...
Baffah yace “Mai kuma zan maka...?”
Gajeren tsaki Khalid yai kana yace “Idan ba zaka zo ba just tell me na nemi hanyar fita before they kick me out... I can’t believe Daddy can go this far... He canceled all of my cards, I can’t even have access to account d’in da nake da tabbacin baida masaniya da ita....”
Mik’ewa Baffah yayi yana fad’in “Alright alright gani nan zuwa....”
Yana katse kiran Ammi tace maza yaje sa ya duba halin da Khalid d’in ke ciki idan akwai debts sai ya clearing ..... Siyama ta saka shewa tana fad’in “Ammi kin gani ko plan d’in yayi aiki yanzu dole Khalid ya dawo gida tinda baida zab’i....”
Ammi ta murmusa kana tace “Ai gwara da aka saka masa pressure na tabbata yanzu zai nemi hanyar gida.....
Yesmin harda mik’ewa tsaye tana tik’a tsallen murna...
Ammi ta yab’e baki tace “Ke kuma meye haka god’e god’e....”
Yesmin ta cuno baki tace “Kai Ammi, ai dai murna nake at last my Kay zai dawo....”
Ammi batace komai ba sai tab’e baki da tayi kana ta mik’e ta nufi upstairs ...
Siyama na dariya tace da Yesmin... “Kinga zama bata kamamu ba, get me my car keys upstairs...”
Da mamaki Yesmin tace “Ina kuma zamu....?”
Siyama ta murmusa tace “of course we’re gonna follow Baffah.... Kinga yi sauri kafin ya fice....”
Yesmin ta dara cike da jin dad’in kana ya nufi upstairs kaman zata kifa.... Sauri sauri motarsu tabi bayan ta Baffah....
Baffah ne ya gama settling bills d’in Khalid d’in gaba d’aya a counter, ba tare da ya dubi Khalid d’in da tun fitowar su ke duban wani gefen ba ya nufi room d’in Khalid d’in, tattare suitcases d’insa da duk wani belonging d’insa ya dingayi without any hesitation.... Nan ya hangi cellphone d’insa saman gado... Ya d’auka da sauri ya shiga trying nan ya samu tana bud’e, kai tsaye contacts ya shiga yana duba weird suna don yasan yanda abokin nasa yake weirdo haka zai saving lambar Nabila....
Teddy bear ya gani harda hoton bear... Baffah ya girgiza kai had’ida murmusawa a fili ya furta “If not Khalid Mainasara who...?”
Cikin sauri yayi copying lambar Nabilah kana ya fito janye da suitcases d’in.. Kai tsaye ya shige yana mai mik’awa receptionist d’an mabud’in....
Khalid ya tsaresa da kallon mamaki
“Ina kake tunanin zanje....?” Ya tambaya yana duban Baffan....
Janyo sa Baffah ya shigayi da d’aya hannun yana fad’in “You need to end this nonsense right now...”
Ya bud’e mota yana k’ok’arin danna kansa ciki Khalid yace “Ba abinda na kira ka kamin ba kenan, thanks for helping out, but I’m not going back to house.....”
Yanda yayi maganar kana iya hango tsantsan kafiyar sa...
Su Siyama da motarsu ke lab’e gefe suka dubi juna...
Suna gani Khalid yasa kai zai shige ya bar Baffah nan tsaye...
Cikin sauri Siyama taiwa Baffan idanu cewa yabi bayanshi...
Aiko tuni ya soma binsa yana bashi hak’uri yana rok’on sa ya shiga mota su tafi..
Da sharad’in bazai kaisa gidan mahaifinsa ba ya shige motar Baffah, basu zarce ko ina ba sai gidansu Baffan, nan ma bai yarda ya bari mahaifiyar Baffan tasan da zuwan sa don kai tsaye sashen Baffan ya wuce kuma yace baiso kowa yasan da zuwansa..
Hankalin Siyama ya d’an kwanta ganin gidans u Baffah ya koma, Yesmin kam ba haka taso ba taso ya koma gida don tayi kewar sa sosai dukda ba shiga hark’arta yake ba...
***
Kano
Sanye yake cikin pajamas d’insa autarsa Najma na kwance gefe saman makeken gadon nasa na alfarma, shiru yayi had’da k’urama waje guda idanu, zancensu da Akram na kuma dawowa kwanyarsa, akwai tambayoyi da dama da yakeso yayiwa Akram gameda ita.... But what if she’s really a married woman...? Ya lumshe idanu a hankali had’ida furta istigfari a fili... Baisan dalili ba, sau d’aya tak ya saurari program d’inta amma muryarta ya kasa b’acewa daga kwanyar sa, shi ba ma’abocin sauraren radio ba amma rana guda tak da ya saurari shirinta yaji yana son sake saurara, maybe sabida itama tana supporting d’insa ne, maybe program d’in yake son sake saurare ba muryar ta ba, da wannan tunanin yaji ya d’an sami natsuwa cikin zuciyarsa...
Ya karanto addu’a ya tofawa d’iyarsa yana k’ok’arin kwanciya kenan ta turo k’ofa ta shigo...
Ko kallon arziki bata ishesa ba ya juya yayi kwanciyarsa....
Tsegege ta tsaya masa aka tana faman huci...
“Engr....”
Shiru bai amsata ba
“Ma’aruf...”
Nanma shiru bai amsata ba idanunsa a lumshe...
Tasan weakness d’in mijin nata idan akwai abinda ke saurin raunanasa shine yaji mace na kuka, kai shi kuka entirely d’aga masa hankali yake... Take Muhibba ta fashe da kuka had’ida silalewa k’asa...
Ya bud’e idanu a hankali ya sauk’esu kanta, fuskar sa ya d’aura saman hannayen sa guda biyu ba tareda yace da ita komai ba....
Muhibba ta kannare idanu taga ya tashi ya zauna nan ta kuma narkewa tana shak’an kuka...
Kukan nata ya shiga d’aga masa hankali...
Shafe kansa ya shigayi yana furta “That’s enough Muhibba... Ya isa haka nan....”
Haba nan fah ta kuma narkewa...
Engr ya fuzar da iska a hankali kana yakai hannu a hankali ya dafata yana k’ok’arin lallashinta don ya gaji da sauraren kukan nata...
Tamkar wacce take jira ta rungumesa gaba d’aya had’ida kwantawa cikin jikinsa zuciyarta na mata fari don tabi shawarin k’wayenta gwara ta lallab’a mijinta su shirya kar azo a kafa gwamnati yayi aure ya watsar da ita wata tazo ta zama First Lady tana nan ita kuma ta koma ‘yar kallo a cikin gidanta, wata tazo ta rabata dashi da kuma yaranta da tayi imani sune rayuwarsa....
***
A tare Abbah da Sameer suka shigo d’akin da sallama saman bakunan su, Raiha na kwance tana shan fruits da Mamani ta yanka mata an ida mata dressing kenan Sister Salma nurse dake mata dressing ko yaushe...
A daidai k’ofar babban parlornsa suka had’u...
Akram na sadda kai k’asa yake fad’in “A min afuwa your excellency....”
Engr ya d’an girgiza kai kurum kana yace “Amma sanin kanka ne African time bashi a tsarina, sannan idan nayi alk’awariwa mutane cewa lokaci kaza zanzo toh ko dak’ik’a guda banson k’arawa.... I suppose kasan duka wad’annan by now.....”
Kai a k’asa Akram yace “I’m very sorry your excellency uziri ne ya rik’eni amma In sha Allah hakan bazata kuma faruwa ba...”
D’an girgiza kai kurum yai kana yace ”A dinga kiyayewa....”
Cikin sauri Akram ya take masa baya yana fad’in “In sha Allah...”
A haka suka nufi mota sauran jama’an na hangosu kowa ya mik’e suka nufi nasu motocin....
Suna tafe Engr Ma’aruf na hankalce da Akram, agogon jikin motar ya kalla ya kuma duba wanda ke d’aure tsintsiyar hannunsa, tabbas lokacin gudanar da shirin ne... Ya kai duban sa ga radio din jikin motar da alama yau dai Akram mancewa yayi qilan, samun kansa yayi da kai hannun sa jikin radio d’in motar ya murd’ata....
Akram ya d’an dubeshi cikeda mamaki sanin cewa maigidan nashi ba ma’abocin sauraren radio bane hasalima a baya ko kunna radio din motar baiyi saiko kira’a....
Jin bai kamo channel d’in ba yasa shi d’an duban Akram....
Cikin sauri Akram ya rage speed kana ya d’an dubi maigidan nasa, ya gane tashar Radio ‘Yanci yake nema, baiyi zaci Ubangidan nasa har ya zama attached to shirin ba, ya saki murmushi a hankali kana ya d’anyi gyaran murya yace “Ai kwana biyu ba’a gudanar da shirin sabida wacce ke gudanarwa anyi mata rasuwa, hasalima uzurin da ya rik’eni ta’aziya mukaje mukai mata....”
Engr Mutallab ya dubesa da mamaki kana yace “Anyi mata rashi....?”
Akram ya jinjina kai a hankali yace “Eh ranka shi dad’e d’iyarta ta rasu yau kwana uku kenan....”
_D’iyarta_ Kalmar da Engr ya nanata cikin zuciyarsa, bai tab’a kawowa tana da aure ba, a hankali ya maida duban sa ga window ba tareda ya kuma cewa komai ba... Akram ya d’an dube sa ba tareda yace komai ba, lokaci guda ya kunna masu k’ira’an Alk’ur’ani mai girma cikin muryar marigayi Sheik Jabir....
***
KADUNA
Yau kwanan sa uku a hotel d’in duk wasu savings d’insa ya k’aryar dole ya nemi kudi ya biya kudin d’aki sannan yaci abinci.... Drawer dake gefen gadon ya janyo ya ciro wallet d’insa ya zari credit card dinsa guda da bai baiwa Daddy ba a cewarsa wannan account d’in tsohuwar account d’insa ne babu kwabon Companyn mahaifinsa a ciki....
K’asa ya sauk’o domin yin payment saidai to his greatest surprise Card d’in was declined.... Mamaki ya cika Khalid bai tsamman Mahaifin sa nada access to wannan account d’in ba... Girgiza kai yayi don yasan wannan bazai wuce aikin Siyama ba....Wato dai shi har yanzu a gidan kallon yaro ake masa.... Fuzar da iska ya d’anyi had’i da shafa sumar sa kafin ya amshi card d’insa, idan bai biya ba k’arshe dai dole ya bar hotel d’in don ba barinsa zasuyi ya zauna a bati ba.... Ba don yaso ba ya shiga neman layin Baffah....
Baffah na parlorn Ammi tare da su Siyama suna tattauna lamarin wayar Khalid ya shigo masa.....
D’agowa Baffah yai yana dubansu bayan ya dubi screen d’in kana yai murmushi yace “Kun ganshi nan na kira....”
Ammi tai saurin cewa “D’aga d’aga muji mai zaice....”
Baffah ya jinjina kai kana ya d’aga wayar
Daga d’aya b’angaren Khalid yace “Kana ina ne...?”
“Gida.... Why..?” Baffah ya fad’i a tak’aice
“Can you come over to the hotel please....?” Khalid ya fad’i tamkar wanda baison maganar...
Baffah ya dubesu su d’inma shi suke duba da shike a speaker ya saka wayar... Siyama ta masa ido kan yaci gaba da magana...
Baffah yace “Mai kuma zan maka...?”
Gajeren tsaki Khalid yai kana yace “Idan ba zaka zo ba just tell me na nemi hanyar fita before they kick me out... I can’t believe Daddy can go this far... He canceled all of my cards, I can’t even have access to account d’in da nake da tabbacin baida masaniya da ita....”
Mik’ewa Baffah yayi yana fad’in “Alright alright gani nan zuwa....”
Yana katse kiran Ammi tace maza yaje sa ya duba halin da Khalid d’in ke ciki idan akwai debts sai ya clearing ..... Siyama ta saka shewa tana fad’in “Ammi kin gani ko plan d’in yayi aiki yanzu dole Khalid ya dawo gida tinda baida zab’i....”
Ammi ta murmusa kana tace “Ai gwara da aka saka masa pressure na tabbata yanzu zai nemi hanyar gida.....
Yesmin harda mik’ewa tsaye tana tik’a tsallen murna...
Ammi ta yab’e baki tace “Ke kuma meye haka god’e god’e....”
Yesmin ta cuno baki tace “Kai Ammi, ai dai murna nake at last my Kay zai dawo....”
Ammi batace komai ba sai tab’e baki da tayi kana ta mik’e ta nufi upstairs ...
Siyama na dariya tace da Yesmin... “Kinga zama bata kamamu ba, get me my car keys upstairs...”
Da mamaki Yesmin tace “Ina kuma zamu....?”
Siyama ta murmusa tace “of course we’re gonna follow Baffah.... Kinga yi sauri kafin ya fice....”
Yesmin ta dara cike da jin dad’in kana ya nufi upstairs kaman zata kifa.... Sauri sauri motarsu tabi bayan ta Baffah....
Baffah ne ya gama settling bills d’in Khalid d’in gaba d’aya a counter, ba tare da ya dubi Khalid d’in da tun fitowar su ke duban wani gefen ba ya nufi room d’in Khalid d’in, tattare suitcases d’insa da duk wani belonging d’insa ya dingayi without any hesitation.... Nan ya hangi cellphone d’insa saman gado... Ya d’auka da sauri ya shiga trying nan ya samu tana bud’e, kai tsaye contacts ya shiga yana duba weird suna don yasan yanda abokin nasa yake weirdo haka zai saving lambar Nabila....
Teddy bear ya gani harda hoton bear... Baffah ya girgiza kai had’ida murmusawa a fili ya furta “If not Khalid Mainasara who...?”
Cikin sauri yayi copying lambar Nabilah kana ya fito janye da suitcases d’in.. Kai tsaye ya shige yana mai mik’awa receptionist d’an mabud’in....
Khalid ya tsaresa da kallon mamaki
“Ina kake tunanin zanje....?” Ya tambaya yana duban Baffan....
Janyo sa Baffah ya shigayi da d’aya hannun yana fad’in “You need to end this nonsense right now...”
Ya bud’e mota yana k’ok’arin danna kansa ciki Khalid yace “Ba abinda na kira ka kamin ba kenan, thanks for helping out, but I’m not going back to house.....”
Yanda yayi maganar kana iya hango tsantsan kafiyar sa...
Su Siyama da motarsu ke lab’e gefe suka dubi juna...
Suna gani Khalid yasa kai zai shige ya bar Baffah nan tsaye...
Cikin sauri Siyama taiwa Baffan idanu cewa yabi bayanshi...
Aiko tuni ya soma binsa yana bashi hak’uri yana rok’on sa ya shiga mota su tafi..
Da sharad’in bazai kaisa gidan mahaifinsa ba ya shige motar Baffah, basu zarce ko ina ba sai gidansu Baffan, nan ma bai yarda ya bari mahaifiyar Baffan tasan da zuwan sa don kai tsaye sashen Baffan ya wuce kuma yace baiso kowa yasan da zuwansa..
Hankalin Siyama ya d’an kwanta ganin gidans u Baffah ya koma, Yesmin kam ba haka taso ba taso ya koma gida don tayi kewar sa sosai dukda ba shiga hark’arta yake ba...
***
Kano
Sanye yake cikin pajamas d’insa autarsa Najma na kwance gefe saman makeken gadon nasa na alfarma, shiru yayi had’da k’urama waje guda idanu, zancensu da Akram na kuma dawowa kwanyarsa, akwai tambayoyi da dama da yakeso yayiwa Akram gameda ita.... But what if she’s really a married woman...? Ya lumshe idanu a hankali had’ida furta istigfari a fili... Baisan dalili ba, sau d’aya tak ya saurari program d’inta amma muryarta ya kasa b’acewa daga kwanyar sa, shi ba ma’abocin sauraren radio ba amma rana guda tak da ya saurari shirinta yaji yana son sake saurara, maybe sabida itama tana supporting d’insa ne, maybe program d’in yake son sake saurare ba muryar ta ba, da wannan tunanin yaji ya d’an sami natsuwa cikin zuciyarsa...
Ya karanto addu’a ya tofawa d’iyarsa yana k’ok’arin kwanciya kenan ta turo k’ofa ta shigo...
Ko kallon arziki bata ishesa ba ya juya yayi kwanciyarsa....
Tsegege ta tsaya masa aka tana faman huci...
“Engr....”
Shiru bai amsata ba
“Ma’aruf...”
Nanma shiru bai amsata ba idanunsa a lumshe...
Tasan weakness d’in mijin nata idan akwai abinda ke saurin raunanasa shine yaji mace na kuka, kai shi kuka entirely d’aga masa hankali yake... Take Muhibba ta fashe da kuka had’ida silalewa k’asa...
Ya bud’e idanu a hankali ya sauk’esu kanta, fuskar sa ya d’aura saman hannayen sa guda biyu ba tareda yace da ita komai ba....
Muhibba ta kannare idanu taga ya tashi ya zauna nan ta kuma narkewa tana shak’an kuka...
Kukan nata ya shiga d’aga masa hankali...
Shafe kansa ya shigayi yana furta “That’s enough Muhibba... Ya isa haka nan....”
Haba nan fah ta kuma narkewa...
Engr ya fuzar da iska a hankali kana yakai hannu a hankali ya dafata yana k’ok’arin lallashinta don ya gaji da sauraren kukan nata...
Tamkar wacce take jira ta rungumesa gaba d’aya had’ida kwantawa cikin jikinsa zuciyarta na mata fari don tabi shawarin k’wayenta gwara ta lallab’a mijinta su shirya kar azo a kafa gwamnati yayi aure ya watsar da ita wata tazo ta zama First Lady tana nan ita kuma ta koma ‘yar kallo a cikin gidanta, wata tazo ta rabata dashi da kuma yaranta da tayi imani sune rayuwarsa....
***
A tare Abbah da Sameer suka shigo d’akin da sallama saman bakunan su, Raiha na kwance tana shan fruits da Mamani ta yanka mata an ida mata dressing kenan Sister Salma nurse dake mata dressing ko yaushe...