← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 198

Sashe 38

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mama na parlor tana kallon tashan Discovery family taji bak’uwar sallama daga bakin k’ofa, ta rage muryar tv d’in a hankali kana ta amsa sallamar had’ida bada izinin shigowa.....
Tabi matashiyar matar da kallo domin kaw bata shaidata ba, da fari’arta tai mata iso...
Siyama ta k’araso ciki murmushi kwance saman fuskarta....
Daga can bakin carpet tai yunk’urin zama Mama tai saurin cewa “A’a dan Allah tashi ki zauna sama, sannu da zuwa...”
Siyama tai godiya murmushi saman fuskarta kana ta zauna saman kujeran...
Gaisar da Mama tayi cikeda d’a’a, Mama ta amsa mata da sakin fuska ta k’arada “Saidai ban gane daga inane ba...”
Nanma murmushi Siyama tai had’ida gyara zaman mayafinta tace “Sunana Siyama, ni ce matar Sameer...”
Nan fara’an Mama ya k’aru aka shiga sabon gaisuwa, Mama ta shiga haba haba da ita, da kanta ta tashi ta shiga kawo mata abin tab’awa musamman da taji sauk’anta garin kenan....
Siyama sai jinjina karamcin matar take, Mama ta zauna daga can gefe suna ci gaba da fira yanda a firan ta fahimci Sameer d’in baisan da zuwar Siyamar ba, a nan ne Mama ta d’an sha jinin jikinta...
Siyama ta kuma tambayanta Sameer d’in...
Mama ta d’an muskuta tace “Eh toh gaskiya inaga tinda ya fita sallar la’asar bai dawo ba, amma bazai wuce yana masallacin ba, anjima kad’an zai dawo...”

Siyama ta d’an kauda kai gefe ta yatsina fuska kafin ta juyo tana sakin murmushi, Mama tai mata iso zuwa d’aki don ta huce gajjiya da kyau, itadai Siyama sai yatsine yatsine take tana duban gidan tana ayyanawa a ranta babu laifi dukda dai bai kai nasu kyau da had’uwa ba k’ila zata d’an iya jurewa ta zauna har ta samu ta shawo kan Partner su shirya....

***

A b’angaren su Nabilah kuwa tunda suka shiga aji Yusrah ta k’agu a bud’e jakan suga menene a ciki, Nabilah ta danna mata harara kana tace “Keda kika amso sai kisan yanda zakiyi da jakkar don nikam bazan d’auka ba.. Gwarama kisan yanda zaki samo shi ki bashi abunshi...”Ta k’arashe tana k’ok’arin tattare books d’inta..
Yusrah ta d’an harereta tace “Wllhi sai na bud’e...”
Ta k’arashe tana bud’e jakkar...
Da tsananin mamaki ta tsaya tana duban abindake ciki, tai saurin tab’a Nabilah tana fad’in “Ke kalli abinda ke ciki...”
Nabilah tai pause tana duban Teddy Bear fara k’al mai kyau harda ‘yar crown akanta, dariya ya kusa kufce mata, lallai wannan yama gama rainata, itace zai kawowa abin wasa... Tai k’wafa kana ta finciki Teddy bear d’in hannu Yusrah kafin ta sami zarafin magana taci murya na tashi cikin teddy d’in _I’m sorry_... Suka dubi juna itada Yusrah cikeda mamaki suna kuma duban Teddy d’in...
Nabilah ta sake motsa Teddy d’in domin tabbatar da abinda kunnuwanta suka jiyo mata nan kuma sukaji Teddy d’in ya sake fad’in _I love You_ Ai a d’ari ta saki Teddy d’in ya fad’i k’asa ta saki k’ara cikin firgita...
‘Yan aji suka juyo suna dubansu, Yusrah tai saurin d’auko Teddy d’in tana dariya had’ida furta “Lallai nashi salon daban ne wayyo Allah na... Wato dai bazai bud’i baki ya sanar dake ba saidai ya turo d’an aike da sak’o...Gaskiya k’awata na miki murna...” Ta k’arashe tana rungume teddy d’in cikeda nuna farin ciki...
Nabilah da gaba d’aya jikinta ya mutu kasa furta komai tayi sai k’urama teddy d’in idanu da tai, can k’asar zuciyarta wani irin annashuwa takeji wanda batasan dalili ba, gaba d’aya sai ta koma wata sukuku da ita haka nan...
Koda sukazo tafiya gida Yusrah ta damk’a mata jakan teddy d’inta tana fad’in “Matar Bear ki adanashi da kyau kuma don Allah ki amince ki zama baby bear d’inshi don wllhi kun bala’in dacewa...”

Harara Nabilah ta galla mata kana tace “Allah ya sawak’e min, ina zuwa gida zan kirashi yazo ya amshi abunshi ko na jefar...”

Yusrah ta dara tana fad’in “Ahab na yaushe k’wayar idanunki sun nuna kin kamu da son bear babe....” Nabilah ta kai mata duka Yusrah ta zille ta shige adaidaita tana dariya tana fad’in idan bear ya kira a gaisheshi...

Nabilah ta rakata da harara tana fad’in zasu had’u gobe ne...
Tinda ta shiga adaidaita itama kalaman take kan nanatawa cikin zuciyarta _I’m Sorry.... I Love you_ A hankali ta saki murmushin da batasan daga ina ya taso mata ba, har ta isa gida tinani take cikin adaidaitan....

***

Ya jima sosai a masallacin yana lazimi da kai kukansa ga mahaliccinsa situation d’in da yake ciki Allah ya kawo masa mafita...
Ya mik’e ya maida Alkur’an ma’ajiyanshi... D’ago idanun da zai ya hangi Abbah daga can gefe wanda shima nashi kukan ya kawo wajen mahallicin shi, Abbah yana d’ago idanu sukai ido hud’u da Sameer wanda ya hangi rama da ya d’anyi... Su duka biyun suka k’urama juna idanu tamkar masu tunanin wani abun....

Sameer yai k’ok’arin k’ak’aro murmushi ya sakarwa Abbah kana ya nufo yanda yake a zaune....
Saidai yana k’arasowane ya hangi damshin hawaye a idanun Dattijo Abbah.. Jikin Sameer ya kuma yin sanyi sakamakon hango hawaye da yayi cikin idanun Dattijon....
A hankali ya duk’a yayi zama irinta rak’umi a gaban Abbah...

SameenaAleeyou📚
[08/02, 13:34] +234 703 745 3539: *INDA RAI*
_...............DA RABO_

*33*

*©Sameena Aleeyou...✍🏽*

Shamsu bai ida rufe baki ba Siyama ta shigo kanta a k’asa tana satan kallon Sameer wanda ya koma tamkar bai tab’a murmushi ba tsawon rayuwarsa...
Shamsu ya mik’e ya basu waje ya fice gaba d’aya ko d’an zolayar data zamar masa d’abi’a bai tsaya yinta ba don ya fahimci abokin nasa da matarsa suna buk’atar ganawa mai mahimmanci...

Daga can kujerar gefenshi ta zauna tana mai kuma shan jinin jikinta, a hankali ta furta “Partner...!”

Wani duban da yai mata ya sanyata had’iye maganar nata...
“What brings you here...? Wait da izininwa ma kika taho har garin nan...? Kodayake bai kamata na tsaya tambayarki batun neman izini ba tinda kinyi abinda yafi wannan.... Ki tashi ki koma yanda kika fito bana buk’atarki a nan...”

Tai saurin d’agowa tana dubansa k’irjinta na bugawa da sauri, anya wannan Sameer d’inta ne kokuwa dai canza shi akai....
Ya kuma darara mata tsawa “Nace ki tashi ki koma yanda kika fito...!”

Tai saurin zabura k’walla na k’ok’arin ciko idanunta, cikin muryar kuka take furta “Partner wllhi babu yanda zan koma sai ka saurareni, haba Sameer does it has to be like this... Can’t you see I’m suffering.... Sameer just pills ka gani fah... Kuma at least sai ka bani dama nai bayani, meyasa kake punishing soyayyarmu haka... Sameer we both know that we love each other so much, Please mana Partner...”

Da tsananin mamaki da takaici ya d’ago yana dubanta kana ya girgiza kai yace “Did you just say love...? Siyama kinsan abinda ake kira so kuwa....?” Yayi maganar yana mata wani irin duba da rinannun idanunsa...

A hankali ta sauk’ar da nata idanun k’asa...
Sameer ya girgiza kai a hankali kana yaci gaba da fad’in “Da ace kinsan matsayin abinda kike fad’i da baki aikata abinda kika aikata ba.... Mutumin da yake sonka bazai tab’a k’yamatar abinda zai fito daga jikinka ba.... Shiyasa nakeson jin dalilin amincewa aurena da kikayi idan har bakison had’a zuri’a dani....”

Tai saurin d’ago idanunta mai zuban hawaye tana dubansa, lokaci guda ta shiga girgiza kai tana furta “Ba haka bane Partner...”

“Toh yaya ne..!!?” Ya tambaya cikin d’aga murya da ware idanu wanda daga gani zuciyarsa zafi take masa...

Cikin muryar kuka taci gaba da fad’in “Partner I don’t want to share your love with anyone else, I want you to love me, just me and only me... Even your parents don babu yanda na iya ne shiyasa nake tsoron idan ka haifi yara zaka daina sona...” Ta k’arashe tana goge hawayen da suka wanke mata fuska....

A yayinda Sameer ya mata k’uri yana dubanta.... Siyama ta gangaro daga kujeran da take zaune hawaye naci gaba da kwaranya mata ta durk’usa gabanshi, cikin muryar kuka taci gaba da fad’in “Partner I’m sorry... I really I am... I I I’m only human, and I thought I was doing what’s best for the both of us.... please forgive me.... I didn’t mean to hurt you...”

Tuni zuciyarsa ta karaya, sam bai k’aunar yaga mutum na kuka balle ace mace macenma matarshi ta sunnah... A hankali yasa hannuwansa duka biyu ya tallafo Siyama dukda cewa abinda ta masa abu ne mai wuyan yafewa....
Tuni ta shige cikin jikinsa tana sakin wani sabon kuka...
Murya can k’asa yake furta “Is ok... Ya isa haka ki daina kuka, abinda ban gane ba shine meyasa zaki aikata such a horrible thing like that... Bakiso ki haihu dani ne... Kina gudun abin kunya ne sabida kar ace uban ‘ya’yanki baida asali... Wannan shine dalilinki...?”

D’agowa tai tana dubansa da watery eyes d’inta, lokaci guda ta shiga girgiza kai tana mai furta “What... Asali....? I don’t get you....”

Gyara mata zama yayi kana yace “Don’t play a dumb here Siyama, wannan shine dalilinki ba wancan silly excuse d’in da kika bani ba.... C’mon sweetheart, idan har da gaske kina sona don’t lie to me anymore... Please... So tell is there anything you’re not telling me....” Ya k’arashe yana rik’e da ‘yan yatsunta...

Saida ta had’iyi wani miyau sanda ta tuna kalaman Ammi cewa taci da shan maganin hana d’aukan ciki kana ta girgiza kai tace “I don’t anything please believe me Partner... Wai meke faruwa ne...?”

K’uri ya mata da rinannun idanunsa domin kuwa har k’asan zuciyarsa yakeji akwai abubuwa da Siyama ke b’oye masa tin bayan abinda ya faru tsakaninsu...Cikin wane irin yanayi ya furta “It turns out mutanen da tun tasowata na sansu a matsayin mahaifa na basune suka haifeni ba...”

A firgice Siyama ta mik’e zaune daga jikinshi tana dubanshi...
Girgiza kai ta shigayi tana furta “But... how... How comes...?”

Jinjina mata kai ya kumayi kana yace “Yes, Momy and Dad aren’t my real parents....”

Cikeda shock Siyama tace “If they aren’t your parents, then where are your real parents...?”
Chapter 38 · 0% Book details