Sashe 39
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“I don’t know... Ban sani ba nima, bansan ya akai na k’are a hannunsu ba, dukda cewa basu tab’a nunamin wani abu ba basu tab’a muzguna min ba tsawon rayuwata dasu I think I deserve to know who my real parents are... Sannan na cancanci nasan dalilin da yasa na koma hannunsu, shin iyayena mutuwa sukayi kokuwa suna raye, idan har suna raye inaso na gansu na masu tambayoyi da dama idan kuwa sun mutu mai matsayin mutanen da na girma a hannunsu... I’ve a lot of questions....”
Hannayensa Siyama ta rik’e fuskarta d’aukeda tsananin damuwa kana tace “I’m sorry Partner, this must be hard for you... Wannan lokaci ne da ya kamata na zamto ina gefenka, kayi hak’uri Partner...”
K’ak’aro murmushi yai ya sakar mata kana yace “Now that you know... Shin kinaso kici gaba da zama dani a haka....Zaki iya ci gaba da k’aunata after learning all this...?” Ya mata k’uri yana dubanta...
Murmushi ta sakar masa kana ta matso cikin jikinshi ta kwanta....
“I’ll always love and accept you for you are... remember, kaid’in nakeso just you...”
A hankali ya jinjina kai gajeren murmushi saman fuskarsa kana yace “Are you sure..?”
D’agowa tai tana dubansa kana tace “Wait.. Are you doubting me again...?”
K’uri ya mata yana nazarinta kafin ya sakar mata murmushi ya janyota jikinsa ya rungume... Lokaci guda yayima waje guda k’uri yana nazarin abubuwa.....
***
Nabila taima wayarta k’uri tana kuma juya Teddy d’in da Khalid ya bata, ita kad’ai take sakin murmushi tana mamakin salonshi, ko ba’a fad’a ba da alama kiranshi take jira.... Marliya ce ta shigo ta taddata a haka... Kallo ta bita dashi tana mamakin mai ya had’ata da teddy...
Marliya tai saurin k’arasawa saman gadon had’ida fincikan teddy d’in tana fad’in “Addah Naby ina kika samo wannan...? Dan Allah ki bani....”
Nabilah data d’an firgita fauce teddy din tai tana fad’in “Ke da Allah bani nan god’e god’e dake mai zakiyi dashi...”
Marliya ta d’an b’ata fuska tace “Toh ke mai yakeyi wajenki...?”
Nabilah ta d’an daburce lokaci guda ta shiga inda inda tana furta “Ni.. ni wa yace miki nawa ne na Kausar ne gobe zan kai mata...” Ta k’arashe tana tura Teddy d’in cikin drawer...
Marliya dai k’uri ta mata ganin yanda ‘yar uwar tata ta zama nervous all of a sudden, gaba d’aya Nabilah canzawa take a ‘yan kwanakin... D’an gyaran murya tai kana tai mata seda safe ta wuce wajen kwanciyarta....
Nabilah dai kwanciya kawai tai amma zuciyarta fal tunani Khalid ne ciki, ta janyo drawer d’in data jefa teddy din ciki tana duba murmushi kwance saman fuskarta, Marliya dake k’yallare da idanu guda tamkar mai bacci sai karantar ta take...
Vibration d’in da wayarta tai ne ta d’an razaneta...
Tai saurin zabura k’irjinta na bugawa da sauri, shid’in ne mai kira...
Ta lumshe idanunta a hankali had’ida sakin deep breath, saida wayar tai ringing kaman zata yanke sannan Nabilah tai k’arfin halin d’agawa....
Shiru kaman ba mai niyyan magana cikinsu....
Kaman daga sama don har ta cire rai bazai magana ba sai kuma ta sinkayo muryarsa yana fad’in “Are you still there....?”
Ta rasa mai zatace kaman tai hanging up sai kuma tai k’ok’arin saita kanta don bataso ya fahimci halin da take ciki, da d’an fad’a take furta “Kaga Malam kazo ka amshi kyautarka babu abinda zanyi dashi ko nai maka kama da mai wasan yara ne...?”
Ya murmusa a hankali daga yanda yake kishingid’e kana yace “Like right now... Can I come over...?”
Juya idanu tai kana tace “Kaga Malam karma kai tunanin zuwa gidanmu don Abbah baya tolerating kowa ya tsaya masa a k’ofar gida...”
“Idan ban mance ba gani na biyu da kikamin a gidanku a parlorn Abbah ne, so idan zanzo wajenki ba waje zan tsaya ba saidai a parlor... And I didn’t call to receive goodnight scolds.... And don’t sleep late because you’ve class tomorrow....Take care....” Daga haka katse kiran yai yana sakin murmushi ba tareda ya jira cewarta ba...
Tabi wayar da kallo tana mamakin hali irin na Khalid.... Murmushi ta saki ita kad’ai had’ida girgiza kai kana ta aje wayar ta kwanta tana sakin murmushi tana maimaita kalmarsa ta k’arashe cikin zuciyarta....
Marliya dake mak’ale da idanu tana dubanta dad’i ya rufe ta ganin Addar tata is finally giving herself a chance to be in a relationship, ba kaman yanda idan an mata maganan saurayi a baya ba tayita fad’a da masifa kenan tana fad’in ita bazata tab’a yin aure ba don bazata d’auki wani disappointment ba ganin yanda Addarta Zulfa’u tasha wahala gidan aure... Lallai dole Mamy taji wannan batu....
***
Washe gari da rana su biyu suke zaune gaban Malaminsu suna kora masa bayani....
Wata laya ya aje saman k’asa da aka zana da yatsu cikin babban tray, ya aje cazbaha saman layar kana ya dubi Lami da Haule....
Haule da ta gama zak’uwa tace “Malam mai ka gani....?”
Jinjina kai Malam yayi kana yace “Tabbas Ma’aruf na raye hasalima yana tsakankaninku kuma yana gab da dawowa cikin danginsa....”
Aunty Lami ta shiga sallallami tana furta sun shiga uku sun lalace Aminiyar Sirri ta cucesu datasa suka amince ta kashe Ma’aruf..
Haule ta shiga mintsilinta tana fad’in tai shiru sunzo wajen mai share masu kukansu...
Malam yace “Mai kukeso ayi...?”
Cikin sauri Haule tace “Malam kafin ya bayyana cikin dangi munaso a gama dashi ma’ana a kasheshi...”
Lami ta kalleta a firgice tana girgiza kai kana tace “A’a Malam a kuma badd’ashi a nisantashi da danginshi na har abada....”
Malam yace “Naji ra’ayoyinku..... Yanzu abinda za’ai ko wacce a cikinku zata d’au ‘ya’yan calbin guda d’ai d’ai...”
***
Hafiz na zube a parlor ya d’an sami baccin rana musamman da ya samu jarabebbiyar matarsa bata nan har wani hamdala saida yayi ya zube saman kujera bacci yai gaba dashi, nan cikin baccin nasa ya soma jiyo kururwa ana ihun b’arawo.... Ya mik’e zunbur ya fice a guje tamkar zararre ya nufi k’ofar gidan....
Cincirindon mutane ya taddata ana jajanta satar Babur da akai, sai lokacin ya tuna ashe a waje ya aje babur d’insa koda ya dawo daga kasuwa....
SameenaAleeyou📚
[09/02, 10:19] +234 703 745 3539: *INDA RAI*
_................DA RABO_
*32*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sam Abbah baiso Sameer ya fahimci halin da yake ciki don haka bai kuma d’ago kai sun had’a idanu ba, idanun nasa naga cazbaha da yake ja a hankali, Sameer ya d’an bud’e murya kad’an ya gaidashi...
Abbah ya amsa cikin raunanniyar murya yana mai k’ok’arin had’iye damuwarshi....
Shiru na wasu ‘yan lokuta suka gifta....
Sameer yana son tambayar Dattijon wanda bai nuna komai a gareshi ba sai karamci tun had’uwarsu amma saidai baisan ta yanda zai soma tambayarsa damuwarshi ba, baisan mai zaice ba amma kam har cikin zuciyarsa yakejin zogin ganin bawan Allahn haka cikin damuwa.... Muryar Abban ne ya katse masa tunaninsa sanda yake fad’in “Rayuwa takanzo ma bawa da abubuwa da dama wanda bai tab’a zato ba balle tsammani, rayuwar duniya gaba d’ayanta jarabawace.... Ta fannuka daban daban Allah yakan jarabci bayinsa, idan bawa ya yarda da k’addara kyakkyawa da akasinta tabbas shi yaci ribar rayuwar duniya... Da yawan mutane sukan halaka sakamakon fad’uwa jarabawar da Allah yaso jarabtarsu da ita....”
Tunda ya soma magana Sameer ke dubansa yanaji tamkar nasiha yake mashi tamkar ya shiga zuciyarshi yaga halin da yake ciki, Abbah yaci gaba da fad’in “Maiyasa tsawon rayuwata na danganta jarabawar da Ubangijina ya min da cewa laifin matata ne...? Mai yasa na biyewa mahaifiyata muka taru muka d’aurawa baiwar Allah laifi tsawon shekaru talatin....? Maiyasa rayuwata ta sauya tun daga wannan lokacin....?” Hawaye suka soma kwararo mashi sanda yaci gaba da fad’in “Shin da gaske banyi tawakkali da rashin Ma’aruf ba.... Mai yasa na kasa amincewa zuciyata Ma’aruf ya tafi tafiya ta har abada kuma bazai dawo gareni ba....” Babban mutum kaman Abbah ya kifa kanshi yana kuka sosai wanda ya karya zuciyar Sameer matuk’a, tsananin tausayin dattijon ya rufe shi... Kodaji zaka fahimci abubuwan da Abbah ke fad’i sun jima suna damunsa cikin zuciyarsa saidai bai samu wanda zai sharing dashi ba....
A hankali Sameer ya kai hannu ya dafa kafad’an Abbah guda...
Abbah ya d’ago k’wayar idanunsu ta had’e waje guda su duka biyu zuban hawaye suke mai tsananin ban tausayi da tab’a zuciya...
A hankali Sameer yake furta “Rayuwa haka takanzo mana da abubuwa masu tsananin ban mamaki... amma babu yanda muka iya dole mu amshi wad’annan k’addarori a bisa yanda sukazo mana....”
Abbah ya jinjina kai a hankali yana mai furta “Wad’annan sune k’addarorin da na kasa bud’e ido na gani tuntuni.... Idanuna sun rufe wajen d’aura laifin ga mahaifiyarshi wacce itama na tabbata rayuwarta ya kasance cikin tsananin na tsawon shekarun talatin, maimakon na zamto mai bata k’arfin gwiwa sai na kasance mai cuzguna mata da k’ara mata bak’in ciki, matata wacce nafiso wacce idanuna suka rufe na rasa farin cikina a tattareda ita, farin cikin da muka gina tun farkon had’uwarmu.....”
Sameer ya masa k’uri cikeda son jin asalin labarin wad’annan bayin Allah.....
D’an gyara zamansa yayi kana yace “Baba don Allah ka sanar dani labarinka.....”
Abbah ya d’ago idanu yana duban Sameer wani irin duba mai cikeda shauk’i kana ya shiga girgiza kai lokaci guda yake furta “Labarina ya canza ne shekaru talatin baya...” Lokaci guda kuma yaci gaba da girgiza kai yana furta “A’a Sameer, banso na saka ma raina cewa Ma’aruf na raye, sabida na jirashi tsawon shekaru talatin ko zai dawo amma bai dawo ba....”
Sameer da k’irjinsa ke tsananin bugu a hankali ya furta “Baba... Wanene Ma’aruf...?”
Abbah yai shiru na wasu dak’ik’ai kana yace “Ma’aruf d’anah ne wanda na rasashi tun yana shekaru uku a duniya....”
Gyara zama Sameer ya kumayi kana yace “Mutuwa yayi ko kuwa b’acewa yayi...?”
Abbah ya d’ago ya kuma dubansa kana yace “Duka.... Ya b’ace sannan ya mutu....”
“Ya akai kasan ya mutu....?”
Sameer ya jefo mishi tambayar
Hannayensa Siyama ta rik’e fuskarta d’aukeda tsananin damuwa kana tace “I’m sorry Partner, this must be hard for you... Wannan lokaci ne da ya kamata na zamto ina gefenka, kayi hak’uri Partner...”
K’ak’aro murmushi yai ya sakar mata kana yace “Now that you know... Shin kinaso kici gaba da zama dani a haka....Zaki iya ci gaba da k’aunata after learning all this...?” Ya mata k’uri yana dubanta...
Murmushi ta sakar masa kana ta matso cikin jikinshi ta kwanta....
“I’ll always love and accept you for you are... remember, kaid’in nakeso just you...”
A hankali ya jinjina kai gajeren murmushi saman fuskarsa kana yace “Are you sure..?”
D’agowa tai tana dubansa kana tace “Wait.. Are you doubting me again...?”
K’uri ya mata yana nazarinta kafin ya sakar mata murmushi ya janyota jikinsa ya rungume... Lokaci guda yayima waje guda k’uri yana nazarin abubuwa.....
***
Nabila taima wayarta k’uri tana kuma juya Teddy d’in da Khalid ya bata, ita kad’ai take sakin murmushi tana mamakin salonshi, ko ba’a fad’a ba da alama kiranshi take jira.... Marliya ce ta shigo ta taddata a haka... Kallo ta bita dashi tana mamakin mai ya had’ata da teddy...
Marliya tai saurin k’arasawa saman gadon had’ida fincikan teddy d’in tana fad’in “Addah Naby ina kika samo wannan...? Dan Allah ki bani....”
Nabilah data d’an firgita fauce teddy din tai tana fad’in “Ke da Allah bani nan god’e god’e dake mai zakiyi dashi...”
Marliya ta d’an b’ata fuska tace “Toh ke mai yakeyi wajenki...?”
Nabilah ta d’an daburce lokaci guda ta shiga inda inda tana furta “Ni.. ni wa yace miki nawa ne na Kausar ne gobe zan kai mata...” Ta k’arashe tana tura Teddy d’in cikin drawer...
Marliya dai k’uri ta mata ganin yanda ‘yar uwar tata ta zama nervous all of a sudden, gaba d’aya Nabilah canzawa take a ‘yan kwanakin... D’an gyaran murya tai kana tai mata seda safe ta wuce wajen kwanciyarta....
Nabilah dai kwanciya kawai tai amma zuciyarta fal tunani Khalid ne ciki, ta janyo drawer d’in data jefa teddy din ciki tana duba murmushi kwance saman fuskarta, Marliya dake k’yallare da idanu guda tamkar mai bacci sai karantar ta take...
Vibration d’in da wayarta tai ne ta d’an razaneta...
Tai saurin zabura k’irjinta na bugawa da sauri, shid’in ne mai kira...
Ta lumshe idanunta a hankali had’ida sakin deep breath, saida wayar tai ringing kaman zata yanke sannan Nabilah tai k’arfin halin d’agawa....
Shiru kaman ba mai niyyan magana cikinsu....
Kaman daga sama don har ta cire rai bazai magana ba sai kuma ta sinkayo muryarsa yana fad’in “Are you still there....?”
Ta rasa mai zatace kaman tai hanging up sai kuma tai k’ok’arin saita kanta don bataso ya fahimci halin da take ciki, da d’an fad’a take furta “Kaga Malam kazo ka amshi kyautarka babu abinda zanyi dashi ko nai maka kama da mai wasan yara ne...?”
Ya murmusa a hankali daga yanda yake kishingid’e kana yace “Like right now... Can I come over...?”
Juya idanu tai kana tace “Kaga Malam karma kai tunanin zuwa gidanmu don Abbah baya tolerating kowa ya tsaya masa a k’ofar gida...”
“Idan ban mance ba gani na biyu da kikamin a gidanku a parlorn Abbah ne, so idan zanzo wajenki ba waje zan tsaya ba saidai a parlor... And I didn’t call to receive goodnight scolds.... And don’t sleep late because you’ve class tomorrow....Take care....” Daga haka katse kiran yai yana sakin murmushi ba tareda ya jira cewarta ba...
Tabi wayar da kallo tana mamakin hali irin na Khalid.... Murmushi ta saki ita kad’ai had’ida girgiza kai kana ta aje wayar ta kwanta tana sakin murmushi tana maimaita kalmarsa ta k’arashe cikin zuciyarta....
Marliya dake mak’ale da idanu tana dubanta dad’i ya rufe ta ganin Addar tata is finally giving herself a chance to be in a relationship, ba kaman yanda idan an mata maganan saurayi a baya ba tayita fad’a da masifa kenan tana fad’in ita bazata tab’a yin aure ba don bazata d’auki wani disappointment ba ganin yanda Addarta Zulfa’u tasha wahala gidan aure... Lallai dole Mamy taji wannan batu....
***
Washe gari da rana su biyu suke zaune gaban Malaminsu suna kora masa bayani....
Wata laya ya aje saman k’asa da aka zana da yatsu cikin babban tray, ya aje cazbaha saman layar kana ya dubi Lami da Haule....
Haule da ta gama zak’uwa tace “Malam mai ka gani....?”
Jinjina kai Malam yayi kana yace “Tabbas Ma’aruf na raye hasalima yana tsakankaninku kuma yana gab da dawowa cikin danginsa....”
Aunty Lami ta shiga sallallami tana furta sun shiga uku sun lalace Aminiyar Sirri ta cucesu datasa suka amince ta kashe Ma’aruf..
Haule ta shiga mintsilinta tana fad’in tai shiru sunzo wajen mai share masu kukansu...
Malam yace “Mai kukeso ayi...?”
Cikin sauri Haule tace “Malam kafin ya bayyana cikin dangi munaso a gama dashi ma’ana a kasheshi...”
Lami ta kalleta a firgice tana girgiza kai kana tace “A’a Malam a kuma badd’ashi a nisantashi da danginshi na har abada....”
Malam yace “Naji ra’ayoyinku..... Yanzu abinda za’ai ko wacce a cikinku zata d’au ‘ya’yan calbin guda d’ai d’ai...”
***
Hafiz na zube a parlor ya d’an sami baccin rana musamman da ya samu jarabebbiyar matarsa bata nan har wani hamdala saida yayi ya zube saman kujera bacci yai gaba dashi, nan cikin baccin nasa ya soma jiyo kururwa ana ihun b’arawo.... Ya mik’e zunbur ya fice a guje tamkar zararre ya nufi k’ofar gidan....
Cincirindon mutane ya taddata ana jajanta satar Babur da akai, sai lokacin ya tuna ashe a waje ya aje babur d’insa koda ya dawo daga kasuwa....
SameenaAleeyou📚
[09/02, 10:19] +234 703 745 3539: *INDA RAI*
_................DA RABO_
*32*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sam Abbah baiso Sameer ya fahimci halin da yake ciki don haka bai kuma d’ago kai sun had’a idanu ba, idanun nasa naga cazbaha da yake ja a hankali, Sameer ya d’an bud’e murya kad’an ya gaidashi...
Abbah ya amsa cikin raunanniyar murya yana mai k’ok’arin had’iye damuwarshi....
Shiru na wasu ‘yan lokuta suka gifta....
Sameer yana son tambayar Dattijon wanda bai nuna komai a gareshi ba sai karamci tun had’uwarsu amma saidai baisan ta yanda zai soma tambayarsa damuwarshi ba, baisan mai zaice ba amma kam har cikin zuciyarsa yakejin zogin ganin bawan Allahn haka cikin damuwa.... Muryar Abban ne ya katse masa tunaninsa sanda yake fad’in “Rayuwa takanzo ma bawa da abubuwa da dama wanda bai tab’a zato ba balle tsammani, rayuwar duniya gaba d’ayanta jarabawace.... Ta fannuka daban daban Allah yakan jarabci bayinsa, idan bawa ya yarda da k’addara kyakkyawa da akasinta tabbas shi yaci ribar rayuwar duniya... Da yawan mutane sukan halaka sakamakon fad’uwa jarabawar da Allah yaso jarabtarsu da ita....”
Tunda ya soma magana Sameer ke dubansa yanaji tamkar nasiha yake mashi tamkar ya shiga zuciyarshi yaga halin da yake ciki, Abbah yaci gaba da fad’in “Maiyasa tsawon rayuwata na danganta jarabawar da Ubangijina ya min da cewa laifin matata ne...? Mai yasa na biyewa mahaifiyata muka taru muka d’aurawa baiwar Allah laifi tsawon shekaru talatin....? Maiyasa rayuwata ta sauya tun daga wannan lokacin....?” Hawaye suka soma kwararo mashi sanda yaci gaba da fad’in “Shin da gaske banyi tawakkali da rashin Ma’aruf ba.... Mai yasa na kasa amincewa zuciyata Ma’aruf ya tafi tafiya ta har abada kuma bazai dawo gareni ba....” Babban mutum kaman Abbah ya kifa kanshi yana kuka sosai wanda ya karya zuciyar Sameer matuk’a, tsananin tausayin dattijon ya rufe shi... Kodaji zaka fahimci abubuwan da Abbah ke fad’i sun jima suna damunsa cikin zuciyarsa saidai bai samu wanda zai sharing dashi ba....
A hankali Sameer ya kai hannu ya dafa kafad’an Abbah guda...
Abbah ya d’ago k’wayar idanunsu ta had’e waje guda su duka biyu zuban hawaye suke mai tsananin ban tausayi da tab’a zuciya...
A hankali Sameer yake furta “Rayuwa haka takanzo mana da abubuwa masu tsananin ban mamaki... amma babu yanda muka iya dole mu amshi wad’annan k’addarori a bisa yanda sukazo mana....”
Abbah ya jinjina kai a hankali yana mai furta “Wad’annan sune k’addarorin da na kasa bud’e ido na gani tuntuni.... Idanuna sun rufe wajen d’aura laifin ga mahaifiyarshi wacce itama na tabbata rayuwarta ya kasance cikin tsananin na tsawon shekarun talatin, maimakon na zamto mai bata k’arfin gwiwa sai na kasance mai cuzguna mata da k’ara mata bak’in ciki, matata wacce nafiso wacce idanuna suka rufe na rasa farin cikina a tattareda ita, farin cikin da muka gina tun farkon had’uwarmu.....”
Sameer ya masa k’uri cikeda son jin asalin labarin wad’annan bayin Allah.....
D’an gyara zamansa yayi kana yace “Baba don Allah ka sanar dani labarinka.....”
Abbah ya d’ago idanu yana duban Sameer wani irin duba mai cikeda shauk’i kana ya shiga girgiza kai lokaci guda yake furta “Labarina ya canza ne shekaru talatin baya...” Lokaci guda kuma yaci gaba da girgiza kai yana furta “A’a Sameer, banso na saka ma raina cewa Ma’aruf na raye, sabida na jirashi tsawon shekaru talatin ko zai dawo amma bai dawo ba....”
Sameer da k’irjinsa ke tsananin bugu a hankali ya furta “Baba... Wanene Ma’aruf...?”
Abbah yai shiru na wasu dak’ik’ai kana yace “Ma’aruf d’anah ne wanda na rasashi tun yana shekaru uku a duniya....”
Gyara zama Sameer ya kumayi kana yace “Mutuwa yayi ko kuwa b’acewa yayi...?”
Abbah ya d’ago ya kuma dubansa kana yace “Duka.... Ya b’ace sannan ya mutu....”
“Ya akai kasan ya mutu....?”
Sameer ya jefo mishi tambayar