Sashe 147
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari kaman yanda suka shirya had’uwa gaba d’aya gidan babbar yayarsu Abidah hakan ce ta kasance, koda Aunty Bara’atu takaimasu Zulfah labarin abubuwan da suka faru a jiya d’aurin auren nasu ba k’aramin mamaki abin ya basu ba, Aunty Bara’atu ta sanar dasu komai dik abubuwan dasu Haule suka jima suna k’ullawa da yanda sukaita warwarewa da sirrikan da suka bayyana a jiyan, saidai bata sanar da Zulfa’u cewa aurenta ya tashi daga kan Akram ya koma kan uban gidansa kuma d’an uwanta ba, mamaki da al’ajabi yaita kamasu, Nabilah ta kad’a kai yafi abinda yafi kana tace “Wllhi Aunty ni dama na jima da karantar matan nan mugayen munafukai ne, Ke kiga Aunty Lami d’in nan yanda take kaffa kaffa da Mamy dama nasan naci na ciki mugayen banza azzalumai...”
Zulfah ta d’an harereta tace “Ke kuma ya isa haka kafin ki fara...”
Aunty B tace “Batta ta fad’i cikinta ai ba k’azafi aka masu ba... Kunga ku tashi mu shirya yanzu his Excellency zai turo motoci a kwashemu mu tafi can gidan Ammah (Ya Abidah)...”
Nabilah tai far da idanu tace “Kai ashe dai munada RABON shiga gidan gwamnati... Ayyye mun zama k’annen his Excellency....!”
Atika ta mik’a mata hannu suka tafe tace “Fad’i dai ki saka fad’i...” Gaba d’aya darawa sukai kana Aunty B ta kuma duban Atika tace su had’e kayan Zulfa’u waje d’aya dan daga can bazata dawo nan ba gidanta za’a wuce da ita... Atika tace “An gama Aunty...”
Zulfah dai har yanzu abin mamaki yaketa bata, ashe dai bawan Allahn nan jini suka had’a dashi shisa tinda ya fito siyasa taji bata tab’a cin karo da d’an siyasan dake matuk’ar bugeta ba kaman shi dikda cewa alkhairansa ga Al’umma ne yasa ya zamto gwaninta a fagen siyasa ashe dai harda jini suka had’a, Allah sarki wannan shine ikon Allah, Kullum tana burin ganinshi ido da ido sai gashi yanzu zata ganshi a arha tinda ya zamto d’an uwanta, in sha Allahu kaw sai ta bashi labarin ita babbar fan d’insa ce d’aya daga cikin magoya bayansa... Tana jin Aunty Bara’atu da Atika na magana k’us k’us batabi takansu ba ta mik’e ta nufi bathroom da niyyan d’auro alwala kafin su shige dan ita mace ce mai yawan zama cikin alwala muddin tana cikin tsarki...
A b’angaren Nabilah ma har yanzu abin al’ajabi yake bata jin cewa Aunt d’in Khalid matar Babansa k’anwar mahaifiyarsu ce, lallai wannnan shine ikon Allah mai gudanar da Al’amransa yanda yaso, bata tab’a zaton hakan mai yuwuwa bane saidai tabbas ba’a mamaki da ikon Allah domin kaw shid’in ne mai cikakken iko akan komai.... Kasancewar jarabawa suke shisa nata k’awayen babu ko k’wara harta Yusrah ma ta tafi da safe sunyi dasu Safwan zasu shiga tutorial da safen, sauk’in abin ma ita nan gidan Aunty Bara’atun zata dawo tinda ba yanzu zasu tafi can Abujan ba sai ta gama jarabawarta, ga wannan al’amari kuma da ya b’ullo kai, tana ganin Khalid na kiranta tak’i d’agawa tasan zancen bazai wuce yace zaizo su tafi gidan Ammah tare bane dan haka tama k’i d’aga wayar nasa, tsaf tasan halinsa yanzu sai yaje yaita bata kunya gaban iyaye, maganin bari karma a fara bazata d’aga ba saidai su had’u can gidan Ammahn....
Bayan shud’ewan wasu mintoci kaw hamshak’iyar Jeep d’in ta faka k’ofan gidan Aunty Bara’atu driver na jiran fitowarsu, ita dai Zulfah ta kasa aminta kasa yarda cewa Atika bata b’oye mata wani abu, dan ta kula falli da murnan Atika yama ninka lokacin da akace an saka aurenta, gashi har yanzu basuji daga Akram ba amma ko a jikin Atika... Saima wani Farin ciki da annashuwa data lura ya k’aru mata, wata zuciyar tace tinda kikaga haka toh ko shakka babu Akram na cikin k’oshin lafiya, k’ila wasu sabgogin nasa suka sha gabansa, amma fah ace kayi Amarya abin da kamar wuya da mamaki ka kasa koda d’aga waya ka kirata ne... Ta k’arashe tinanin tana mai sauk’e ajiyan zuciya a daidai sanda motar ya paka... Atika itace a front seat yayinda Aunty B Zulfa’u da kuma Nabilah Ke zaune daga bayan motar... Zulfah ta d’aga idanu tana duban ginin gidan tana iya tinowa a shekarun baya tun tana k’arama sun tab’a zuwa da Mamy taga Mamy ta fito tana kuka shikenan kuma bata sake jin d’uriyar matar daga Mamy ba, Allah sarki ashe dai rana irin wannan na zuwa masu ranan da zasu dunk’ule waje guda... Tinaninta ya katse sanda taji Aunty Bara’atu tana fad’in su k’araso Hajja mai aikin Ammah na amana ta nufosu tanai masu lale lale baki har kunne ganin gidansu da ya mutu shekara da shekaru yau ya dawo cikin rayuwa, rayuwa mai cikeda tarin albarka... Atika ta janyo trolly d’in Zulfa’u ta nufi bayan Hajja dake fad’in suje ta nuna mata d’akin da zata ije jakar... Atika dai sai zanzali da falli take tana kuma jinjina lamarin Wai yau Zulfa’u ce ta zamto matar Engr Mutallab daga gidan Hafiz, lallai Allah ya isa mai jujjuya al’amara yanda yaso ya kuma ga daman su gudana... Tabbas mahuk’urci mawadaci, ita tana mata Farin cikin ta rabu da Hafiz ta samu Akram ashe fin Akram tama samu, wannan shine INDA RAI tofah akwai RABO..... Ji take tafi kowa farin ciki ma Zulfa’u k’awarta...Tuni ta soma hango Zulfah a Office d’in First Lady dan tasan Zulfah ta kusa bankwana da station d’insu...
Can suka taddasu Mamy su Aunty Daula, Aunty Daula tana ganin Nabilah ta tafi ta rungumeta tana fad’in ko ba’a ce mata ba ga ‘yar gidanta amaryar d’an gidanta Khalid... Tuni su Ijlaal ma suka nufosu suna rungumarsu one by one, kan kace mai Zulfa’u Sarkin kuka idanunta sun shiga k’ok’arin kawo ruwa, yau gasu da zuri’arsu gaba d’aya a tare... Nan fah d’aukacin mutanen dake wajen ma idaniyansu suka shiga zuban hawaye.... Yaya Abidah ta isa tsakiyan Nabilah da Zulfah, tana hawaye ta rungumesu gaba d’aya suma hawayen suke... Mamy, Aunty B da kuma Aunty D suka isa suka rungumesu gaba d’aya suma... Aunty B ta mik’e tana amsa wayan Sameer da alama sanar da ita yake zai biya ya d’auko Raihanah da Marliya dan su biyu ne basu a wajen saiko Engr Ma’aruf da nasa family d’in su Muhibbah da yaransa da har yanzu suma basu samu isowa ba...
Aunty Bara’atu tace “Sameer Sarkin aiki, kai har weekends d’inma bazaka huta ba....?”
Daga d’aya b’angaren Sameer yace “Aunty dole ce ta kama emergency aka samu kuma ni ake buk’ata a wajen...”
Aunty B tace “Allah dai ya dafa maku gaba d’aya, aikin naka is not easy... Kodashike taimakon Al’umma ne, Allah ya baka ladanka...”
Sameer ya amsada Ameen Aunty na... Ku bamu mintina kad’an gamu nan isowa in sha Allah...”
Aunty Bara’atu tace “Take your time shima babban Yayan naku har yanzu bai iso ba, k’ila wani uzurin ya rik’esa....”
Sameer yace “Alright zan kirashi naji...Kinsan Excellency mai hidima da jama’a ne sosai....”
Aunty B tace “Toh shikenan sai Kun iso, Allah ya tsare...”
Sameer ya asmada Ameen Aunty kana sukai sallama....
***
A can gida kaw har yanzu gaban Raihanah bai daina fad’uwa ba, gashi Mamani tin safe babu wanda ya sakata a idanu, itakam sosai ta damu da Mamani dikda abubuwan da suka faru, dan d’an zaman da tai gabanta ta kula Mamani mutuniyar kirkice in her own ways dikda cewa tanada nata hayyan mabanbanta, ko kusa bazata had’a zaman gaban Mamani da zaman da tai gaban Haule ba... A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya tana duban rantsetsiyar doguwar rigar da Mamy ta bata tace ta saka, tasan dai can gidan Yayar Mamy zasu tinda yanzu maganan is all over babu wanda baisan Mamy sun had’eda zuri’ararsu gaba d’aya ba, amma koda wasa batasan cewa ita d’in matar aure bace har yanzu, auren ma yayansu Ma’aruf mijin da Yayarta Sahariyya was about to marry him....
Sosai rigar tai mata kyau ta zauna a jikinta d’as, Marliya ta tak’urata sai ta d’anyi kwalliya a fuskarta... Murmushi kawai Raihanah tai kana tace “Toh Wai a waye zanyi kwalliyan ne...?”
Marliya tace “Gidan biki fah zamu tafi, kika sani ko ki had’uda naki Prince Charming d’in mu kuma shan nik’i soon...” Ta k’arashe tana kashe mata idanu...
Harara Raihanah ta d’an aika mata kana ta girgiza kai tace “Ke koh... Zaki sani ne...”
Marliya ta kuma darawa tace “Eh dai naji....”
Gyara d’aurin kwalinta take gaban mirror lokaci guda take ci gaba da fad’in “Na kasa daina tinanin abubuwan da suke kan faruwa, Wai yau Mamy da family d’inta gaba d’aya a had’e waje guda.... Allah mai iko...”
Raihanah dake nad’e mayafin rigar akanta tace “Ikon Allah kenan Marliya, ya wuce gaban tinanin d’an adam... Mamy ta cancanci Farin ciki Bayan dik tulin k’alubalen data fuskanta a rayuwa, ita d’in tanada zuciya mai kyau , dole duk wani masoyinta yai mata Farin ciki....”
Marliya tace “Haka ne kam, Kinga tsaya na d’an shafa miki koda powder ce kawai kafin Ya Ma’aruf ya iso....”
Juya idanu kawai Raihanah tai had’ida girgiza kai kana tace “Wllhi Marliya kin faye fitina, Nabilah ce maganinki, Ana ganin itace mafad’aciya fad’arta batayi saida dalili, kece mai damunta da fitina, kija gefe ki nok’e kaman ba ke ba....”
Marliya ta tintsire da dariya tace “Allah sarki Addah Beels d’ina wllhi zanyi kewarta sosai...”
Raihanah ta murmusa a daidai lokacinda sukaji sallaman Yayansu Ma’aruf a k’ofa... Wani irin fad’uwan gaba Raihanah taji ya sauk’ar mata lokaci guda...
***
Zulfah ta d’an harereta tace “Ke kuma ya isa haka kafin ki fara...”
Aunty B tace “Batta ta fad’i cikinta ai ba k’azafi aka masu ba... Kunga ku tashi mu shirya yanzu his Excellency zai turo motoci a kwashemu mu tafi can gidan Ammah (Ya Abidah)...”
Nabilah tai far da idanu tace “Kai ashe dai munada RABON shiga gidan gwamnati... Ayyye mun zama k’annen his Excellency....!”
Atika ta mik’a mata hannu suka tafe tace “Fad’i dai ki saka fad’i...” Gaba d’aya darawa sukai kana Aunty B ta kuma duban Atika tace su had’e kayan Zulfa’u waje d’aya dan daga can bazata dawo nan ba gidanta za’a wuce da ita... Atika tace “An gama Aunty...”
Zulfah dai har yanzu abin mamaki yaketa bata, ashe dai bawan Allahn nan jini suka had’a dashi shisa tinda ya fito siyasa taji bata tab’a cin karo da d’an siyasan dake matuk’ar bugeta ba kaman shi dikda cewa alkhairansa ga Al’umma ne yasa ya zamto gwaninta a fagen siyasa ashe dai harda jini suka had’a, Allah sarki wannan shine ikon Allah, Kullum tana burin ganinshi ido da ido sai gashi yanzu zata ganshi a arha tinda ya zamto d’an uwanta, in sha Allahu kaw sai ta bashi labarin ita babbar fan d’insa ce d’aya daga cikin magoya bayansa... Tana jin Aunty Bara’atu da Atika na magana k’us k’us batabi takansu ba ta mik’e ta nufi bathroom da niyyan d’auro alwala kafin su shige dan ita mace ce mai yawan zama cikin alwala muddin tana cikin tsarki...
A b’angaren Nabilah ma har yanzu abin al’ajabi yake bata jin cewa Aunt d’in Khalid matar Babansa k’anwar mahaifiyarsu ce, lallai wannnan shine ikon Allah mai gudanar da Al’amransa yanda yaso, bata tab’a zaton hakan mai yuwuwa bane saidai tabbas ba’a mamaki da ikon Allah domin kaw shid’in ne mai cikakken iko akan komai.... Kasancewar jarabawa suke shisa nata k’awayen babu ko k’wara harta Yusrah ma ta tafi da safe sunyi dasu Safwan zasu shiga tutorial da safen, sauk’in abin ma ita nan gidan Aunty Bara’atun zata dawo tinda ba yanzu zasu tafi can Abujan ba sai ta gama jarabawarta, ga wannan al’amari kuma da ya b’ullo kai, tana ganin Khalid na kiranta tak’i d’agawa tasan zancen bazai wuce yace zaizo su tafi gidan Ammah tare bane dan haka tama k’i d’aga wayar nasa, tsaf tasan halinsa yanzu sai yaje yaita bata kunya gaban iyaye, maganin bari karma a fara bazata d’aga ba saidai su had’u can gidan Ammahn....
Bayan shud’ewan wasu mintoci kaw hamshak’iyar Jeep d’in ta faka k’ofan gidan Aunty Bara’atu driver na jiran fitowarsu, ita dai Zulfah ta kasa aminta kasa yarda cewa Atika bata b’oye mata wani abu, dan ta kula falli da murnan Atika yama ninka lokacin da akace an saka aurenta, gashi har yanzu basuji daga Akram ba amma ko a jikin Atika... Saima wani Farin ciki da annashuwa data lura ya k’aru mata, wata zuciyar tace tinda kikaga haka toh ko shakka babu Akram na cikin k’oshin lafiya, k’ila wasu sabgogin nasa suka sha gabansa, amma fah ace kayi Amarya abin da kamar wuya da mamaki ka kasa koda d’aga waya ka kirata ne... Ta k’arashe tinanin tana mai sauk’e ajiyan zuciya a daidai sanda motar ya paka... Atika itace a front seat yayinda Aunty B Zulfa’u da kuma Nabilah Ke zaune daga bayan motar... Zulfah ta d’aga idanu tana duban ginin gidan tana iya tinowa a shekarun baya tun tana k’arama sun tab’a zuwa da Mamy taga Mamy ta fito tana kuka shikenan kuma bata sake jin d’uriyar matar daga Mamy ba, Allah sarki ashe dai rana irin wannan na zuwa masu ranan da zasu dunk’ule waje guda... Tinaninta ya katse sanda taji Aunty Bara’atu tana fad’in su k’araso Hajja mai aikin Ammah na amana ta nufosu tanai masu lale lale baki har kunne ganin gidansu da ya mutu shekara da shekaru yau ya dawo cikin rayuwa, rayuwa mai cikeda tarin albarka... Atika ta janyo trolly d’in Zulfa’u ta nufi bayan Hajja dake fad’in suje ta nuna mata d’akin da zata ije jakar... Atika dai sai zanzali da falli take tana kuma jinjina lamarin Wai yau Zulfa’u ce ta zamto matar Engr Mutallab daga gidan Hafiz, lallai Allah ya isa mai jujjuya al’amara yanda yaso ya kuma ga daman su gudana... Tabbas mahuk’urci mawadaci, ita tana mata Farin cikin ta rabu da Hafiz ta samu Akram ashe fin Akram tama samu, wannan shine INDA RAI tofah akwai RABO..... Ji take tafi kowa farin ciki ma Zulfa’u k’awarta...Tuni ta soma hango Zulfah a Office d’in First Lady dan tasan Zulfah ta kusa bankwana da station d’insu...
Can suka taddasu Mamy su Aunty Daula, Aunty Daula tana ganin Nabilah ta tafi ta rungumeta tana fad’in ko ba’a ce mata ba ga ‘yar gidanta amaryar d’an gidanta Khalid... Tuni su Ijlaal ma suka nufosu suna rungumarsu one by one, kan kace mai Zulfa’u Sarkin kuka idanunta sun shiga k’ok’arin kawo ruwa, yau gasu da zuri’arsu gaba d’aya a tare... Nan fah d’aukacin mutanen dake wajen ma idaniyansu suka shiga zuban hawaye.... Yaya Abidah ta isa tsakiyan Nabilah da Zulfah, tana hawaye ta rungumesu gaba d’aya suma hawayen suke... Mamy, Aunty B da kuma Aunty D suka isa suka rungumesu gaba d’aya suma... Aunty B ta mik’e tana amsa wayan Sameer da alama sanar da ita yake zai biya ya d’auko Raihanah da Marliya dan su biyu ne basu a wajen saiko Engr Ma’aruf da nasa family d’in su Muhibbah da yaransa da har yanzu suma basu samu isowa ba...
Aunty Bara’atu tace “Sameer Sarkin aiki, kai har weekends d’inma bazaka huta ba....?”
Daga d’aya b’angaren Sameer yace “Aunty dole ce ta kama emergency aka samu kuma ni ake buk’ata a wajen...”
Aunty B tace “Allah dai ya dafa maku gaba d’aya, aikin naka is not easy... Kodashike taimakon Al’umma ne, Allah ya baka ladanka...”
Sameer ya amsada Ameen Aunty na... Ku bamu mintina kad’an gamu nan isowa in sha Allah...”
Aunty Bara’atu tace “Take your time shima babban Yayan naku har yanzu bai iso ba, k’ila wani uzurin ya rik’esa....”
Sameer yace “Alright zan kirashi naji...Kinsan Excellency mai hidima da jama’a ne sosai....”
Aunty B tace “Toh shikenan sai Kun iso, Allah ya tsare...”
Sameer ya asmada Ameen Aunty kana sukai sallama....
***
A can gida kaw har yanzu gaban Raihanah bai daina fad’uwa ba, gashi Mamani tin safe babu wanda ya sakata a idanu, itakam sosai ta damu da Mamani dikda abubuwan da suka faru, dan d’an zaman da tai gabanta ta kula Mamani mutuniyar kirkice in her own ways dikda cewa tanada nata hayyan mabanbanta, ko kusa bazata had’a zaman gaban Mamani da zaman da tai gaban Haule ba... A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya tana duban rantsetsiyar doguwar rigar da Mamy ta bata tace ta saka, tasan dai can gidan Yayar Mamy zasu tinda yanzu maganan is all over babu wanda baisan Mamy sun had’eda zuri’ararsu gaba d’aya ba, amma koda wasa batasan cewa ita d’in matar aure bace har yanzu, auren ma yayansu Ma’aruf mijin da Yayarta Sahariyya was about to marry him....
Sosai rigar tai mata kyau ta zauna a jikinta d’as, Marliya ta tak’urata sai ta d’anyi kwalliya a fuskarta... Murmushi kawai Raihanah tai kana tace “Toh Wai a waye zanyi kwalliyan ne...?”
Marliya tace “Gidan biki fah zamu tafi, kika sani ko ki had’uda naki Prince Charming d’in mu kuma shan nik’i soon...” Ta k’arashe tana kashe mata idanu...
Harara Raihanah ta d’an aika mata kana ta girgiza kai tace “Ke koh... Zaki sani ne...”
Marliya ta kuma darawa tace “Eh dai naji....”
Gyara d’aurin kwalinta take gaban mirror lokaci guda take ci gaba da fad’in “Na kasa daina tinanin abubuwan da suke kan faruwa, Wai yau Mamy da family d’inta gaba d’aya a had’e waje guda.... Allah mai iko...”
Raihanah dake nad’e mayafin rigar akanta tace “Ikon Allah kenan Marliya, ya wuce gaban tinanin d’an adam... Mamy ta cancanci Farin ciki Bayan dik tulin k’alubalen data fuskanta a rayuwa, ita d’in tanada zuciya mai kyau , dole duk wani masoyinta yai mata Farin ciki....”
Marliya tace “Haka ne kam, Kinga tsaya na d’an shafa miki koda powder ce kawai kafin Ya Ma’aruf ya iso....”
Juya idanu kawai Raihanah tai had’ida girgiza kai kana tace “Wllhi Marliya kin faye fitina, Nabilah ce maganinki, Ana ganin itace mafad’aciya fad’arta batayi saida dalili, kece mai damunta da fitina, kija gefe ki nok’e kaman ba ke ba....”
Marliya ta tintsire da dariya tace “Allah sarki Addah Beels d’ina wllhi zanyi kewarta sosai...”
Raihanah ta murmusa a daidai lokacinda sukaji sallaman Yayansu Ma’aruf a k’ofa... Wani irin fad’uwan gaba Raihanah taji ya sauk’ar mata lokaci guda...
***