Sashe 120
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Dawowa tai ta kuma yin tsaye akan mijin nata kana tace “Toh yanzu da ka k’yalesa ya tafi sai inji meye shirin naka ai....” Ta k’arashe tana mai zama gefensa...
Murmusawa Daddy yai kana yace “Ko Ke fah Farida.. Shi miji idan anaso yayi abu ba’a nuna masa isa da gadara, indai ta wannan hanyar akeso yayi abu toh fah bazai yi ba, amma idan aka biyo ta hanyar kwantar da kai sai ya kwanta miki ma ki taka gadon bayansa ki shige abinki...”
Ammi tasha jinin jikinta tana duban sabon sauyin data samu daga mijin nata, tinda suke dashi yau sama da shekaru talatin bai tab’a yi mata magana mai kamada wannan ba, kullum dik abinda take so abinda tai niyya shi ake, da alama yanzun hannunka mai sanda yake mata...
“Ban fahimceka ba Daddyn Siyaam...” Ta fad’i tana mai karkatowa zuga dubansa sosai...
Murmushin Daddy ya kuma sakar mata kana yace “Soon zaki fahimceni Farida tah...Kuma na miki alk’awari nan bada jimawa ba Khalid d’inki zai aure.... Ki kwantar da hankalinki kinji koh....” Ya k’arashe yana mai kamo ‘yan yatsun hannunta had’ida murzasu kad’an...
Take annuri ya cika fuskar Ammi, tasan mijin nata bazai tab’a bata kunya ba tanada hundred percent guarantee akansa, dik abinda takeso shi yakeyi, bai tab’a keta dokarta ba a tsawon shekarun da sukai tare, mai ma zaisa taji wannan karon bazai abinda take so ba...? Lokaci guda ta kuma sakin murmushi tana duban Daddyn kana tace “Shisa nake matuk’ar k’aunarka mijina, kana min duk abinda nake so a koda yaushe...” Ta k’arashe tana mai kwantar da kai cikin k’irjinsa....
Lumshe idanunsa kurum Daddy yai, daga shi saiko Mahaliccinsa ne yakeda tabbacin suka san abinda yake ji cikin zuciyarsa...
***
A b’angaren Khalid kuwa abubuwan da suke faruwa a ‘yan kwanakin gaba d’aya sun d’aure masa kai, sun dagula masa lissafi... First canzawar Daddy, had’uwarsa dasu Aunty Daula, kusancin Daddy da Baffah yanzu kuma ga aikin gyaran gidansa na Gwarimpa da ya d’aurasa bisa... Dafe kansa yai a hankali yana furta “What are you up to Daddy...?” Ya fuzar da iska a hankali had’ida girgiza kansa kad’an lokaci guda yaci gaba da shirya kayansa...
Aunty Daula ya kira ya sanar da ita yana hanyarsa ta zuwa Abuja gobe da izinin Allah... Wai zo Kaga murna wajen Aunty Daula da yaranta... Tin a ranan suka soma shirye shiryen tarban Khalid...
***
KANO
Sawwama dake zaune gefen mahaifiyarta ta turo kallabi gaba sai taunar chewing gum take irin na matan da suka makara a bariki... D’aga k’afa tai ta d’aura d’aya bisa d’aya tana wani jijjiga take furta “Magajiya kenan... Ai na riga na samo lagon Hafiz... Zanyi dik abinda yake so daga k’arshe na k’yale shegiyar Zulfa’un ta auka ramina.... Haba ya kike kokonto na saika ba rainonki ba... Kinga nan...” Ta d’aga tafin hannunta tana nuna mata kana taci gaba da fad’in “Na kamasa a nan tinda ya bari nasan lagnosa...”
Dariya sukai itada mahaifiyarta kana Magajiya tace “Kinyi min dadai... Kici gaba karki fasa komai...” Suka kuma saka shewa suna tafe hannaye... Daidai nan Dillaliya tai sallama yara na biyeda ita d’auke da saitin akwatina nik’i nik’i....
“Gafara dai! Gafara dai !!! Inji masu gidan suna nan....?” Dilla iya tace sanda take kwab’e mayafinta tai d’amara dashi...
A tare Sawwama da Magajiya suka fito... Dilalliya na nunima yaran cewa su ije akwatinan a nan tsakar gidan....
Magajiya tabi akwatunan da kallo kana ta isa ta mik’awa Dillaliya tafukan hannayenta biyu suka tafe tana fad’in “Anyiririri Billahillazi na soma jiyo k’amshin amarci.... Kai ta wajena akwatunan nan sunci kud’insu...” Ta k’arashe tana jujjuya ‘yar k’aramar akwatin mai suffan jaka wacce ake zuba ‘yankunne da sark’a ciki.....
Dillaliliya na Washe baki take fad’in “Yo ai na fad’a miki bana kawo kayan banza... Nan da kike gani akwatinan wata yarinya ce sakin wawa, juyasu da kyau ki gani sabbi ne dal ko lamba ba’a cire masu ba....”
Magajiya tace “Wllhi na gani kaw....” Daidai nan wasu ‘yandaudu suka fito daga wani d’aki suka nufo akwatunan suna shewa da gud’a suna fad’in Uwarsu zata amarce, suna gud’a suna d’aga jakkunan....
“Kai ku ije akwatunan nan ban gama biyan kud’inba...” Cewar Magajiya tana fuzgewa hannun ‘yandaudun...
D’ayan ya wani kame zani yana gyara d’aurin k’irji da kallabi yake fad’in “Yo ai Babanmu ne zai biya... Wayyo wa yaga ni Laminde gidan Ubana na bariki....” Suka kuma kwashewa da dariya gaba d’aya kana Sawwama tace “Wai ku dakata, wai auren waye ake batu, Nifa ban gane ba...?”
‘Yandaudun suka had’e hannayensu waje guda suka tafe had’ida yin salo yanda dai sukeyi kana d’ayan ya kame baki yace “Au Tab! Wai Ke bakida labari... Toh uwa guda nawa mukeda a bariki.... Uwarmu dai itace zata amarce mu kuma mu tafi mata zaman d’aki...” Suka k’arashe suna kuma tafe hannaye.....
Sawwama ta dubi mahaifiyarta da mamaki.... D’aga mata gira tai kana tace “K’warai kuwa Sawwama aure zanyi na raya sunnar ma’aiki nima....”
Sawwama da mamaki ya cikata tace “Magajiya aure... Aure kuma da waye...?”
Magajiya na juya idanu take fad’in “Sati Uku ya rage na amarce Sawwama, ranar Bikin zaki San waye angon.... Kunga ku tattari akwatunan nan ku shigar min ciki...” Taceda ‘yan daudun.... Nan suka shiga kwasan kayan suna wani yauk’i su a dole ga mata.... D’ayan har cewa yake “Ni banma San a waye zan bada d’inkin nawa anko d’in ba....”
Sawwama dai kallo ta bisu dashi har suka shige yayinda Dillaliya da Magajiya suka ci gaba da tattauna cinikinsu don harta sauran su kayan d’aki yau take so su kammala cinikin komai tinda biki ya gabato....
***
Aunty B ta numfasa tana duban ‘yar uwar tata kana tace “Sati uku kacal ya rage a d’aura auren....”
Yaya Abida ta d’ago kod’add’un idanunta tana dubanta kana tace “Kije kisan yanda zakiyi ki hana wannan auren aukuwa Bara’atu.... Sanin kanki ne wannan auren daidai yake da maimaita bak’in tarihi.... Ki hana wannan auren aukuwa....!” Ta k’arashe cikin tsananin karaji tana mai baiwa Aunty Bara’atu baya....
Mik’ewa tsaye Aunty B tai kanta a k’asa kana tace “Yaya banida ikon hana aukuwar wannan auren.... Da ace inada iko hanawa wllhi da kafin nazo gareki da na hana... Ki yarda dani.....”
Juyowa tai sosai tana duban Aunty B kana ta tako gabanta kad’an.... “Bara’atu karki bari ayi wannan aure...!!!” Daga haka bata kuma cewa komai ba sai shigewa k’uryar d’aki da tai ta bar Aunty B nan tsaye cikin tsananin kad’uwar zuciya da mutuwar jiki.....
Wasu hawaye masu d’umin gaske suka gangaro mata.... Fuzar da iska tai kad’an kana ta isa jikin k’ofar d’akin ta dafa, kanta na kife bisa k’ofar take fad’in “Na barki lafiya Yaya... Ubangiji yaci gaba da kareki....!”” Daga haka sa kai tai ta fice daga cikin gidan tana matsan hawaye...
A can cikin d’aki kaw wani hoto dake sanye cikin k’aramar frame ta tsurama idanu, mutum uku ne jikin hoton, Wani dattijon mutumi sai wata matashiyar mace da k’aramin yaro da bazai haura shekaru uku ba... Ta shiga shafa saman hoton tana hango rayuwar da sukai a baya, rayuwa mai dad’i mai cikeda ni’imomi.... Ta rintse idanunta a hankali wasu hawayen suka kuma zubo mata... A hankali ta mik’e ta isa malank’ayin hoton ta kuma ratayesa... Lokaci guda take furta “Ma’aruf bazai biya diyan Ma’aruf ba...!” Tai maganar tana mai k’urama hoton idanu.....
***
Murmusawa Daddy yai kana yace “Ko Ke fah Farida.. Shi miji idan anaso yayi abu ba’a nuna masa isa da gadara, indai ta wannan hanyar akeso yayi abu toh fah bazai yi ba, amma idan aka biyo ta hanyar kwantar da kai sai ya kwanta miki ma ki taka gadon bayansa ki shige abinki...”
Ammi tasha jinin jikinta tana duban sabon sauyin data samu daga mijin nata, tinda suke dashi yau sama da shekaru talatin bai tab’a yi mata magana mai kamada wannan ba, kullum dik abinda take so abinda tai niyya shi ake, da alama yanzun hannunka mai sanda yake mata...
“Ban fahimceka ba Daddyn Siyaam...” Ta fad’i tana mai karkatowa zuga dubansa sosai...
Murmushin Daddy ya kuma sakar mata kana yace “Soon zaki fahimceni Farida tah...Kuma na miki alk’awari nan bada jimawa ba Khalid d’inki zai aure.... Ki kwantar da hankalinki kinji koh....” Ya k’arashe yana mai kamo ‘yan yatsun hannunta had’ida murzasu kad’an...
Take annuri ya cika fuskar Ammi, tasan mijin nata bazai tab’a bata kunya ba tanada hundred percent guarantee akansa, dik abinda takeso shi yakeyi, bai tab’a keta dokarta ba a tsawon shekarun da sukai tare, mai ma zaisa taji wannan karon bazai abinda take so ba...? Lokaci guda ta kuma sakin murmushi tana duban Daddyn kana tace “Shisa nake matuk’ar k’aunarka mijina, kana min duk abinda nake so a koda yaushe...” Ta k’arashe tana mai kwantar da kai cikin k’irjinsa....
Lumshe idanunsa kurum Daddy yai, daga shi saiko Mahaliccinsa ne yakeda tabbacin suka san abinda yake ji cikin zuciyarsa...
***
A b’angaren Khalid kuwa abubuwan da suke faruwa a ‘yan kwanakin gaba d’aya sun d’aure masa kai, sun dagula masa lissafi... First canzawar Daddy, had’uwarsa dasu Aunty Daula, kusancin Daddy da Baffah yanzu kuma ga aikin gyaran gidansa na Gwarimpa da ya d’aurasa bisa... Dafe kansa yai a hankali yana furta “What are you up to Daddy...?” Ya fuzar da iska a hankali had’ida girgiza kansa kad’an lokaci guda yaci gaba da shirya kayansa...
Aunty Daula ya kira ya sanar da ita yana hanyarsa ta zuwa Abuja gobe da izinin Allah... Wai zo Kaga murna wajen Aunty Daula da yaranta... Tin a ranan suka soma shirye shiryen tarban Khalid...
***
KANO
Sawwama dake zaune gefen mahaifiyarta ta turo kallabi gaba sai taunar chewing gum take irin na matan da suka makara a bariki... D’aga k’afa tai ta d’aura d’aya bisa d’aya tana wani jijjiga take furta “Magajiya kenan... Ai na riga na samo lagon Hafiz... Zanyi dik abinda yake so daga k’arshe na k’yale shegiyar Zulfa’un ta auka ramina.... Haba ya kike kokonto na saika ba rainonki ba... Kinga nan...” Ta d’aga tafin hannunta tana nuna mata kana taci gaba da fad’in “Na kamasa a nan tinda ya bari nasan lagnosa...”
Dariya sukai itada mahaifiyarta kana Magajiya tace “Kinyi min dadai... Kici gaba karki fasa komai...” Suka kuma saka shewa suna tafe hannaye... Daidai nan Dillaliya tai sallama yara na biyeda ita d’auke da saitin akwatina nik’i nik’i....
“Gafara dai! Gafara dai !!! Inji masu gidan suna nan....?” Dilla iya tace sanda take kwab’e mayafinta tai d’amara dashi...
A tare Sawwama da Magajiya suka fito... Dilalliya na nunima yaran cewa su ije akwatinan a nan tsakar gidan....
Magajiya tabi akwatunan da kallo kana ta isa ta mik’awa Dillaliya tafukan hannayenta biyu suka tafe tana fad’in “Anyiririri Billahillazi na soma jiyo k’amshin amarci.... Kai ta wajena akwatunan nan sunci kud’insu...” Ta k’arashe tana jujjuya ‘yar k’aramar akwatin mai suffan jaka wacce ake zuba ‘yankunne da sark’a ciki.....
Dillaliliya na Washe baki take fad’in “Yo ai na fad’a miki bana kawo kayan banza... Nan da kike gani akwatinan wata yarinya ce sakin wawa, juyasu da kyau ki gani sabbi ne dal ko lamba ba’a cire masu ba....”
Magajiya tace “Wllhi na gani kaw....” Daidai nan wasu ‘yandaudu suka fito daga wani d’aki suka nufo akwatunan suna shewa da gud’a suna fad’in Uwarsu zata amarce, suna gud’a suna d’aga jakkunan....
“Kai ku ije akwatunan nan ban gama biyan kud’inba...” Cewar Magajiya tana fuzgewa hannun ‘yandaudun...
D’ayan ya wani kame zani yana gyara d’aurin k’irji da kallabi yake fad’in “Yo ai Babanmu ne zai biya... Wayyo wa yaga ni Laminde gidan Ubana na bariki....” Suka kuma kwashewa da dariya gaba d’aya kana Sawwama tace “Wai ku dakata, wai auren waye ake batu, Nifa ban gane ba...?”
‘Yandaudun suka had’e hannayensu waje guda suka tafe had’ida yin salo yanda dai sukeyi kana d’ayan ya kame baki yace “Au Tab! Wai Ke bakida labari... Toh uwa guda nawa mukeda a bariki.... Uwarmu dai itace zata amarce mu kuma mu tafi mata zaman d’aki...” Suka k’arashe suna kuma tafe hannaye.....
Sawwama ta dubi mahaifiyarta da mamaki.... D’aga mata gira tai kana tace “K’warai kuwa Sawwama aure zanyi na raya sunnar ma’aiki nima....”
Sawwama da mamaki ya cikata tace “Magajiya aure... Aure kuma da waye...?”
Magajiya na juya idanu take fad’in “Sati Uku ya rage na amarce Sawwama, ranar Bikin zaki San waye angon.... Kunga ku tattari akwatunan nan ku shigar min ciki...” Taceda ‘yan daudun.... Nan suka shiga kwasan kayan suna wani yauk’i su a dole ga mata.... D’ayan har cewa yake “Ni banma San a waye zan bada d’inkin nawa anko d’in ba....”
Sawwama dai kallo ta bisu dashi har suka shige yayinda Dillaliya da Magajiya suka ci gaba da tattauna cinikinsu don harta sauran su kayan d’aki yau take so su kammala cinikin komai tinda biki ya gabato....
***
Aunty B ta numfasa tana duban ‘yar uwar tata kana tace “Sati uku kacal ya rage a d’aura auren....”
Yaya Abida ta d’ago kod’add’un idanunta tana dubanta kana tace “Kije kisan yanda zakiyi ki hana wannan auren aukuwa Bara’atu.... Sanin kanki ne wannan auren daidai yake da maimaita bak’in tarihi.... Ki hana wannan auren aukuwa....!” Ta k’arashe cikin tsananin karaji tana mai baiwa Aunty Bara’atu baya....
Mik’ewa tsaye Aunty B tai kanta a k’asa kana tace “Yaya banida ikon hana aukuwar wannan auren.... Da ace inada iko hanawa wllhi da kafin nazo gareki da na hana... Ki yarda dani.....”
Juyowa tai sosai tana duban Aunty B kana ta tako gabanta kad’an.... “Bara’atu karki bari ayi wannan aure...!!!” Daga haka bata kuma cewa komai ba sai shigewa k’uryar d’aki da tai ta bar Aunty B nan tsaye cikin tsananin kad’uwar zuciya da mutuwar jiki.....
Wasu hawaye masu d’umin gaske suka gangaro mata.... Fuzar da iska tai kad’an kana ta isa jikin k’ofar d’akin ta dafa, kanta na kife bisa k’ofar take fad’in “Na barki lafiya Yaya... Ubangiji yaci gaba da kareki....!”” Daga haka sa kai tai ta fice daga cikin gidan tana matsan hawaye...
A can cikin d’aki kaw wani hoto dake sanye cikin k’aramar frame ta tsurama idanu, mutum uku ne jikin hoton, Wani dattijon mutumi sai wata matashiyar mace da k’aramin yaro da bazai haura shekaru uku ba... Ta shiga shafa saman hoton tana hango rayuwar da sukai a baya, rayuwa mai dad’i mai cikeda ni’imomi.... Ta rintse idanunta a hankali wasu hawayen suka kuma zubo mata... A hankali ta mik’e ta isa malank’ayin hoton ta kuma ratayesa... Lokaci guda take furta “Ma’aruf bazai biya diyan Ma’aruf ba...!” Tai maganar tana mai k’urama hoton idanu.....
***