Sashe 51
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sameer ya soma calming nasu a hankali “Ku kwantar da hankulanku, his condition is stable now, daga yanzu zuwa ko wane lokaci zai iya farkawa.....”
Gaba d’aya suka shiga jero hamdala suna godiyawa Sameer...
Mamani ta kafesa da idanu tamkar mai tunanin wani abin, hannayen Sameer d’in ta rik’e tana mai furta “Ubangiji ya saka maka da mafificin alheri likita ceton rayuwar d’anah da kayi...”
Sameer ya murmusa a hankali yana mai duban tsohuwar wacce kallo guda ya mata yaji zuciyarsa ya natsu da ita, a hankali yake furta “Babu komai Baaba ai Abbah tamkar mahaifi na d’aukeshi, ku daina min godiya dan Allah...”
Mamani ta jinjina kai tace “Iyayenka sunyi sa’an samun d’ah d’an albarka irinka, kaga ba irin jikana Hafizu ba wanda ya zama shanyayye watsattse shida mahaifinsa....”
Jin zata saki layi yasa Baffah Wada saurin kamota ya zaunarta yana fad’i a hankali “Mamani asibiti muke bai kamata kina maganganu haka ba...”
“Yo sai mai k’arya na fad’i....” Ta fad’i tana watsawa Baffah Wada muguwar kallo ta wafce hannunta ta k’arasa saman benci ta zauna tana mai ci gaba da surutanta...
Shiko Sameer ba tareda ya fahimci maganganun nata ba ya d’an saki murmushi kana ya koma d’akin da Abbah yake....
Kwance ya sameshi idanunshi a rufe na’uran bature naci gaba da aiki....
Zama yayi daga gefenshi had’ida k’ura masa idanu, shi kad’ai yake ayyana abubuwa da dama cikin zuciyarsa, a hankali Sameer ya tsinci kanshi yana mai kai hannayensa saman na Abbah ya dafa a hankali... Hannayen nasa sun jima saman na Abbah kafin daga bisani ya soma k’ok’arin janye su.....
Kaman daga sama yaji Abban ya rik’e hannayensa gam yana mai furta “Ma’aruf kar ka tafi ka barni, nasan zaka dawo garemu... Na jima da ayyanwa cikin zuciyata cewa INDA RAI, DA RABON watarana ka dawo... Kar ka kuma tafiya D’ah nah....”
K’wallan da Sameer ke rik’ewa suka shiga gangarowa, inama ace da gaske shine Ma’aruf d’in da suke nema, inama ace da gaske sud’in ne iyayensa, baiso yasama ransa hope d’in da ba haka bane... A hankali shima ya damk’e hannayen Abbah lokaci guda hawayen Sameer suka d’iga saman hannun Abbah wanda ya sanya Abbah bud’e idanunshi...
K’uri yayiwa Sameer shima Sameer d’in Abbah ke kallo...
Abbah yai k’ok’arin mik’ewa Sameer ya saurin taimaka masa yana mai goge hawayen fuskarsa don baiso Abbah ya fahimci hawayen nasa...
Abbah bai daina nazarin Sameer ba yana mai dubansa... Sameer ya kula da hakan duk sai yaji ya kasa sakewa a hankali ya soma k’ok’arin mik’ewa yana fad’in “Family d’inka gaba d’aya suna nan barin sanar dasu ka farka....”
Mik’ewan da zai yaji Abbah ya rik’o hannunsa guda, ya tsaya cak k’irjinsa naci gaba da bugawa... Abbah na daga kwance yace “Sameer kaima zuri’ata ne, daga sanda Allah ya kawoka cikin rayuwarmu ka zama family kaima, na gode da taimakon ka gareni, da ace baka nan kusa da bamusan abinda zai faru ba....”
Sameer ya juyo a hankali yana duban Abbah kana ya sakar masa murmushi, bai iya furta koda kalma ba sabida wasu abubuwa da yakeji suna fizgar masa lokaci guda...
Abbah yaci gaba da fad’in “Kai hak’uri abubuwan daka tadda suna faruwa damu nida zuri’ata... Nasan akwai abubuwa da dama da bai kamata kaga suna faruwa ba amma ka sani Allah shike gudanar da al’amaran bayinsa yanda yaso, shike jarabtan bayinsa da jarabawa irin wacce basuyi tsammani ba... Kayi hak’uri Sameer....”
Girgiza kai Sameer yai yana mai kuma dafa hannayen Abbah yake fad’in “Abbah kowa a rayuwar nan nada kalan nasa damuwan sannan kaman yanda kace Allah shike jarabtan bayinsa ba tareda shawarin kowa ba, ka daina bani hak’uri kaji Abbah...” Shiru na wasu ‘yan dak’ik’ai suka gifta kan Abbah a k’asa kafin Sameer d’in ya d’an kuma gyaran murya yace “Abbah likita ya tabbatarmin kana buk’atan rage yawan tunani sabida zuciyarka datayi weak, idan har bakai k’ok’arin rage damuwa da tarin tunani ba kana iya samun bugawar zuciya wanda sam bama fata, so try as much as possible kaga ka rage yawan tunani....” Ya k’arashe cikin kwantar da murya mai nitsa zuciya...
Abbah ya d’ago yana duban Sameer d’in kana yace “Anya Malam Sameer zan iya cire tunanin Zulfa’u cikin zuciyata bayan a lokacin da ya kamata na kasance mahaifi na k’warai a gareta ban kasance ba... Na muzguna mata da yawa, na bada gudummawa mai girma wajen ganin rayuwarta ta salwanta... Nabi sharrin shaid’an da son zuciyata, shin kana tunanin Zulfa’u zata yafe min.... Sam ban kasance mahaifin da zatai alfahari dashi ba.... Ni ne jigo na fad’awarta rayuwar k’unci data tsinci kanta ciki a yau... Kaicona...” Muryarsa ta shiga rawa sosai hawaye na gangaro mashi...
Jikin Sameer ya kumayin sanyi da al’amarin Abbah.... Ya zauna gefe dashi kad’an yana bashi baki...
“Abbah ka daina fad’in haka, dukda zamata dakai na d’an lokaci ne k’ank’ani, na fahimci kaid’in mutumin k’warai ne wanda ko wane d’ah zai alfaharin samunka matsayin mahaifi....”
Abbah ya tsareshi da idanu yana mai girgiza kai kana yace “Sameer zan sanar dakai komai, kama daga b’acewan d’anah Ma’aruf har izuwa irin rik’on da na baiwa sauran d’iyoyina da Allah ya damk’amin su matsayin amana na kumayi watsi da wannan nauyi mai girma da Allah ya d’auramin duk a rashin d’ahnah Ma’aruf....”
Shiru Sameer yai yana duban Abbah zuciyarsa bata daina raunana ba, hawaye basu daina zubo masa ba a lokacin da Abbah ke sanar dashi yanda ya watsar da d’iyoyinshi mata duk akan rashin Ma’aruf, sosai ya tausayawa Abbah da rayuwar da ahalin gidansa suka tsinci kawunansu ciki....
Jiki a sanyaye Sameer yace “Shin idan Ma’aruf ya dawo gareku kuna tunanin zai yafe maku k’ask’anta rayuwar k’annensa da kukayi duk a sabida rashinsa...? Shin da wasu idanu zaku duba Ma’aruf da ‘yan uwansa...? Shin meye laifin ‘yan uwan Ma’aruf....?” Tambayoyin da suka kuma sanya Abbah zuban hawaye sosai yayinda shima Sameer d’in ke zuban hawaye....
Aljihun gaban rigarsa Abbah ya zira hannu ciki ya zaro wata hoto ya mik’awa Sameer kana yace “Tsawon rayuwata a koda yaushe Ma’aruf na ajiye gefen zuciyata ban tab’a canzawa hoton nan ma’ajiyi ba daidai da rana guda tun bayan b’acewarsa... Inada yak’ini d’ahnah zai saurareni zai kuma yafemin...”
Duk maganganun da Abbah keyi idanun Sameer naga hoton k’aramin yaro da bazai wuce shekaru biyu zuwa uku ba dake rik’e hannunsa... Hawayensa suka k’aru, k’afafuwansa suna barazanar kasa d’aukarsa...
A hankali cikin rawar murya yaceda Abbah “Shin wannan shine d’anka Ma’aruf...?”
Abbah ya jinjina kai a hankali kana yace “Shine Ma’aruf d’ina....”
“Da ace yana nan zaikai kimanin shekaru nawa a yanzu...?” Sameer ya kuma jefo masa wata tambayar.....
Abbah ya d’anyi shiru kaman mai nazari kana yace “Zaikai kimanin shekaru talatin da uku....”
Sameer ya kuma jin zuciyarsa tai masa rauni tana mai kuma jadadda masa waswasinsa....
A hankali ya mik’e yana k’ok’arin saita kansa kana ya dafa Abbah kaman zai magana sai kuma ya kasa a hankali ya janye hannunsa ya fice cikin sauri sabon k’walla na k’ok’arin ciko idanunsa, abu guda zaiyi ya cire zuciyarsa daga d’inbin waswasin dake k’unshe cikinta, irin yanda yayi da iyayensa na can gida, bazai tunk’ari Abbah da batun ba sai ya tabbatar ma zuciyarsa ya kuma samu hujja mai k’arfi da zai tabbatar da hakan...
Kai tsaye laboratory ya wuce yanda sukayi ganawa ta sirri shida d’aya daga cikin ma’aikatan lab d’in, tuni ya bada sample d’in jininshi ya kuma buk’aci a d’au na Abbah a b’oye a duba idan sun had’a dangantaka ta jini...
Sameer na fitowa ya hangi family d’in Abbah zazzaune suna jiran tsammani, jikinsa ya kumayin sanyi sosai sanin cewa wad’annan zuri’a na iya zama zuri’arsa, idanunsa ya sauk’a kan Mamy tsananin tausayinta ya rufesa, ji yayi kaman yaje ya rungumeta yace mata shine long lost son d’inta, take kuma zuciyarsa ta shiga raya masa yanada buk’atan sanin ya akai ya b’ace ya rabu da danginsa tsawon shekaru shin jefar dashi sukai kokuwa b’acewa yayi...Sannan ya akai ya k’are hannunsu Mummy...? Wad’annan tambayoyi ne da ya kamata yasan amsoshinsu kafin ya yanke wani hukunci... Cikin sauri yasa kai ya shige ba tareda ya bari sun gansa ba...
Kai tsaye bai zarce ko ina ba sai gidansu Shamsu...
A b’angarensu Mamy kuwa haka suka d’unguma suka shiga duba Abbah kowa nason sanin halinda Abban ke ciki har saida Likitoci suka d’an dakatar dasu, ganin jikin nasa da sauk’i sosai yasa su Nabilah Marliya da Raihanah suka nufi gida don shirya abincin da za’a kawo masu asibitin da kuma wasu abubuwan buk’ata...
Adaidaitansu na tsayuwa sai karo da gungun yara sukai cikin layin nasu tamkar wanda suke jiran isowarsu suka ci gaba da wak’e wak’e suna kiran sunan Nabilah cikin aibantawa da tsananin tozarci...
Nabila Raiha da Marliya cirko cirko sukai suna kallon wannan ikon Allah, kan kace mai sunyo kansu suna ci gaba da tafi da wak’e wak’e cewa Nabilah karuwace, ‘yan sa idon unguwan tuni sunyi chaa ga d’oyoyin su Baffah Wadah suma duk sun fito suna kallon wannan bak’on al’amari mai ban mamaki...
Kankace mai yaran nan sun shiga dunbuzan k’asa suna jifan Nabilah dashi.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*42*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
NOT EDITED
Gaba d’aya suka shiga jero hamdala suna godiyawa Sameer...
Mamani ta kafesa da idanu tamkar mai tunanin wani abin, hannayen Sameer d’in ta rik’e tana mai furta “Ubangiji ya saka maka da mafificin alheri likita ceton rayuwar d’anah da kayi...”
Sameer ya murmusa a hankali yana mai duban tsohuwar wacce kallo guda ya mata yaji zuciyarsa ya natsu da ita, a hankali yake furta “Babu komai Baaba ai Abbah tamkar mahaifi na d’aukeshi, ku daina min godiya dan Allah...”
Mamani ta jinjina kai tace “Iyayenka sunyi sa’an samun d’ah d’an albarka irinka, kaga ba irin jikana Hafizu ba wanda ya zama shanyayye watsattse shida mahaifinsa....”
Jin zata saki layi yasa Baffah Wada saurin kamota ya zaunarta yana fad’i a hankali “Mamani asibiti muke bai kamata kina maganganu haka ba...”
“Yo sai mai k’arya na fad’i....” Ta fad’i tana watsawa Baffah Wada muguwar kallo ta wafce hannunta ta k’arasa saman benci ta zauna tana mai ci gaba da surutanta...
Shiko Sameer ba tareda ya fahimci maganganun nata ba ya d’an saki murmushi kana ya koma d’akin da Abbah yake....
Kwance ya sameshi idanunshi a rufe na’uran bature naci gaba da aiki....
Zama yayi daga gefenshi had’ida k’ura masa idanu, shi kad’ai yake ayyana abubuwa da dama cikin zuciyarsa, a hankali Sameer ya tsinci kanshi yana mai kai hannayensa saman na Abbah ya dafa a hankali... Hannayen nasa sun jima saman na Abbah kafin daga bisani ya soma k’ok’arin janye su.....
Kaman daga sama yaji Abban ya rik’e hannayensa gam yana mai furta “Ma’aruf kar ka tafi ka barni, nasan zaka dawo garemu... Na jima da ayyanwa cikin zuciyata cewa INDA RAI, DA RABON watarana ka dawo... Kar ka kuma tafiya D’ah nah....”
K’wallan da Sameer ke rik’ewa suka shiga gangarowa, inama ace da gaske shine Ma’aruf d’in da suke nema, inama ace da gaske sud’in ne iyayensa, baiso yasama ransa hope d’in da ba haka bane... A hankali shima ya damk’e hannayen Abbah lokaci guda hawayen Sameer suka d’iga saman hannun Abbah wanda ya sanya Abbah bud’e idanunshi...
K’uri yayiwa Sameer shima Sameer d’in Abbah ke kallo...
Abbah yai k’ok’arin mik’ewa Sameer ya saurin taimaka masa yana mai goge hawayen fuskarsa don baiso Abbah ya fahimci hawayen nasa...
Abbah bai daina nazarin Sameer ba yana mai dubansa... Sameer ya kula da hakan duk sai yaji ya kasa sakewa a hankali ya soma k’ok’arin mik’ewa yana fad’in “Family d’inka gaba d’aya suna nan barin sanar dasu ka farka....”
Mik’ewan da zai yaji Abbah ya rik’o hannunsa guda, ya tsaya cak k’irjinsa naci gaba da bugawa... Abbah na daga kwance yace “Sameer kaima zuri’ata ne, daga sanda Allah ya kawoka cikin rayuwarmu ka zama family kaima, na gode da taimakon ka gareni, da ace baka nan kusa da bamusan abinda zai faru ba....”
Sameer ya juyo a hankali yana duban Abbah kana ya sakar masa murmushi, bai iya furta koda kalma ba sabida wasu abubuwa da yakeji suna fizgar masa lokaci guda...
Abbah yaci gaba da fad’in “Kai hak’uri abubuwan daka tadda suna faruwa damu nida zuri’ata... Nasan akwai abubuwa da dama da bai kamata kaga suna faruwa ba amma ka sani Allah shike gudanar da al’amaran bayinsa yanda yaso, shike jarabtan bayinsa da jarabawa irin wacce basuyi tsammani ba... Kayi hak’uri Sameer....”
Girgiza kai Sameer yai yana mai kuma dafa hannayen Abbah yake fad’in “Abbah kowa a rayuwar nan nada kalan nasa damuwan sannan kaman yanda kace Allah shike jarabtan bayinsa ba tareda shawarin kowa ba, ka daina bani hak’uri kaji Abbah...” Shiru na wasu ‘yan dak’ik’ai suka gifta kan Abbah a k’asa kafin Sameer d’in ya d’an kuma gyaran murya yace “Abbah likita ya tabbatarmin kana buk’atan rage yawan tunani sabida zuciyarka datayi weak, idan har bakai k’ok’arin rage damuwa da tarin tunani ba kana iya samun bugawar zuciya wanda sam bama fata, so try as much as possible kaga ka rage yawan tunani....” Ya k’arashe cikin kwantar da murya mai nitsa zuciya...
Abbah ya d’ago yana duban Sameer d’in kana yace “Anya Malam Sameer zan iya cire tunanin Zulfa’u cikin zuciyata bayan a lokacin da ya kamata na kasance mahaifi na k’warai a gareta ban kasance ba... Na muzguna mata da yawa, na bada gudummawa mai girma wajen ganin rayuwarta ta salwanta... Nabi sharrin shaid’an da son zuciyata, shin kana tunanin Zulfa’u zata yafe min.... Sam ban kasance mahaifin da zatai alfahari dashi ba.... Ni ne jigo na fad’awarta rayuwar k’unci data tsinci kanta ciki a yau... Kaicona...” Muryarsa ta shiga rawa sosai hawaye na gangaro mashi...
Jikin Sameer ya kumayin sanyi da al’amarin Abbah.... Ya zauna gefe dashi kad’an yana bashi baki...
“Abbah ka daina fad’in haka, dukda zamata dakai na d’an lokaci ne k’ank’ani, na fahimci kaid’in mutumin k’warai ne wanda ko wane d’ah zai alfaharin samunka matsayin mahaifi....”
Abbah ya tsareshi da idanu yana mai girgiza kai kana yace “Sameer zan sanar dakai komai, kama daga b’acewan d’anah Ma’aruf har izuwa irin rik’on da na baiwa sauran d’iyoyina da Allah ya damk’amin su matsayin amana na kumayi watsi da wannan nauyi mai girma da Allah ya d’auramin duk a rashin d’ahnah Ma’aruf....”
Shiru Sameer yai yana duban Abbah zuciyarsa bata daina raunana ba, hawaye basu daina zubo masa ba a lokacin da Abbah ke sanar dashi yanda ya watsar da d’iyoyinshi mata duk akan rashin Ma’aruf, sosai ya tausayawa Abbah da rayuwar da ahalin gidansa suka tsinci kawunansu ciki....
Jiki a sanyaye Sameer yace “Shin idan Ma’aruf ya dawo gareku kuna tunanin zai yafe maku k’ask’anta rayuwar k’annensa da kukayi duk a sabida rashinsa...? Shin da wasu idanu zaku duba Ma’aruf da ‘yan uwansa...? Shin meye laifin ‘yan uwan Ma’aruf....?” Tambayoyin da suka kuma sanya Abbah zuban hawaye sosai yayinda shima Sameer d’in ke zuban hawaye....
Aljihun gaban rigarsa Abbah ya zira hannu ciki ya zaro wata hoto ya mik’awa Sameer kana yace “Tsawon rayuwata a koda yaushe Ma’aruf na ajiye gefen zuciyata ban tab’a canzawa hoton nan ma’ajiyi ba daidai da rana guda tun bayan b’acewarsa... Inada yak’ini d’ahnah zai saurareni zai kuma yafemin...”
Duk maganganun da Abbah keyi idanun Sameer naga hoton k’aramin yaro da bazai wuce shekaru biyu zuwa uku ba dake rik’e hannunsa... Hawayensa suka k’aru, k’afafuwansa suna barazanar kasa d’aukarsa...
A hankali cikin rawar murya yaceda Abbah “Shin wannan shine d’anka Ma’aruf...?”
Abbah ya jinjina kai a hankali kana yace “Shine Ma’aruf d’ina....”
“Da ace yana nan zaikai kimanin shekaru nawa a yanzu...?” Sameer ya kuma jefo masa wata tambayar.....
Abbah ya d’anyi shiru kaman mai nazari kana yace “Zaikai kimanin shekaru talatin da uku....”
Sameer ya kuma jin zuciyarsa tai masa rauni tana mai kuma jadadda masa waswasinsa....
A hankali ya mik’e yana k’ok’arin saita kansa kana ya dafa Abbah kaman zai magana sai kuma ya kasa a hankali ya janye hannunsa ya fice cikin sauri sabon k’walla na k’ok’arin ciko idanunsa, abu guda zaiyi ya cire zuciyarsa daga d’inbin waswasin dake k’unshe cikinta, irin yanda yayi da iyayensa na can gida, bazai tunk’ari Abbah da batun ba sai ya tabbatar ma zuciyarsa ya kuma samu hujja mai k’arfi da zai tabbatar da hakan...
Kai tsaye laboratory ya wuce yanda sukayi ganawa ta sirri shida d’aya daga cikin ma’aikatan lab d’in, tuni ya bada sample d’in jininshi ya kuma buk’aci a d’au na Abbah a b’oye a duba idan sun had’a dangantaka ta jini...
Sameer na fitowa ya hangi family d’in Abbah zazzaune suna jiran tsammani, jikinsa ya kumayin sanyi sosai sanin cewa wad’annan zuri’a na iya zama zuri’arsa, idanunsa ya sauk’a kan Mamy tsananin tausayinta ya rufesa, ji yayi kaman yaje ya rungumeta yace mata shine long lost son d’inta, take kuma zuciyarsa ta shiga raya masa yanada buk’atan sanin ya akai ya b’ace ya rabu da danginsa tsawon shekaru shin jefar dashi sukai kokuwa b’acewa yayi...Sannan ya akai ya k’are hannunsu Mummy...? Wad’annan tambayoyi ne da ya kamata yasan amsoshinsu kafin ya yanke wani hukunci... Cikin sauri yasa kai ya shige ba tareda ya bari sun gansa ba...
Kai tsaye bai zarce ko ina ba sai gidansu Shamsu...
A b’angarensu Mamy kuwa haka suka d’unguma suka shiga duba Abbah kowa nason sanin halinda Abban ke ciki har saida Likitoci suka d’an dakatar dasu, ganin jikin nasa da sauk’i sosai yasa su Nabilah Marliya da Raihanah suka nufi gida don shirya abincin da za’a kawo masu asibitin da kuma wasu abubuwan buk’ata...
Adaidaitansu na tsayuwa sai karo da gungun yara sukai cikin layin nasu tamkar wanda suke jiran isowarsu suka ci gaba da wak’e wak’e suna kiran sunan Nabilah cikin aibantawa da tsananin tozarci...
Nabila Raiha da Marliya cirko cirko sukai suna kallon wannan ikon Allah, kan kace mai sunyo kansu suna ci gaba da tafi da wak’e wak’e cewa Nabilah karuwace, ‘yan sa idon unguwan tuni sunyi chaa ga d’oyoyin su Baffah Wadah suma duk sun fito suna kallon wannan bak’on al’amari mai ban mamaki...
Kankace mai yaran nan sun shiga dunbuzan k’asa suna jifan Nabilah dashi.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*42*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
NOT EDITED