Sashe 5
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai Aunty tayi kafin ta k’arasa tana ambaton sunan Nabila cikin kakkausar murya...
Nabila ta d’ago a zabure tana subanta, lokaci guda ta tab’e fuska ba tareda tace da ita komai ba, Aunty taci gaba da fad’in “Ki wuce a wajen banson sakarci da rashin kunya, mai zaiki jin tattaunawar iyayenki, rashin hankali ko mai....?”
K’unk’uni Nabila keyi fuska a turb’une ta wuce Aunty tana mai ci gaba da k’unk’uninta cewa ita dai ba maras kunya bace.... Aunty ta bita da kallo yawa ta kikkifeta da mari sam tasu batazo d’aya da Nabila ba a cewarta yarinyar ita kad’ai ta fita zakka a gidan, sam Nabila batada ta ido, girman yarinyar akwai aiki inji Aunty....
Waje ta nema ta zauna a parlorn had’ida rapka uban tagumi tana jiran fitowar Abbah....
A b’angaren Nabila kuwa tana ficewa sashen Mamani ta nufa....
Sakina d’iyar Baffah Wali ta tarar parlorn tana kallo don babu a sashensu sai sunzo sashen Mamani suke kalla koda zata masu wulak’anci da masifa amma haka suke shanyewa sabida tsabagen son abin duniya...
Kallon arziki basuyima juna ba Nabila ta shige uwar d’akin....
Bata sameta a d’akin ba amma taji k’aran zuban ruwa daga bayi hakan ya tabbatar mata tana band’akin....
Bakin gado ta samu ta hakince harda d’ora k’afa d’aya bisa d’aya tana jiran fitowar Mamani daga bayi.....
***
“Sahariyya ki tashi ki dafawa yarinyar indomie tintine kin zaune sai aikin danna wayar banza kike....”
Hajiya da Khausar ke zaune bisa cnyarta ta fad’i
Tsuka Sahariyya tayi a hankali kana tace “Haba Hajiya nifah wllhi bacci ma nakeji wannan fitinanniyar yarinyar sam bata barmu munyi wani baccin kirki ba sai kuka take tana ambaton mamanta, ni wllhi Hajiya ki maidata gidan iyayenta don bazan masu bautar ‘yarsu ba nidai....” Tana k’arashe fad’in haka ta janyo earpiece d’inta ta manna a kunnenta....
Hajiya ta gyad’a kai had’ida furta yayi daidai, Najah dake faman mulka powder a fuskarta dukda cewa kayan makaranta ne jikinta kai kace biki zata yanda ta zauna tana zuba kwalliya a fuska, idanunta naga madubi take fad’in “Nidai kin gani shirin makaranta nake....” Ta k’arashe tana mai mik’ewa tsaye cikin matsattsun kayan makarantar nata....
Da mamaki Hajiya ke dubanta kana tace “Ke Najah ba Raiha tace an baku hutun kwana biyu ba, wani makarantar kuma zaki....”
Tsuka naja tayi had’ida turo baki kana tace “Wllhi Hajiya k’aryan Raiha da Marliya ne, hala dai ‘yan ajinsune aka basu mudai ba’a bamu ba...” Ta k’arashe tana zira jakkan makarantar ta.....
Hajiya ta maido da dubanta ga Sahariyya kana taci gaba da fad’in “Ke k’atuwar banza da ba makarantar kike zuwa ba ke ya kamata ki dafa mata, ace sau biyar kina zana jarabawar aji shida amma kin kasa ci gaba, dubi Zulfa’u dai da kad’an ta girmeki gashi har tana bautan k’asa, ga yarinyar can Nabilah tayi nisa ke kuwa haka nan baga karatun ba baga aurenba.....”
A hasale Sahariyya ta katseta da fad’in “Nidai karma ki had’ani da wad’ancan matsiyatan Hajiya ehe, kuma da kike maganarki ince Yaya Hafiz ma tunda aka koresa yayi satan amsa bai koma ba aidai gwarani farawa ne banyi ba, gaskiya ni Hajiya babu ruwanki da maganar makarantata balle aurena....” Tana ida fad’in haka ta buge skirt d’inta ta shige parlor tana maimaita wak’ar dake tashi cikin earpiece d’inta...
Najah ce ta dubi mahaifiyar tasu kana ta murmusa tace “Hajiya toh me amfanin Raiha tinda tace suna hutu ai sai ta dafa mata ta kula da ita kokuwa....”
“Raiha wanke wanke take kuma tana gamawa zata gyara kayan miyan abincin rana yau za’a kaiwa Alhaji can Kasuwa.....”
Najah ta jinjina kai tana mai darawa kana tace “Toh ai Hajiya sai ki mik’e ki shiga kitchen, ni na tafi sai na dawo....”
“Toh a dawo lafiya....” Hajiya ta fad’i sanda take mik’ewa tsaye, parlor ta nufa ta dangwalawa Sahariyya Khausar tana fad’in “Saiki rik’eta naje kitchen d’in.....”
Aiko ana ajiye Yarinyar ta fashe da kukan gaske sabida har ta gane Sahariyya irin tsawa da masifa data dinga mata a daren jiya don kawai tana kukan mahaifiyarta, yarinyar da duka bata wuce shekaru biyu da watanni bakwai zuwa takwas ba... Aiko Sahariyya ta bud’e murya ta daka mata tsawa wanda ya kuma birkitata harda d’auko wayar earpiece d’inta tana nuna mata zata zaneta....
Daga yanda Raihanah ke wanke wanke tana jiyo sautin kukan Khausar tausayin yarinyar ya cikata, cikin sauri ta tsame hannayenta ta nufi parlorn yanda Sahariyya da Khausar ke zaune...
Cikin sauri ta k’arasa ta d’auketa ganin yarinyar ta dungura tana kuka.....
Sahariyya ta daka mata tsawa, “Ke uban wa ya baki izinin d’aukarta....”
Cikin sanyin murya tace “Addah Sahariyya kuka fah take...”
“Toh anji kuka take saiki wuce ki ficemin da ita daga nan kafin na had’eku na daka.... Uwar kilibibi kawai....”
Cikin sauri Raihanah ta fice tana jijjiga yarinyar da tuni tayi lamo cikin jikinta, d’akinta ta nufa ta d’auko zanin goyo ta goyata a baya kana ta koma bakin aikinta, tanayi tana jijjiga Khausar har bacci yayi gaba da ita.....
***
Shaye da mamaki Mamani ta tsaya tana duban Nabilah dake zaune saman gadonta tana jijjiga k’afafu....
K’arasowa tayi cikin tafiyarta mai yanayi da d’ingishi sabida girma kana tace “Ke Halimatu lafiyarki kika shigo min har uwar d’aki ba tareda izinina ba kina faman kad’a k’afa... Hanshak’iya Mandiya...!” Ta k’arashe tana d’aura hannayenta bisa kunkuminta...
Mik’ewa Nabila tayi kana tace “Mamani ina kwana.....”
“Da ban kwanaba kya ganni maras kunya kawai....”
Nabilah ta kad’a kai kana tace “Allah ya gani na gaisheki na fita.... Dama zuwa nayi na fad’a maki na jaddada maki wllhi duk randa mahaifiyarmu ta gaji da zaman gidan nan tace zata tafi toh ki sani tare zamu tafi don wllhi Allah kinji na rantse Mamy tana sa k’afa da sunan barin gidan nan muma saidai a nememu a rasa, daga ke har Abban sai ku zauna a gidanku cikin kwanciyar hankali kiji da sauran jikokin naki amma dai kam ba ‘ya’yan Abbah ba don wllhi tafiya zamuyi....” Tana gama fad’in haka ta fice abinta ba tareda ta kuma bin takan Mamani dake daskare wajen ba...
Haba nan fah Mamani ta soma sbabi tana fad’in “Eh lallai yarinyar nan kin rik’a, laifin uban naku da ya k’yaleki kina boko yak’i aurar dake, dolema ki fand’are mana, ohni Halima bansan miyasa aka sakawa wannan maras kunyar yarinyar sunana ba, bakiyi halina ba wllhi, fitsararriya kawai mai halin uwarta...”
Daga parlor yanda Sakina ke zaune banda dariya bata komai bud’e murya tayi kana tace “Ai sunanki da aka saka mata yasata biyo halinki Mamani...”
“Kai waye a wajen nan maras kunya masu halin iyayensu mata...”
Kafin ta fito Sakina ta mik’e ta fice tana ci gaba da dariya, sauri sauri ta nufi sashensu kai rahoto wa mahaifiyarta Karima matan Baffah Wali....
***
*Kaduna*
A gajjiye ta shigo gidan jaka a hannu mayafi a hannu dogon takalminta a hannu, cikin kasaltacciyar murya take kwad’a masa kira don taga motarsa a parking lot hakan ya tabbatar mata yana gida...
“Partner..! Partner...!! I’m home, where are you....”
“Yes honey I’m here...” Ya amsata daga yanda yake...
B’angaren da tajiyo muryar nasa ta nufa bayan ta zuba tarkacan hannunta a parlor....
Tsaye ta gansa bakin gass cooker yana juya sausage cikin pan ga bread da fresh lettuce a gefe alamun sandwich zai had’a....
Rungumesa ta baya tayi tana fad’in “Umm it smell delicious Partner, ayi sauri a bani naci I’m starving already...” Ta k’arashe tana d’ora hab’arta bisa kafad’arsa....
Murmushi yake yana ci gaba da zuba sausage d’in cikin plate kana yace “Partner kinsan wannan aikinki ne kawai karambani nake maki, don haka zo ki k’arasa ki samu ladanki...”
Turo baki tayi had’ida dad’a matseshi kana tace “But you know I’m not a good cook Partner...”
Juyowa yayi yana dubanta kafin ya d’anja hancinta yace “My wife can’t cook but she can run a company.... Am I right...?”
Jinjina masa kai tayi kana tace “Exactly Partner.... Muje muci before it get cold....”
Bata jira cewansa ba ta soma d’aukan abincin zuwa dining table...
Misalin k’arfe goma da rabi sun gama duk wasu d’abi’unsu da suke kafin suyi bacci tuni ta haye saman gado ba tareda jiran Partner d’in nata ba, dubanta kurum yayi had’ida murmusawa kafin ya jawo computer d’insa ya shiga mail d’insa yana duba abinda yake tsammani... Aiko nan yaga sak’on ya shigo... A hankali ya rintse idanu had’ida sauk’e ajiyan zuciya... Rufe computer d’in yayi kafin ya k’arasa saman gadon yanda Siyama ke kwance tana duba sak’wannin da suka shigo mata a wastapp sai faman hamma take alamun bacci da gajjiya...
Ta bayanta yasa hannayensa ya rungumota kafin ya zame wayar nata a hankali yana fad’in “Partner this is my time a ajiye wannan saida safe kuma....”
Cikin kasaltacciyar murya take fad’in “Partner what are you doing, I’m exhausted please...”
Matseta yayi kana yace “Okay maybe some little massage may help... wouldn’t they....? Or may be some kisses may help too....”
Kukan shagwab’a ta soma masa tana turesa jin abinda yake mata tana fad’in “Partner no.... let go please, not now.. I know exactly what you’re up to....” Rufe bakinta yayi da sumba kafin ya kashe masu side lamp...
*SameenaAleeyou📚*
[25/11, 16:43] +234 703 745 3539: *INDA RAI*
_.................DA RABO_
*05*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Tafe suke cikin farfajiyan asibitin ko wannensu cikin shiga irinta k’wararrun likitoci, hannayensu rik’eda wasu ‘yan kofi da sukafi kamada disposable saman wasu ‘yan k’anan plates, shakka babu coffee ne ciki kasancewar safiya ce lokacin....
Wajene mai kunshe da mutane wanda yafi kamada a kirasa Cafeteria, can wani table suka nufa suka zauna yayinda wasu nurses ke mik’a masu gaisuwa, Sultan ne kawai mai iya amsawa shi kuwa Sameer saidai ya jinjina kai alamun amsawa...
Hannu Sultan ya nad’e yana duban abokin nasa wanda gaba d’aya yau d’in bai gane masa ba, a hankali ya d’au coffee d’insa yana kurb’a ba tareda ya d’aga idanunsa daga duban Sameer d’in ba, ko ba’a fad’a maka ba yana cikin damuwa da tashin hankali...
Sultan ya d’anyi gyaran murya kana yace “Are you sure you’re alright Sameer, it’s obvious you’re not yourself.... Wai meke faruwa ne.....?”
Nabila ta d’ago a zabure tana subanta, lokaci guda ta tab’e fuska ba tareda tace da ita komai ba, Aunty taci gaba da fad’in “Ki wuce a wajen banson sakarci da rashin kunya, mai zaiki jin tattaunawar iyayenki, rashin hankali ko mai....?”
K’unk’uni Nabila keyi fuska a turb’une ta wuce Aunty tana mai ci gaba da k’unk’uninta cewa ita dai ba maras kunya bace.... Aunty ta bita da kallo yawa ta kikkifeta da mari sam tasu batazo d’aya da Nabila ba a cewarta yarinyar ita kad’ai ta fita zakka a gidan, sam Nabila batada ta ido, girman yarinyar akwai aiki inji Aunty....
Waje ta nema ta zauna a parlorn had’ida rapka uban tagumi tana jiran fitowar Abbah....
A b’angaren Nabila kuwa tana ficewa sashen Mamani ta nufa....
Sakina d’iyar Baffah Wali ta tarar parlorn tana kallo don babu a sashensu sai sunzo sashen Mamani suke kalla koda zata masu wulak’anci da masifa amma haka suke shanyewa sabida tsabagen son abin duniya...
Kallon arziki basuyima juna ba Nabila ta shige uwar d’akin....
Bata sameta a d’akin ba amma taji k’aran zuban ruwa daga bayi hakan ya tabbatar mata tana band’akin....
Bakin gado ta samu ta hakince harda d’ora k’afa d’aya bisa d’aya tana jiran fitowar Mamani daga bayi.....
***
“Sahariyya ki tashi ki dafawa yarinyar indomie tintine kin zaune sai aikin danna wayar banza kike....”
Hajiya da Khausar ke zaune bisa cnyarta ta fad’i
Tsuka Sahariyya tayi a hankali kana tace “Haba Hajiya nifah wllhi bacci ma nakeji wannan fitinanniyar yarinyar sam bata barmu munyi wani baccin kirki ba sai kuka take tana ambaton mamanta, ni wllhi Hajiya ki maidata gidan iyayenta don bazan masu bautar ‘yarsu ba nidai....” Tana k’arashe fad’in haka ta janyo earpiece d’inta ta manna a kunnenta....
Hajiya ta gyad’a kai had’ida furta yayi daidai, Najah dake faman mulka powder a fuskarta dukda cewa kayan makaranta ne jikinta kai kace biki zata yanda ta zauna tana zuba kwalliya a fuska, idanunta naga madubi take fad’in “Nidai kin gani shirin makaranta nake....” Ta k’arashe tana mai mik’ewa tsaye cikin matsattsun kayan makarantar nata....
Da mamaki Hajiya ke dubanta kana tace “Ke Najah ba Raiha tace an baku hutun kwana biyu ba, wani makarantar kuma zaki....”
Tsuka naja tayi had’ida turo baki kana tace “Wllhi Hajiya k’aryan Raiha da Marliya ne, hala dai ‘yan ajinsune aka basu mudai ba’a bamu ba...” Ta k’arashe tana zira jakkan makarantar ta.....
Hajiya ta maido da dubanta ga Sahariyya kana taci gaba da fad’in “Ke k’atuwar banza da ba makarantar kike zuwa ba ke ya kamata ki dafa mata, ace sau biyar kina zana jarabawar aji shida amma kin kasa ci gaba, dubi Zulfa’u dai da kad’an ta girmeki gashi har tana bautan k’asa, ga yarinyar can Nabilah tayi nisa ke kuwa haka nan baga karatun ba baga aurenba.....”
A hasale Sahariyya ta katseta da fad’in “Nidai karma ki had’ani da wad’ancan matsiyatan Hajiya ehe, kuma da kike maganarki ince Yaya Hafiz ma tunda aka koresa yayi satan amsa bai koma ba aidai gwarani farawa ne banyi ba, gaskiya ni Hajiya babu ruwanki da maganar makarantata balle aurena....” Tana ida fad’in haka ta buge skirt d’inta ta shige parlor tana maimaita wak’ar dake tashi cikin earpiece d’inta...
Najah ce ta dubi mahaifiyar tasu kana ta murmusa tace “Hajiya toh me amfanin Raiha tinda tace suna hutu ai sai ta dafa mata ta kula da ita kokuwa....”
“Raiha wanke wanke take kuma tana gamawa zata gyara kayan miyan abincin rana yau za’a kaiwa Alhaji can Kasuwa.....”
Najah ta jinjina kai tana mai darawa kana tace “Toh ai Hajiya sai ki mik’e ki shiga kitchen, ni na tafi sai na dawo....”
“Toh a dawo lafiya....” Hajiya ta fad’i sanda take mik’ewa tsaye, parlor ta nufa ta dangwalawa Sahariyya Khausar tana fad’in “Saiki rik’eta naje kitchen d’in.....”
Aiko ana ajiye Yarinyar ta fashe da kukan gaske sabida har ta gane Sahariyya irin tsawa da masifa data dinga mata a daren jiya don kawai tana kukan mahaifiyarta, yarinyar da duka bata wuce shekaru biyu da watanni bakwai zuwa takwas ba... Aiko Sahariyya ta bud’e murya ta daka mata tsawa wanda ya kuma birkitata harda d’auko wayar earpiece d’inta tana nuna mata zata zaneta....
Daga yanda Raihanah ke wanke wanke tana jiyo sautin kukan Khausar tausayin yarinyar ya cikata, cikin sauri ta tsame hannayenta ta nufi parlorn yanda Sahariyya da Khausar ke zaune...
Cikin sauri ta k’arasa ta d’auketa ganin yarinyar ta dungura tana kuka.....
Sahariyya ta daka mata tsawa, “Ke uban wa ya baki izinin d’aukarta....”
Cikin sanyin murya tace “Addah Sahariyya kuka fah take...”
“Toh anji kuka take saiki wuce ki ficemin da ita daga nan kafin na had’eku na daka.... Uwar kilibibi kawai....”
Cikin sauri Raihanah ta fice tana jijjiga yarinyar da tuni tayi lamo cikin jikinta, d’akinta ta nufa ta d’auko zanin goyo ta goyata a baya kana ta koma bakin aikinta, tanayi tana jijjiga Khausar har bacci yayi gaba da ita.....
***
Shaye da mamaki Mamani ta tsaya tana duban Nabilah dake zaune saman gadonta tana jijjiga k’afafu....
K’arasowa tayi cikin tafiyarta mai yanayi da d’ingishi sabida girma kana tace “Ke Halimatu lafiyarki kika shigo min har uwar d’aki ba tareda izinina ba kina faman kad’a k’afa... Hanshak’iya Mandiya...!” Ta k’arashe tana d’aura hannayenta bisa kunkuminta...
Mik’ewa Nabila tayi kana tace “Mamani ina kwana.....”
“Da ban kwanaba kya ganni maras kunya kawai....”
Nabilah ta kad’a kai kana tace “Allah ya gani na gaisheki na fita.... Dama zuwa nayi na fad’a maki na jaddada maki wllhi duk randa mahaifiyarmu ta gaji da zaman gidan nan tace zata tafi toh ki sani tare zamu tafi don wllhi Allah kinji na rantse Mamy tana sa k’afa da sunan barin gidan nan muma saidai a nememu a rasa, daga ke har Abban sai ku zauna a gidanku cikin kwanciyar hankali kiji da sauran jikokin naki amma dai kam ba ‘ya’yan Abbah ba don wllhi tafiya zamuyi....” Tana gama fad’in haka ta fice abinta ba tareda ta kuma bin takan Mamani dake daskare wajen ba...
Haba nan fah Mamani ta soma sbabi tana fad’in “Eh lallai yarinyar nan kin rik’a, laifin uban naku da ya k’yaleki kina boko yak’i aurar dake, dolema ki fand’are mana, ohni Halima bansan miyasa aka sakawa wannan maras kunyar yarinyar sunana ba, bakiyi halina ba wllhi, fitsararriya kawai mai halin uwarta...”
Daga parlor yanda Sakina ke zaune banda dariya bata komai bud’e murya tayi kana tace “Ai sunanki da aka saka mata yasata biyo halinki Mamani...”
“Kai waye a wajen nan maras kunya masu halin iyayensu mata...”
Kafin ta fito Sakina ta mik’e ta fice tana ci gaba da dariya, sauri sauri ta nufi sashensu kai rahoto wa mahaifiyarta Karima matan Baffah Wali....
***
*Kaduna*
A gajjiye ta shigo gidan jaka a hannu mayafi a hannu dogon takalminta a hannu, cikin kasaltacciyar murya take kwad’a masa kira don taga motarsa a parking lot hakan ya tabbatar mata yana gida...
“Partner..! Partner...!! I’m home, where are you....”
“Yes honey I’m here...” Ya amsata daga yanda yake...
B’angaren da tajiyo muryar nasa ta nufa bayan ta zuba tarkacan hannunta a parlor....
Tsaye ta gansa bakin gass cooker yana juya sausage cikin pan ga bread da fresh lettuce a gefe alamun sandwich zai had’a....
Rungumesa ta baya tayi tana fad’in “Umm it smell delicious Partner, ayi sauri a bani naci I’m starving already...” Ta k’arashe tana d’ora hab’arta bisa kafad’arsa....
Murmushi yake yana ci gaba da zuba sausage d’in cikin plate kana yace “Partner kinsan wannan aikinki ne kawai karambani nake maki, don haka zo ki k’arasa ki samu ladanki...”
Turo baki tayi had’ida dad’a matseshi kana tace “But you know I’m not a good cook Partner...”
Juyowa yayi yana dubanta kafin ya d’anja hancinta yace “My wife can’t cook but she can run a company.... Am I right...?”
Jinjina masa kai tayi kana tace “Exactly Partner.... Muje muci before it get cold....”
Bata jira cewansa ba ta soma d’aukan abincin zuwa dining table...
Misalin k’arfe goma da rabi sun gama duk wasu d’abi’unsu da suke kafin suyi bacci tuni ta haye saman gado ba tareda jiran Partner d’in nata ba, dubanta kurum yayi had’ida murmusawa kafin ya jawo computer d’insa ya shiga mail d’insa yana duba abinda yake tsammani... Aiko nan yaga sak’on ya shigo... A hankali ya rintse idanu had’ida sauk’e ajiyan zuciya... Rufe computer d’in yayi kafin ya k’arasa saman gadon yanda Siyama ke kwance tana duba sak’wannin da suka shigo mata a wastapp sai faman hamma take alamun bacci da gajjiya...
Ta bayanta yasa hannayensa ya rungumota kafin ya zame wayar nata a hankali yana fad’in “Partner this is my time a ajiye wannan saida safe kuma....”
Cikin kasaltacciyar murya take fad’in “Partner what are you doing, I’m exhausted please...”
Matseta yayi kana yace “Okay maybe some little massage may help... wouldn’t they....? Or may be some kisses may help too....”
Kukan shagwab’a ta soma masa tana turesa jin abinda yake mata tana fad’in “Partner no.... let go please, not now.. I know exactly what you’re up to....” Rufe bakinta yayi da sumba kafin ya kashe masu side lamp...
*SameenaAleeyou📚*
[25/11, 16:43] +234 703 745 3539: *INDA RAI*
_.................DA RABO_
*05*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Tafe suke cikin farfajiyan asibitin ko wannensu cikin shiga irinta k’wararrun likitoci, hannayensu rik’eda wasu ‘yan kofi da sukafi kamada disposable saman wasu ‘yan k’anan plates, shakka babu coffee ne ciki kasancewar safiya ce lokacin....
Wajene mai kunshe da mutane wanda yafi kamada a kirasa Cafeteria, can wani table suka nufa suka zauna yayinda wasu nurses ke mik’a masu gaisuwa, Sultan ne kawai mai iya amsawa shi kuwa Sameer saidai ya jinjina kai alamun amsawa...
Hannu Sultan ya nad’e yana duban abokin nasa wanda gaba d’aya yau d’in bai gane masa ba, a hankali ya d’au coffee d’insa yana kurb’a ba tareda ya d’aga idanunsa daga duban Sameer d’in ba, ko ba’a fad’a maka ba yana cikin damuwa da tashin hankali...
Sultan ya d’anyi gyaran murya kana yace “Are you sure you’re alright Sameer, it’s obvious you’re not yourself.... Wai meke faruwa ne.....?”