← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 198

Sashe 22

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Koda Hajiya da iyalanta suka dawo basusan anyi hakan ba, toh mai ma ya shallesu dasu, Hajiya ce ma mai d’an k’ok’arin kulada Kausar sabida jinin d’anta dake jikinta Najah kuwa ‘yar ko oho ce abinda Sahariyya ta d’aurata akai take bi, ita kuwa Sahariyyar tinda Hafiz ya mata kaca kaca akan Kausar ta kuma d’aukan karan tsana ta d’orawa yarinyar, batak’i ta wayi gari ta tadda yarinyar ta mace gaba d’aya ba, k’ila da har party saita had’a sabida farin ciki....

***

Shigowarta gidan kenan, dawowarta daga office ta hangi mota pake gefen flowers tamkar nasa, gabanta ya fad’i... For the first time da tab’a jin shakku cikin zuciyarta shin tana farin ciki ne da ganin Partner ko kuwa akasin hakan......

*SameenaAleeyou📚*
*INDA RAI*
_...............DA RABO_

*21*

*©Sameena Aleeyou...✍🏽*

Tijjani mai bayiwa flowers ta kirawo tana tambaya......

“Tijjani motar waye wannan....?”

Da tsananin mamaki Tijjani ke dubanta don a tunaninsa idan kowa zai mance kamannin motar Sameer ai ita bai kamata ace ta mance ba.....

Sosa kai Tijjani yayi kana yace “Hajiya ai motar Datta ne.... Bai jima da isowa ba .....”

Jinjina kai tai had’id lumshe idanu, da gaske Sameer na cikin gidansu, abinda ya faru last week ya shiga mata yawo a kwanya, tunanin ta yanda zata soma fuskantarsa ya addabeta, gani take tamkar Sameer zai fahimci wani abin....

Saida ta sauk’e deep breath kafin ta iya samun strength ta bud’e motar ta fice....

Kallo guda zaka mata ka fahimci tsananin sanyi da jikinta yayi, a hankali tasa hannu ta tura k’ofar parlorn, ba kowa sai Yesmin dake aikin kallo....

“Hi cousin...” Yesmin tace tana sakar mata murmushi...

Murmushin itama tai k’ok’arin maida mata kana tace “Are you alone....?”

Yesmin ta jinjina kai tana mai gyara zama saman sofa take fad’in “Eh Mummy da Ammi sun fita, Ya Khalid kuma yana tareda bak’o a sashensa.....”

Jinjina kai Siyama tai kana ta nufi upstairs don yin wanka, shiga tayi cikin sauk’ak’an kaya, doguwar riga mai laushin gaske as usual kai a bud’e....

Tsintar kanta tai da kasa fitowa daga d’akin sai faman sak’e sak’e take, bata tab’a tunanin cire cikin nan zai dameta irin haka ba, har cikin ranta take jin bazata iya fuskantar Sameer ba, what if ya ganeta..? What if ya tambayeta.... Mai zata soma ce masa....?

A hankali ta lumshe idanunta tana mai ayyanawa this is the best for the both of them.....

Parlorn ta nufo tana mai shafa samar wayarta a daidai lokacinda Khalid da Sameer suka shigo parlorn...

Daga can ya hangeta saman bene tai looking very pale kaman tai ciwo, gaban Sameer ya yanke ya fad’i cikin sauri ya nufi yanda take tsaye ta kasa motsa koda ‘yar yatsanta ne....

Khalid kam cikama rigarsa iska yayi musamman da ya hangi wannan yarinya mai uwar rawar kan a parlor, gaba d’aya ya fice daga gidan don dama Sameer ne ya zaunar dashi.....

Kallon juna suka shigayi tamkar wanda suka jima basuga juna ba, murya can k’asan mak’oshi Sameer yace “Partner...!”

K’wallan da Siyama ke mak’alewa ya gangaro mata... Sameer bai wata wata ba ya rungume matarsa tsam cikin jikinsa...

Fad’i yake “I’m here Partner... I’m here...”

Sosai Siyama ta kwanta cikin k’irjinsa tana sakin kuka a hankali, abinda ta rasa na ‘yan kwanaki... Batai zaton tayi kewar mijinta har haka ba...

Ita kuwa Yesmin yanda kasan ta sami tv haka take kallonsu, batai zaton ana irin wannan soyayyar a nigeria ba Nigeria d’in ma arewacinta.... Sun bala’in birgeta, Ita da Khalid kawai take hangowa cikin fuskokinsu, lallai cousin d’inta nada babban sa’a dama wannan shine mijin nata, he’s every woman’s dream... Gaskiya Siyama ta cab’a don babu macen da bazata so wannan had’edd’en gayen yake mutuwa akanta ba, gaba d’aya sun tafi da ita uwa wani duniya musamman data kuma jiyo muryar Sameer cikin damuwa yana furta

“Partner are you sure you’re fine... look, kalli fah.... kalli yanda kika koma... My goodness Siyaam have you been eating...? Talk to me...”

Ya k’arashe yana rik’e arms d’inta had’ida d’an jijjigata kad’an...

Harara ta d’an jefa masa kana tace “What do you expect Partner bayan ka tafi ka barni... So abinci ma bazanci da kyau ba....”

Murmushi ya sakar mata wanda ta jima bata gani ba kana yace “I’m sorry honey, zamu tafi tare wannan karon....”

D’an zaro idanu tai tana dubansa bata kai ga magana ba su Ammi sukayi sallama....

Sameer ya d’anyi k’ok’arin zare jikinsa daga na Siyama cikeda kunya yana d’an sosa k’eya ya nufo parlorn gaisar dasu Ammi...

Ammi fad’i take “A’a Dr sauk’an yaushe..? Sannu da zuwa lale...”

K’arasowa yayi ya zauna saman carpet yana mai gaidata...

“Mun sameku lafiya Ammi...”

Ammi tace “Alhamdulillah Sameer, ya aiki...”

Amsa mata yayi da angode Allah kafin Aunty Hidaya tace “Wannan ne sirkin namu..?”

Ammi tace “Gashi nan fah sirkin naki...”

Sameer ya duk’a ya gaidata itama cikeda karramawa, Ammi tai introducing Aunty Hidaya da d’iyarta Yesmin....

Yesmin ta mik’e a guje tabi bayan Siyama zuwa kitchen yanda ta tadda Siyamar ta saka Kubura ta markad’e masa lemun abarba...

Rungumeta Yesmin tai tana fad’in “Cousin kin gama dacewa kekam babu abinda ya miki saura,this kind love ku bar mana saura nida Khalid....” Ta k’arashe tana d’an daka tsalle...

Kubura da ta kafeta da idanu dariya ta kwashe dashi kana tace “Iska na wahalda mai kayan kara....”

Yesmin ta juyo a kufule tana dannawa Kubura muguwar kallo don dama tun zuwanta gidan jininsu baizo d’aya ba ta lura son gulma ne da ma’aikatan...

“Mai kikace...?”

Yesmin ta tambaya...

Kubura ta d’ago idanu kana tace “Au wai ni... Bance komai ba...”

Siyama ta danno mata mugun kallo kana tace “I know you Kubura mai kikace...?”

Kubura tace “Haba Aunty kinsan dai bana miki k’arya wannan yarinyar kawai k’aunata ce batai... Kuma ni naga ba son Khalid nake ba koh Aunty...” Ta k’arashe tana duban Siyama...

Siyama ta murmusa don ta lura har yanzu Kubura bazata daina haukan da take da wauta akan Khalid ba a baya ta zaci tsaban yarinta ne amma yanzu ta lura hauka kurum Kubura keyi, gashi ko hanyar da Khalid d’in ya taka idan ance tabi bazata bi ba tsaban tsoronsa da take...

Girgiza Siyama tai kana taceda Yesmin “Rabu da ita cousin haka take...”

Yesmin ta kuma galla mata harara kana tace “I heard her loud and clear fah wllhi tace wani abin k’ilanma zagina tayi...”

Kubura ta kuma watso wata maganar a hankali kafin Yesmin tai magana taceda Siyama “Aunty ga lemun yau dai zamuyi kewarki a gidan nan tinda Likita ya dawo gashi baki bani na kati ba yau.....”

Tak’aitaccen murmushi Siyama tai kana tace “Wai ke Kubura kullum sai an baki na kati waima waye kike kira....?”

Kubura ta zaro idanu kana tace “Aunty donma bakiga yanda a facebook samari ke bina ina masu wulak’anci ba sabida ni inada mijina gangariya ko kulasu banayi...”

Saida Siyama ta dara kana tace “Ko kuma kece iskan ke wahalwa... Kinga ki shirya yanzu ki tafi gidana kije ki kintsa gidan kafin mu k’araso.... Ki haura sama ki d’auko min handbag d’ina...”

Cikeda jin dad’i Kubura tace “An gama Hajjaju tamu Allah dai ya kare mana ke hasken zuciyar Dapta...”

Janyo hannun Yesmin Siyama tai suka fice tana fad’iwa Kubura “Ni ki wuce kafin daren ya idayi....”

Kubura sai murna take tasan yau tim Siyama zata cika mata aljihu.. Ta raka Yesmin da harara tana fad’i bayan sun fice...

“Kuji wannan abin meyema Khalid d’ina zaiyi dake..? Wllhi yafi k’arfin ajinki, nan gani nan bari akwatin maye... Duk barikancinki bazai k’yalla idanu kanki ba ehe... Banza kawai, ni yanzu daga Facebook ma makaranta zan koma sabida na lura Khalid d’ina asalin d’an boko da gayu ne ...” Ta k’arashe tana jan dogon tsaki had’ida sauya taku.....

Hhhhhh Wayaga su Kubura mata a gidan Khalid...

***

*Kano*

Banda taunar chewing gum bata komai sai wani d’add’aga idanu sama take tana tafiya tana bankad’a k’irji gaba, a yatsine ta k’araso teburin da yake kana tace “Ina saurarenka....”

Kallo ya bita dashi yanda tai masa tsaye aka kana yace “Ki zauna mana....”

Saida ta d’auki lokaci tamkar bazata zauna ba sai kuma ta finciko kurar ta zauna had’ida bashi baya tana mai ci gaba da taunar chewing gum...

“A haka ne zamuyi maganar...?” Ya fad’i yana yana mai d’an rank’ofowa....

Hannu ta d’aga masa cikeda tsiwa take fad’in “Kaga Hafiz nifa ba k’aramar yarinya bace da zaka nemi rainan wayo, idan magana kakeso muyi kayi maganar gaskiya ka turo gidanmu idan kuma ba haka ni kada ka sake zuwa wajena don wllhi bazan baka kaina ka watse dani a waje ba kaman yanda kayi da wancan ‘yar agwagwan ehe...”

Ta k’arashe tana mai danna masa aya.....

K’uri kawai Hafiza ya mata yama rasa mai zaice mata sai sunkuyar da kansa da yayi yana sosa goshi a hankali.....

Alhaji Tanimu mai kula da ginin da ake a gefen Kantin ne ya shigo yana faman washe mata baki, da gayya Sawwama ta mik’e ta nufesa cikin yanayin tafiyarta anayi ana rawa da k’irji ta isa gareshi tana fad’in “Alhajin kowa mai za’a kawo maka...?”

Bai daina yak’e baki ba yake fad’in “A kawo min tuwo ‘yar kyakkyawa...” Ya k’arashe idanunsa k’yam a k’irjinta...

A fusace Hafiz ya mik’e ya nufi Alhaji Tanimu zai kai masa naushi nan fah yaran Alhaji Tanimu sukayo kansa... Magajiya mahaifiyar Sawwama ta nufosu gadan gadan tana k’ok’arin rabon fad’a.. Sai fincika Hafiz yake yana fad’in Uban mai Alhaji Tanimu ke kallo jikin matarsa...

Sawwama bata tab’a sanin Hafiz na sonta haka ba sai yau, dad’i ya mamaye zuciyarta ganin irin kishin da Hafiz ke nunawa akanta...

Da k’yar aka raba fad’an Hafiz Alhaji Tanimu saida aka fidda Alhaji Tanimu daga restaurant d’in.. Shiko Hafiz a zuciye ya k’araso gaban Sawwama yana fad’in “Kin gama aiki a restaurant d’in nan, ince damuwarki a d’aura auren ne...?”

Cikin fad’a Sawwama ma tace “Wllhi babu igiyanka akaina baka isa hanani zuwa nan ba...”

A hasale yace “Haka kikace...?”

“Kwarai kuwa haka nace...!” Ta k’arashe tana galla masa harara hannaye a kunkumi...

K’wafa yayi kana ya d’auki mabud’in abin hawansa yayi ficewarsa daga Kantin...
Chapter 22 · 0% Book details