Sashe 58
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Su Hajiya suna hango shi yayi tsaye suka nufi kansa suna tambayarsa Hajiya na fad’in “Likita ina jikata...? Ka fad’a mini ina tak...?” Muryar Hajiya ya sark’e sanda tai idanu hud’u da mutumin da ya bayyana gabanta matsayin likita, zuciyarta ta shiga harbawa da sauri, tsoro da firgici suka bayyana mata.... Ta soma tunanin kodai Ma’aruf gizo yake mata... Tsananin tashin hankali ya wanzu a tattareda Hajiya... Idanu hud’u sukai itada Aunty Lami wacce itama hakance ta kasance da ita, ko shakka babu su biyun suna buk’atar keb’ewa su tattauna lamarin Ma’aruf wanda ke barazanar tarwatsa masu rayuwa...
Maganganun Hajiya ya dawo da hankulansu, gaba d’aya kallon sani suke masa... Sahariyya kaw tuni jikinta ya d’au rawa har ta mance mai ya kawosu asibitin ta shiga bin Sameer da mayen kallo tana yank’are baki had’ida komad’a ita kad’ai... Tabbas ba gizo yake mata ba wannan na nuni da alamun cewa shid’in nata ne da sannu zai zama rabonta tinda gashi Allah ya kuma had’asu, ita kad’ai sai sakin murmushi take tamkar tab’ebb’iya...
Zulfa’u tai k’arfin halin maimaita tambayarta “Dr how’s my daughter.... How’s she doing.... Ina take dan Allah.. Shin zamu iya ganinsu...?”
D’an jim Sameer yayi ba tareda ya iya furta koda kalma ba sai kallo da yake bin Zulfa’u dashi yana hango wasu abubuwa nasu dake yanayi...
Cikin hawaye tana mai goge fuskarta take fad’in “Dr kamin magana dan Allah... Kace wani abu.... kace zamu iya shiga mu gansu na rok’ek’a dan Allah....”
Kasa furta komai Aunty B tai sai k’ura masa idanu da tayi idanunta na k’ok’arin kawo ruwa.... Cikin sauri ta k’unshe bakinta jin kuka na k’okarin b’alle mata ta fice daga wajen tana mai sakin kukanta, tabbas wannan d’an ‘yar uwartace da ya b’ace shekaru talatin... Allah ya dawo dashi, tabbas ba gizo yake mata ba shid’in ne Ma’aruf ne... Zataso ta zamto mutum ta farko da zata tabbatar da hakan ko don takai wannan labari mai dad’i ga ‘yar uwarta wacce ta rasa farin cikinta da walwalarta shekaru talatin baya....
A tare Hajiya da Aunty Lami suka zame jiki suka fice daga reception din cikin tsananin d’imauta da damuwa... Yanda suke sauk’a daga dakalin k’ofar reception d’in zai tabbatar maka cikin tsananin tashin hankali suke... Aunty Lami hannu biyu dafe da k’irji take fad’in “Haule Haule mun shiga uku abinda muka shuka shekaru talatin shike farautarmu, Haule ba gizo yake mana ba wllhi shine....!”
Cak ta tsaya da kalamanta sanda tai idanu hud’u da Aunty B itama sud’in take duba idanunta d’auke da hawaye......
SameenaAleeyou...📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*47*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Cikin tsananin fuci Aunty B ta tunk’arosu, tana mai gyara fuskarta, murmushin takaici saman fuskarta... Kai tsaye ta fuskanci Hajiyar Hafiz tana mai fad’in “Hankalinki ya kwanta burinki ya cika kin kashe Kausar, nasan da ace kin samu dama tin daga fari da kin kashe Zulfa’u ma amma saidai Allah k’addara mutuwar Zulfa’u hannunki ba.... Shin Haule wace irin ‘yar Adam ce ke...? Shin ashe har zaki iya halak’a jikarki jininki da hannayenki.... Ko zaki musnta min k’unar dasu Kausar sukai ba yinki bane iye....? Kiyi magana mana ya kikai shiru.....???” Ta k’arashe tamkar zata damk’o wuyar Hajiya....
Hajiya ta saki murmushi wanda yafi kama da yak’e kana tace “Bara’atu kenan, k’arfin halinki na mugun birgeni... Yo idan na kashe Kausar sai mai uwar mai zaki iya yi... Ke wacece mai kika isa kiyi.... Banza irinki karan kad’a miya....”
Aunty B da tuni ta gama isowa wuya ta nufo Hajiya gadan gadan zata shak’eta... Tuni Aunty Lami ta shiga tsakaninsu tana fad’in “Haba haba kukuwa... Ya kuke abu tamkar k’anan yara.... Shin da abinda kuke kuna taimaka ma Zulfa’u kenan...? Ya isa haka Bara’atu ki shige ciki Zulfa’u needs you....” Ta k’arashe tana janye Aunty B...
K’uramasu idanu su biyun Aunty B tai kana tace “A juri zuwa rafi wataran tulu zai fashe....”
Hajiya ta sakar mata murmushi a tak’aice kana tace “Zaifi kyau idan kika daina saka hancinki a abinda bai shafeki ba....”
Aunty B ta kuma murmusawa tana mai dubansu su biyun kana tace “Ko mai kuke b’oyewa ku biyun nan zai fito fili.... Mu zuba mu gani....” Daga haka sa kai tai ta shige....
Aunty Lami da Hajiya suka dubi juna ba tareda sun furta kalma guda ba....
Kasa sanar dasu Sameer yayi dole sai Awwab ne yazo ya masu bayani, Sameer na daga yanda yake yana jiyo sautin kukan ‘yan uwansa.... A hankali ya rintse idanunshi tausayinsu na d’awainiya dashi har saida wata nurse ta iskeshi ta sanar dashi an shirya second patient d’in kafin ya nufi theatre room d’in jiki a sanyaye...
Tin daga k’ofa yake jiyo sautin kukanta cikin tsananin sanyin muryarta tana ambaton ina Kausar take.....
Muryar sounds familiar to him, a hankali ya k’arashe shigowa cikin room d’in sauran nurses d’in na gaidashi.... Cak ya tsaya yana dubanta itace dai domin kaw k’unan wutan bai tab’a fuskarta ba, lokacin da ya soma kuskuransu itada k’aramar yarinya da motarsa ya soma tunowa, ya tuna kuskuransu na biyu da yayi lokacin data watsar da kifin da wancan azzalumar matar Baban nata ta aiketa... Ya tuna last ganinsa da ita a gidan Abbah a parlorn Abbah....
A b’angaren Raihana ma shid’in take duba domin kaw sam bata tab’a mance kamaninsa ba mutumin da ya tab’a defending d’inta so d’aya tak a rayuwarta daga muzgunawa da cin zarafi da Hajiya ke mata... Toh mai yakeyi a nan d’in...? Ta tambayi kanta.... Kafin ta nemo amsar tambayarta taji nurse guda na fad’in “Dr everything’s ready....”
A hankali ya jinjina mata kai still idanunsa naga Raihanah... A hankali ya soma takowa har ya k’araso gabanta....
Jikin Raihanah yai sanyi da irin duban da yake mata dukda zogi da tsananin rad’ad’i da fatarta ke mata.... Duban nurses d’in yai kana yace “Get me the injection...”
Jin an ambaci injection ya sata kuma dubanshi saidai gani tai ya sauya gaba d’aya tamkar bai santa ba haka yayi....
Hannu yasa yana k’ok’arin yaye farin k’yallen da aka rufa mata....
Ta kuma zabura tana dubansa saidai sam shid’in ba fuskarta yake duba ba da alama aikinsa yake k’ok’arin yi....
Tana jin sanda ya rik’o hannunta guda b’angaren da babu k’unan.... Daidai sanda idanunsu ya had’e waje guda, tsananin tsoro da firgici ne zalla cikin idanun Raihanah....
D’auke kai Sameer yai daga barin dubanta ya dawo da idnunsa ga yanda yake k’ok’arin zira allurar... Tana jin sanda yake zira mata allurar cikin tsanaki, hakan bai hanata rintse idanu ba dukda cewa zafin allurar baikai zafin k’unan da takeji a cikin jikinta ba...
Sosai doguwar rigar material d’in ta kame jikinta, dole sai an saka almak’ashi ya iya tsaga rigar a rabata da fatarta....
Ya kuma umarni ma nurses d’in su mik’a masa almak’ashi....
Tsoro da firgici ya cika Raihanah dukda duru duru data soma gani alamun allurar da ya mata ya soma kamata.... Sameer ya kurama fuskarta idanu sanda take fad’i cikin magagi...
“Mai mai zaka min... Mai zakuyimin...? Ina Kausar... Ku fad’a min yanda take.... Ku fad’a min tana lafiya....”
A hankali ya janye idanunsa daga duban fuskarta ya shiga k’ok’arin b’arka rigar jikinta.... Yanajin sanda ta rik’e hannunsa da sauri dukda cewa idanunta a lumshe suke tana fad’in “Nidai ka... ka k’yaleni.... Ni please don’t....!”
Duban bakinta yake yanda take maganar da k’yar... A hankali ya d’ago yana duban nurses d’in guda biyu mata...
Sai kallon kallo suke ganin yanayin likitan nasu yau yasha banban da ko yaushe....
“Dr are you alright...?” D’aya daga cikin nurses d’in ta tambaya... Itama d’in dubanta yai kana ya jinjina kai a hankali alamun yana lafiya kana ya mik’a mata almak’ashin ya masu umarni su farke rigar....
***
Tinda ya shigo gidan yake raba idanu ta ina zaiga d’iyarsa, sosai yarinyar ta shiga ransa har cikin ransa yakejin yarinyar cikin d’an lokaci k’ank’ani da suka kasance tare don tinda Hajiya ta kawota shike rainonta shike d’awainiyarta saidai idan zai fita ne sai ya bartama Sawwama nan ma bada son ransa ba sai don babu yanda ya iya.... Wani shak’uwa mai tsanani ne ya k’ullu tsakanin Hafiz da d’iyarsa Kausar, bai tsamman yana son yarinyar har haka ba kodashike Kausar yarinyace mai tsananin shiga rai ga duk wanda ya lak’anceta balle shi mahaifinta akwai bond mai k’arfi tsakani....
Saman kujera ya aje ledar kayan wasan da ya siyo mata musamman, ya d’aga labulen uwar d’aki ko zai gansu... Nan ma shiru babu Sawwama balle Kausar, toh ina suka shiga...? Ya tamabaya yana mai sauk’e labulen... Saman kujera ya zauna ya shiga fidda toys d’in murmushi kwance saman fuskarsa, danginsu doll baby da sauransu ya tabbata zataso kayan wasan shi kad’ai yake raya hakan cikin zuciyarsa....
Yana a haka ne yaji shigowar Sawwama tana tafe tana amsa waya, sanda ta gansa zaune a parlor turus tai tana dubansa lokaci guda ta canza maganar da take da Alhajinta tana mai fad’in “Karki damu Magajiya ai nace maki zanzo, zanzoni In sha Allah... Yauwa a huta gajiya sai munyi magana...” Ta k’arashe tana mai katse kiran...
Dubanta kurum yake domin kaw ba wai ya yarda da Magajiya ta gama waya ba, tun kwanakin baya jikinsa ke basa wani abu saidai baiso ya jefo zargi cikin zaman aurensu....
Cikin salo ta k’araso ta zauna hannun kujera tana mai fad’awa jikinsa had’ida masa salo take fad’in “Hafizy yaushe ka shigo....?” Birki tai ma kalaman nata ganin kayayyakin dake rik’e hannunsa.... Ta wani yatsina fuska kana tace “Wannan fah... Na zaci kaji ne a ledar ma....?”
Girgiza mata kai yai kana yace “Ba kaji bane.... Ina Kausar...?”
Nan ma yatsina ta kumayi had’ida gyara zama tana wani karkad’e wuyar riga had’ida taunar chewing gum kana tace “Aw baka had’u dasu a waje ba....?”
Duban mamaki ya mata kana yace “Su wane....?”
Tana mai rausaya had’ida jijjiga cikin taunar chewing gum d’inta irinta rik’akk’un ‘yan tasha kana tace “Su Sahariyya mana, ai sun biyo sawu sun d’auki Kausar, tana can ‘Yan turame....” Ta k’arashe kai ka rantse iyakacin gaskiyar ta fad’i....
A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya kana ya shiga tattaran kayan yana fad’in “Barin tafi ‘yan turamen na sameta....”
Maganganun Hajiya ya dawo da hankulansu, gaba d’aya kallon sani suke masa... Sahariyya kaw tuni jikinta ya d’au rawa har ta mance mai ya kawosu asibitin ta shiga bin Sameer da mayen kallo tana yank’are baki had’ida komad’a ita kad’ai... Tabbas ba gizo yake mata ba wannan na nuni da alamun cewa shid’in nata ne da sannu zai zama rabonta tinda gashi Allah ya kuma had’asu, ita kad’ai sai sakin murmushi take tamkar tab’ebb’iya...
Zulfa’u tai k’arfin halin maimaita tambayarta “Dr how’s my daughter.... How’s she doing.... Ina take dan Allah.. Shin zamu iya ganinsu...?”
D’an jim Sameer yayi ba tareda ya iya furta koda kalma ba sai kallo da yake bin Zulfa’u dashi yana hango wasu abubuwa nasu dake yanayi...
Cikin hawaye tana mai goge fuskarta take fad’in “Dr kamin magana dan Allah... Kace wani abu.... kace zamu iya shiga mu gansu na rok’ek’a dan Allah....”
Kasa furta komai Aunty B tai sai k’ura masa idanu da tayi idanunta na k’ok’arin kawo ruwa.... Cikin sauri ta k’unshe bakinta jin kuka na k’okarin b’alle mata ta fice daga wajen tana mai sakin kukanta, tabbas wannan d’an ‘yar uwartace da ya b’ace shekaru talatin... Allah ya dawo dashi, tabbas ba gizo yake mata ba shid’in ne Ma’aruf ne... Zataso ta zamto mutum ta farko da zata tabbatar da hakan ko don takai wannan labari mai dad’i ga ‘yar uwarta wacce ta rasa farin cikinta da walwalarta shekaru talatin baya....
A tare Hajiya da Aunty Lami suka zame jiki suka fice daga reception din cikin tsananin d’imauta da damuwa... Yanda suke sauk’a daga dakalin k’ofar reception d’in zai tabbatar maka cikin tsananin tashin hankali suke... Aunty Lami hannu biyu dafe da k’irji take fad’in “Haule Haule mun shiga uku abinda muka shuka shekaru talatin shike farautarmu, Haule ba gizo yake mana ba wllhi shine....!”
Cak ta tsaya da kalamanta sanda tai idanu hud’u da Aunty B itama sud’in take duba idanunta d’auke da hawaye......
SameenaAleeyou...📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*47*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Cikin tsananin fuci Aunty B ta tunk’arosu, tana mai gyara fuskarta, murmushin takaici saman fuskarta... Kai tsaye ta fuskanci Hajiyar Hafiz tana mai fad’in “Hankalinki ya kwanta burinki ya cika kin kashe Kausar, nasan da ace kin samu dama tin daga fari da kin kashe Zulfa’u ma amma saidai Allah k’addara mutuwar Zulfa’u hannunki ba.... Shin Haule wace irin ‘yar Adam ce ke...? Shin ashe har zaki iya halak’a jikarki jininki da hannayenki.... Ko zaki musnta min k’unar dasu Kausar sukai ba yinki bane iye....? Kiyi magana mana ya kikai shiru.....???” Ta k’arashe tamkar zata damk’o wuyar Hajiya....
Hajiya ta saki murmushi wanda yafi kama da yak’e kana tace “Bara’atu kenan, k’arfin halinki na mugun birgeni... Yo idan na kashe Kausar sai mai uwar mai zaki iya yi... Ke wacece mai kika isa kiyi.... Banza irinki karan kad’a miya....”
Aunty B da tuni ta gama isowa wuya ta nufo Hajiya gadan gadan zata shak’eta... Tuni Aunty Lami ta shiga tsakaninsu tana fad’in “Haba haba kukuwa... Ya kuke abu tamkar k’anan yara.... Shin da abinda kuke kuna taimaka ma Zulfa’u kenan...? Ya isa haka Bara’atu ki shige ciki Zulfa’u needs you....” Ta k’arashe tana janye Aunty B...
K’uramasu idanu su biyun Aunty B tai kana tace “A juri zuwa rafi wataran tulu zai fashe....”
Hajiya ta sakar mata murmushi a tak’aice kana tace “Zaifi kyau idan kika daina saka hancinki a abinda bai shafeki ba....”
Aunty B ta kuma murmusawa tana mai dubansu su biyun kana tace “Ko mai kuke b’oyewa ku biyun nan zai fito fili.... Mu zuba mu gani....” Daga haka sa kai tai ta shige....
Aunty Lami da Hajiya suka dubi juna ba tareda sun furta kalma guda ba....
Kasa sanar dasu Sameer yayi dole sai Awwab ne yazo ya masu bayani, Sameer na daga yanda yake yana jiyo sautin kukan ‘yan uwansa.... A hankali ya rintse idanunshi tausayinsu na d’awainiya dashi har saida wata nurse ta iskeshi ta sanar dashi an shirya second patient d’in kafin ya nufi theatre room d’in jiki a sanyaye...
Tin daga k’ofa yake jiyo sautin kukanta cikin tsananin sanyin muryarta tana ambaton ina Kausar take.....
Muryar sounds familiar to him, a hankali ya k’arashe shigowa cikin room d’in sauran nurses d’in na gaidashi.... Cak ya tsaya yana dubanta itace dai domin kaw k’unan wutan bai tab’a fuskarta ba, lokacin da ya soma kuskuransu itada k’aramar yarinya da motarsa ya soma tunowa, ya tuna kuskuransu na biyu da yayi lokacin data watsar da kifin da wancan azzalumar matar Baban nata ta aiketa... Ya tuna last ganinsa da ita a gidan Abbah a parlorn Abbah....
A b’angaren Raihana ma shid’in take duba domin kaw sam bata tab’a mance kamaninsa ba mutumin da ya tab’a defending d’inta so d’aya tak a rayuwarta daga muzgunawa da cin zarafi da Hajiya ke mata... Toh mai yakeyi a nan d’in...? Ta tambayi kanta.... Kafin ta nemo amsar tambayarta taji nurse guda na fad’in “Dr everything’s ready....”
A hankali ya jinjina mata kai still idanunsa naga Raihanah... A hankali ya soma takowa har ya k’araso gabanta....
Jikin Raihanah yai sanyi da irin duban da yake mata dukda zogi da tsananin rad’ad’i da fatarta ke mata.... Duban nurses d’in yai kana yace “Get me the injection...”
Jin an ambaci injection ya sata kuma dubanshi saidai gani tai ya sauya gaba d’aya tamkar bai santa ba haka yayi....
Hannu yasa yana k’ok’arin yaye farin k’yallen da aka rufa mata....
Ta kuma zabura tana dubansa saidai sam shid’in ba fuskarta yake duba ba da alama aikinsa yake k’ok’arin yi....
Tana jin sanda ya rik’o hannunta guda b’angaren da babu k’unan.... Daidai sanda idanunsu ya had’e waje guda, tsananin tsoro da firgici ne zalla cikin idanun Raihanah....
D’auke kai Sameer yai daga barin dubanta ya dawo da idnunsa ga yanda yake k’ok’arin zira allurar... Tana jin sanda yake zira mata allurar cikin tsanaki, hakan bai hanata rintse idanu ba dukda cewa zafin allurar baikai zafin k’unan da takeji a cikin jikinta ba...
Sosai doguwar rigar material d’in ta kame jikinta, dole sai an saka almak’ashi ya iya tsaga rigar a rabata da fatarta....
Ya kuma umarni ma nurses d’in su mik’a masa almak’ashi....
Tsoro da firgici ya cika Raihanah dukda duru duru data soma gani alamun allurar da ya mata ya soma kamata.... Sameer ya kurama fuskarta idanu sanda take fad’i cikin magagi...
“Mai mai zaka min... Mai zakuyimin...? Ina Kausar... Ku fad’a min yanda take.... Ku fad’a min tana lafiya....”
A hankali ya janye idanunsa daga duban fuskarta ya shiga k’ok’arin b’arka rigar jikinta.... Yanajin sanda ta rik’e hannunsa da sauri dukda cewa idanunta a lumshe suke tana fad’in “Nidai ka... ka k’yaleni.... Ni please don’t....!”
Duban bakinta yake yanda take maganar da k’yar... A hankali ya d’ago yana duban nurses d’in guda biyu mata...
Sai kallon kallo suke ganin yanayin likitan nasu yau yasha banban da ko yaushe....
“Dr are you alright...?” D’aya daga cikin nurses d’in ta tambaya... Itama d’in dubanta yai kana ya jinjina kai a hankali alamun yana lafiya kana ya mik’a mata almak’ashin ya masu umarni su farke rigar....
***
Tinda ya shigo gidan yake raba idanu ta ina zaiga d’iyarsa, sosai yarinyar ta shiga ransa har cikin ransa yakejin yarinyar cikin d’an lokaci k’ank’ani da suka kasance tare don tinda Hajiya ta kawota shike rainonta shike d’awainiyarta saidai idan zai fita ne sai ya bartama Sawwama nan ma bada son ransa ba sai don babu yanda ya iya.... Wani shak’uwa mai tsanani ne ya k’ullu tsakanin Hafiz da d’iyarsa Kausar, bai tsamman yana son yarinyar har haka ba kodashike Kausar yarinyace mai tsananin shiga rai ga duk wanda ya lak’anceta balle shi mahaifinta akwai bond mai k’arfi tsakani....
Saman kujera ya aje ledar kayan wasan da ya siyo mata musamman, ya d’aga labulen uwar d’aki ko zai gansu... Nan ma shiru babu Sawwama balle Kausar, toh ina suka shiga...? Ya tamabaya yana mai sauk’e labulen... Saman kujera ya zauna ya shiga fidda toys d’in murmushi kwance saman fuskarsa, danginsu doll baby da sauransu ya tabbata zataso kayan wasan shi kad’ai yake raya hakan cikin zuciyarsa....
Yana a haka ne yaji shigowar Sawwama tana tafe tana amsa waya, sanda ta gansa zaune a parlor turus tai tana dubansa lokaci guda ta canza maganar da take da Alhajinta tana mai fad’in “Karki damu Magajiya ai nace maki zanzo, zanzoni In sha Allah... Yauwa a huta gajiya sai munyi magana...” Ta k’arashe tana mai katse kiran...
Dubanta kurum yake domin kaw ba wai ya yarda da Magajiya ta gama waya ba, tun kwanakin baya jikinsa ke basa wani abu saidai baiso ya jefo zargi cikin zaman aurensu....
Cikin salo ta k’araso ta zauna hannun kujera tana mai fad’awa jikinsa had’ida masa salo take fad’in “Hafizy yaushe ka shigo....?” Birki tai ma kalaman nata ganin kayayyakin dake rik’e hannunsa.... Ta wani yatsina fuska kana tace “Wannan fah... Na zaci kaji ne a ledar ma....?”
Girgiza mata kai yai kana yace “Ba kaji bane.... Ina Kausar...?”
Nan ma yatsina ta kumayi had’ida gyara zama tana wani karkad’e wuyar riga had’ida taunar chewing gum kana tace “Aw baka had’u dasu a waje ba....?”
Duban mamaki ya mata kana yace “Su wane....?”
Tana mai rausaya had’ida jijjiga cikin taunar chewing gum d’inta irinta rik’akk’un ‘yan tasha kana tace “Su Sahariyya mana, ai sun biyo sawu sun d’auki Kausar, tana can ‘Yan turame....” Ta k’arashe kai ka rantse iyakacin gaskiyar ta fad’i....
A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya kana ya shiga tattaran kayan yana fad’in “Barin tafi ‘yan turamen na sameta....”